February 26, 2019

Shekaru 3 Da Kisan-kiyashin Zariya (8)


Daga Saifullahi M. Kabir

RAHOTON AL’ARABIYYA TV A YAYIN ZUWAN BUHARI QATAR

Kwatsam sai ga tashar talabijin ta AL-ARABIYYA ta yi wani rahoto a kan ziyarar da Shugaban kasar Nijeriya Muhammadu Buhari ya kai Qatar, wanda suka dora ‘video’ din rahoton a shafin gidan talabijin din a ranar Talata 1/03/16. Suka yi masa take da “Sabon gargadi daga Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, game da masu yada busharar Shi’anci a Afrika.”

Suka ce: “Buhari ya hangi wani hatsari da ke tunkarowa na yaduwar wata akida mai hatsari, wacce manufarta ita ce, tayar da fitina, raba kan al’umma da kawo hatsaniya.”

Rahoton ya ci gaba da cewa: “Nijeriya wacce take Cibiyar Afrika; ta fi kowace kasa a Nahiyar ta Afirka yawan mutane, wacce ake kiyasta Musulmin cikin ta sun kai miliyan 85. Daga cikin su akwai kasa da miliyan 10 ’yan Shi'a, sauran kuma Musulmi ne mabiya Sunnah.”

Su ci gaba da cewa: “Shi’a ta yadu daga baya (a Nijeriya) ta hannun Ibraheem El-Zakzaky, wanda Iran ta nasabta shi a matsayin Wakilin Hizbullah a Nijeriya. Jami’an tsaro sun kama shi ne a watan Disambar shekarar da ta gabata; bayan sun tuhume shi da yunkurin kashe Shugaban Hafsan Sojojin Nigeria, a lokacin da yake kan hanyarsa ta wucewa Zariya; wacce ake ganin ta a matsayin wuri mafi muhimmanci ga mabiya Shi'a da suke zaune a Arewacin Nijeriya, kuma nan ne mazaunin Shugabanta da ke samun goyon bayan Iran.”

A nan sai suka sanya bidiyon Buhari yana cewa: “Arangamar (ta Zariya) faru ne a lokacin da ya yi kokarin dakatar da tawagar Hafsan-Hafsoshin sojojin Nijeriya. Daga baya Shi’a ta yi karfi. Kuma muna da masaniyar cewa tana samun karfafa da abin da ya yi kama da haka daga Iran”.

Sannan suka ci gaba da sharhi da cewa: “Shugabannin siyasa da sojojin Nijeriya ra’ayinsu ya zo daya a kan cewa Shi’a a Nijeriya - wacce take da goyon bayan Iran – ra’ayinsu daya da kungiyar Boko Haram, wacce ta yi wa Da’esh bai’a.”

Suka ce: “Dalilai da dama ne suka sabbaba yaduwar Shi’a a Nijeriya. Daga cikin su akwai talauci, jahilci, ba da tallafin karatu, (da Shi'a suke badawa) da kuma yaudarar mutane ta hanyar taken ’yanto Masallacin Al-Aqsa. Wadannan dalilan ne ke sa mutane tudadar shiga wannan Mazhabar da Iran ke karfafawa.”

Mai karatu, ka lura da yadda bayanan mutanen nan ke zuwa a tare; yaduwar Shi’anci, tasirin Iran, goyon bayan Iran, da batun TAQIYYA, ko taimakon raunana. Wadannan sune duk abin da suke kokarin su nuna cewa Harkar Musulunci na samu don habakar ta. Kuma shi ne abin da suke kokarin a dakile.

Kuma har ila yau, kalaman Buhari ya nuna maka kai tsaye mai suka yi a Zariya, sun auka wa Shaikh Zakzaky ne da almajiransa, don su dakile yaduwar tasirin Iran a Afirka, musamman a Nijeriya. Amma ba wani abu wai tare hanya ne ya sabbaba kashe mutum 1,000, da kama Shaikh Zakzaky a daure tsawon shekaru da rauni a jikinsa ba, kamar yadda za mu ji daga bakin Yariman Saudiyya a gaba.

Muhammadu Buhari da Malaman Wahabiyawa na Saudiyya da na Nijeriya

RAHOTON DW NA BAYANIN BIN SALMAN KAN DAKILE TASIRIN IRAN A AFIRKA

Sai aka zo, a ranar 24 ga watan Afrilun 2018, sashen Hausa na gidan rediyon DW da ke Jamus ya fitar da rahoton murya, inda Yariman Saudiyya, Muhammad Bin Salman ya furta a sarari cewa su ke da alhakin harin da aka kai wa Shaikh Zakzaky a kokarinsu na dakile karfi da tasirin Iran a Afirka!

Rahoton na DW, ya bayyana cewa: “A wata hira da jaridar TIMES ta Amurka ta yi da Yarima mai jiran gado na Saudiyya, Muhammad Bin Salman ya ce kasarsa ta kai gouro-ta-kai-mari a Afirka don ganin ta rage tasirin Iran a nahiyar, yadda ya zuwa yanzu ta yi nasarar karya karfin kasar ta Iran a Afirka da kimanin kaso 95 cikin 100.”

A shafinsu na sakar sama, DW, sun rubuta a karkashin wani hoto da suka saka, cewa: “Muhammad Bin Salman ya ce kasarsa (Saudi-Arebiya) ce ta dakushe karfin Ibraheem al-Zakzaky a Nijeriya”

Sannan rahoton nasu ya ci gaba da cewa: “Dakta Zayeed Al-Amri, mamba a Cibiyar tsara dabarun mulki da tunkarar matsaloli na kasar ta Saudiyya, ya yi karin bayani kan manufar Yariman, inda yake cewa ‘abin da Yarima ke nufi a nan shi ne tun bayan da ya ayyana shirinsa na tunkarar makiya, Saudiya ta yi nasarar karya tanadin Iran a Yemen da Somaliya da Djibouti da Sudan, kamar yadda ta lalata yunkurinta na kafa makamanciyar kungiyar Hizbollah a Nijeriya da hana Ibraheem Zakzaky yin juyin mulki a kasar.”

Kafar ta DW, ta kuma ruwaito Dakta Amani al-Taweel ta Cibiyar bincike na Al-Ahram a Masar, inda take cewa: “A gaskiya Saudiyya ba abin da ya fi damunta tamkar yada akidar Wahabiyyanci a Afirka fiye da kulla huldar kasuwanci da alakar diflomasiyya ta ban gishiri, in ba ka manda.”

A wannan rahoton, Muhammad Bin Salman da sauran masu sharhi sun bayyana karara dalilin kisan kiyashin Zariya, cewa kwangila ce ta gidan Sarautar Saudiyya zuwa ga Shugaban Nijeriya da jami’an tsaronta a kan su dakile mata Shaikh Zakzaky da abin da suke kira Shi’anci, a kokarinsu na dakile tasirin Iran a Afirka da kuma karfafar yaduwar akidarsu ta Wahabiyyanci.

GUDUMMAWAR MALAMAN WAHABIYAWA A KAN WAKI’AR

Ya gabata tun a kashi na biyu na wannan jerin rubutun, na kawo yadda Malaman Wahabiyyawa suka rika zame-zame da gwamnati da kuma yin wasu kalamai na nuna farin cikinsu kafin da kuma musamman ma bayan abin da ya faru na kashe wadanda suke kira ’yan Shi’a fiye da 1,000 a Zariya.

Mun kawo yadda a ranar Asabar, 19/12/2015 wasu daga cikin Gwamnonin Arewa, karkashin Kashim Shettima, suka gabatar da zama a Kaduna, inda suka tattauna yadda za su bullowa taka wa Harkar Musulunci burki a Jihohinsu.

Da kuma zaman kungiyar Limamai da Malamai na Jihar Kaduna a ranar 28/12/2015 da suka gana da Nasiru El-Rufa’i, inda suka bayyana goyon bayansu a kan fadan da yake da ’yan Shi’a a Jihar tasa. Suka kuma bayyana masa cewa hakan da yake yi wani aiki ne da addinin Musulunci ke maraba da shi.

Mun kuwa kawo yadda a 14 ga Junairun 2016, shi ma GOC I Division, Manjo-Janar Adeniyi Oyebade, ya gana da wasu Malaman Wahabiyawa da Limamansu, ya yi masu bayani a kan shirin jami’an tsaro a kan Shi’a da kuma gudummawar da ake bu}ata daga Malaman, har ya ba su kyautar Naira dubu 500 su raba.

Mun kawo kuma inda a ranar 21/12/2015, Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi; daya daga cikin masu ra’ayin Wahabiyanci ya yi jawabi, inda yake yaba wa sojoji a kan abin da suka yi, da sunan hakan taimakon Sunnah ne da magance masu zagin Sahabbai.

Kungiyar Izala, musamman ta bakin shugabanninta, Shaikh Sani Yahaya Jingre, Shaikh Abdullahi Bala Lau da Shaikh Kabiru Gombe sun yi ta wa’azozi suna masu murna da abin da aka yi a Zariya.

Wani abu da ban kawo ba a baya shi ne bayanin daya daga cikin Malaman Izala, Shaikh Gero Argungun ya yi a fadar Sarkin Yawuri, Dakta Muhammad Zayyanu Abdullahi, kwanaki kadan bayan kisan kiyashin na Zariya, inda bayan ya gama yin karairayi ga Shi’a da Shi’anci a karshe ya shiga bayyana alakar su da Shugaban kasa, Muhammadu Buhari wajen kokarin magance Shi’anci a Nijeriya.

A cikin ‘audio’ din jawabin nasa, Shaikh Gero ya bayyana cewa: “Iran komai suna iya yi, shi ya sa da suka gayyaci Shugaban kasar Nijeriya, Muhammadu Buhari, muka yi ‘meeting’ tare da shi, muka fada masa ya yi hattara da wadannan mutane. Muka fada masa ka ji, ka ji ka ji (dangane da Shi’a). Ya ce to zai lura. Muka ce to in kuma ka je Iran kar ka sa bakaken kaya, don yana cikin hanyar yaudararsu, za su yi maka hoto su yada wa duniya cewa ai kai mamba ne daga cikin su.”

Gero ya ce: “Duk alkawuran da ya yi mana, da ya je Iran ya cika su, kun gan shi a ‘setilayit’ cikin fararen kaya.” Ya ci gaba da cewa: “Da (Buhari) ya dawo ya kira wasu daga cikin mu da muka yi ‘meeting’ da shi (kan ya tafi), ni ban samu zuwa ba. Ya ce duk abin da kuka fada mana kun rage, ni na je Iran na gani da idona, Wallahi babu Musulunci.”

Mai karatu, ba za mu tambayi kanmu cewa mene ne damuwar Shugaban kasar Nijeriya, kasar da ba ruwanta da Allah da addini, ba ruwanta da me kake bautawa a ka’idarta, da akidar Shi’anci ko Mazhabar Ahlul Baiti (AS)?

Kuma hatta taron da Buhari ya je Iran taro ne na wasu kasashe guda 8 masu arzikin man fetur a duniya ne. Ko da yake ya gana da Shugaban addini na kasar Iran, Sayyid Khamene’i, amma sam ganawarsu ba ta da alaka da Musulunci ko Shi’anci, face ya ba shi shawarwari ne a kan muhimmancin dogaro-da-kai da nisantar kasashe masu yin mulkin-mallaka.

KARKAREWA

Daga abin da ya bayyana ga mai karatu, zai fahimci cewa tabbas waki’ar Zariya da aka dira a kan Shaikh Zakzaky da almajiransa, wani yunkuri ne na kokarin kawar da Harkar Musulunci da abin da suka kira Shi’anci, ko tasirin Iran a Afirka. Ya fi karfin wani wasan kwaikwayo na cewa, wai an tare hanya ne kawai sai hakan ya auku, kuma har yau bai kawo karshe ba!

Don haka ne ma duk abin da suka yi na kokarin ganin bayan Harkar ta Musulunci abu ya ci tura, har yanzu ba su hakura ba. Suna ci gaba da tsare daruruwan almajiran Shaikh Zakzaky, da shi kansa Shaikh din da maidakinsa, duk da cewa babbar Kotun Tarayya a Abuja ta ba da umurnin a sake shi.

Amma sun take dokar, yanzu ma sun komar da shi Kaduna ne sun gurfanar da shi a gaban wata kotu suna masa haramtacciyar shari’a, wacce insha Allah a rubutu na gaba za mu tashi da bayanin yadda aka dawo da Shaikh Zakzaky Kaduna daga Abuja, zuwa yadda ake gudanar da haramtacciyar shari’arsa a wata babbar kotu da ke garin Kaduna din.

February 25, 2019

Shekaru 3 Da Kisan-kiyashin Zariya (7)


Daga Saifullahi M. Kabir

HANNUN WAHABIYAWA A KISAN-KIYASHIN ZARIYA

Waki’ar Zariya ta auku ne da nufin kawar da Shaikh Ibraheem Zakzaky da Da’awarsa baki-daya. Don haka ma tun kafin aukuwarta da kuma abubuwan da suka biyo baya, sun nuna balo-balo cewa akwai cikakkiyar gudummawar wadanda ake kira Wahabiyawa, wato akwai hannun tushen Wahabiyanci, gidan Sarautar Saudi-Arebiya a cikin duk abin da ya faru.

A nan, zan so mu dogara ga wasu abubuwa guda biyar da suka auku kafin, da kuma bayan kisan-kiyashin na Zariya, kamar haka:

1- Rahoton WISAL TV a kan yaduwar Shi’a a Nijeriya.

2- Kashedin Shekau ga Shaikh Zakzaky, da kuma kai mana hari da sunan Boko Haram.

3- Waki’ar Zariya da yabawar Sarkin Saudiyyah.

4- Rahoton AL’ARABIYYA a yayin zuwan Buhari Katar.

5- Rahoton DW na bayanin MBS a kan dakile tasirin Iran a Afirka.

6- Gudummawar Malaman Wahabiyawa/Izala a kan waki’ar.



RAHOTON TASHAR WISAL TV

Watanni kamar uku kafin aukuwar waki’ar Zariya, a cikin watan Satumbar 2015, wani gidan TV mai suna Wisal, mallakin kasar Saudi-Arebiya, sun yi wani ‘documentary’ inda a cikin sa suka nuna hadarin da ke fuskantar Nijeriya na yaduwar Shi’anci da tasirin Iran a tsakanin matasa, ta hannun Shaikh Ibraheem Zakzaky. Inda a marshe suka nuna takaici ga yadda aka kyale hakan na faruwa a masar da tafi ko’ina girma da tattalin arziki a nahiyar Afirka.

Rahoton ya bayyana cewa: “A duk duniya, a yanzu babu wata masa mafi ha]ari kamar Nijeriya, saboda yadda wata sabuwar fahimta ke ya]uwa har ta mamaye Jihohi hudu, wadda a cikin su akwai masu wannan a}idar kimanin mutane miliyan 25.”

Suka ce: “Wannan cutar da ta bulla a Nijeriya ita ce Shi’a, wacce take yaduwa a tsakanin matasa, wadanda suke makarantun boko suna karantar ilimin likitanci, Kanikanci da wasu fannonin na ilimin boko, wanda kuma ana daukar nauyinsu su je su kware a fannoni daban-daban. Wannan ya sa da yawan matasan ba su san ilimin addini ba. Don haka cutar Shi’anci ke yaduwa da gaggawa a tsakanin matasan Nijeriya.”

Suka ci gaba da cewa: “Wani matashi mai suna Ibraheem Yaqoub Zakzaky ne ya buya a bayan wasu abubuwa, kamar kokarin ’yanto Masallacin Qudus daga hannun Yahudawa da goyon bayan raunanan al’ummar da ake zalunta, yana yaudarar mutanen Nijeriya zuwa ga shiga wannan akidar ta Shi’anci.”

Suka ce: “Malamin, wanda aka san shi a matsayin dan tawaye, ana gayyatar sa ya je Iran don a kara masa ilimi a kan akidar Shi’a. Tsayuwarsa wajen yi wa Shi’anci aiki ya sa shi da mabiyansa sun kai ga suna shirya wasu Muzaharori kamar na Qudus da Ashura. Ya samu nasarar yada wannan cutar ne ta hanyar yin abin da ake kira TAQIYYA, wanda hakan ne ya sa jahilai suke bin sa. Da’awarsa ta fara shahara ne a shekarun tamaninoni (1980s), ta kuma ci gaba da yaduwa a 1990s. Abin da ya fi bata rai shi ne yadda Malamai suka kyale, suka yi shiru a yayin da wannan akidar mai hadari take ci gaba da yaduwa.”

Rahoton na Wisal ya ce: “Zakzaky din, ya yi fice a harkokin diflomasiyya, ta kai ga yana tura dalibai zuwa Jami’ar Tehran a Iran su yi karatu su mware a fannoni, har ma sun fara dawowa Nijeriya suna yada Shi’anci a tsakanin mutane.”

Suka ce: “Suna da wata Jarida da ake kira ALMIZAN, wacce ake buga ta da Hausa, wacce take yaduwa a cikin mutane sosai. Tana taimakawa wajen kara yaduwar Shi’anci. Kuma suna da Website na Hausa da Turanci, wanda suke yada manufofinsu. Kuma suna sayen lokaci a gidajen rediyo da talabijin da jaridu, don su yada manufofinsu ga al’umma. Wannan ne ya ba su damar samun alaka da kyakkyawar fahimta da masu bin Darikun Sufaye, suke haduwa don su fuskanci Ahlus Sunnah.”

Bayan kare rahoton, sai suka saka hira da wani mutum mai suna Dakta Muhammad al-Mubarak, inda yake sharhi a kan abin da aka fa]a. A ciki yake cewa: “A shekarar 1979, shekarar da Khumaini ya yi juyin-juya-hali, babu Shi’a ko daya a Afrika. Sam ba su san Shi’a ba kwata-kwata. Afirka nahiyar Musulmi ne. Eh, akwai wasu kasashe da mafiya yawan mutanen cikin su Musulmi ne, akwai kuma wasu da ka]an ne Musulmi din, amma Shi’a, sam ba a san Shi’a ba a nahiyar baki daya. Haka nan abin yake a da yawa daga kasashen Musulmi, kamar Indinosia.”

Al-Mubarak ya ce: “Amma bayan juyin Khumaini a 1979, sai aka fara aikin yada akidar Shi’anci zuwa kasashe daban-daban. Za mu iya gani yanzu, abin mamaki, Shi’a ta mamaye mafi girman kasashen Afirka a yawan mutane da tattalin arziki. Yanzu muna jin hauhawar farashin mabiya Shi’a a Nijeriya.”

Wannan rahoton, wanda muke da ‘video clip’ dinsa, in mutum ya nazarce shi, zai ga cewa Saudiyya tana jin takaicin yaduwar da’awar Shaikh Ibraheem Zakzaky na Harkar Musulunci da yake yi a tsakanin matasan Nijeriya, wanda kuma suna wa Da’awar kallon Shi’anci ne, saboda ganin cewa Jagoran Harkar da mafiya yawan mabiyansa suna bin tafarkin Ahlul Baiti (AS) ne.

Don haka sun nuna a cikin rahoton cewa, akwai bukatar taka wa yaduwar Shi’ancin birki ta kowane hali, a yayin da suke kokarin nuna cewa Harkar Musulunci din, ko abin da suke kira Shi’anci, na daga cikin tasirin juyin-juya-halin Musulunci ta Iran, wacce Amurka, Isra’ila da ita Saudi-Arebiya din suke tsananin gaba da shi.

KASHEDIN SHEKAU DA KAWO HARIN BOM A KAN ’YAN’UWA

Ba a jima da yin wannan rahoton na Saudiyya a kan takaicinsu na ya]uwar Shi’anci a Nijeriya ba, kamar wata guda bayan hakan, a karshen watan Oktoban 2015, sai ga Shugaban wata kungiyar Wahabiyawa da suke kai hare-haren ta’addanci a Arewacin Nijeriya da aka saka wa suna Boko Haram, mai suna Abubakar Shekau yana kashedi ga Shaikh Zakzaky da almajiransa a kan su gaggauta tuba daga Shi’anci.

A cikin garejeren bidiyon na Shekau, ya furta cewa: “’Yan Kaduna! Kai Zakzaky! ’Yan Shi’a, masu TAQIYYA! Ku tuba!”

Ku lura da wasu abubuwa a cikin wannan garejeriyar maganar ta Shekau, ta yadda yake kiran sunan Shaikh Zakzaky gatsai yana cewa ya tuba, alhali a baya Shekau bai taba kama sunan wani Malamin addini a kasar nan ya yi masa kashedi ba.

Kuma ku lura da yadda ya ambaci kalmar TAQIYYA, wannan kalmar da rahoton Wisal TV ya jaddada, cewa wai Shaikh Zakzaky yana yaudarar matasa ne ta hanyar yin TAQIYYA. Bai zama abin la’akari ba, a yayin da kalmomin Shekau suka dace da na Saudiyya?

To, bayan wannan kashedin kuma da wata guda, har ila yau, a karshen watan Nuwambar 2015, sai aka kawo wa ’yan’uwa Musulmi almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky harin bom a yayin da suke kan hanyarsu na Tattakin juyayin Arba’in din Imam Husaini (AS), daga Kano sun nufo Zariya.

Harin bom ]in da ya ci rayukan almajiran Shaikh Zakzaky kusan mutum 25, an yi nasarar dakile tashin na mutum daya, a yayin da na guda daya ne ya tashi ya kashe wannan adadin. Kwatam sai aka ji a kafafen yada labarai, wai kungiyar Boko Haram ta dauki alhakin kawo wannan harin.

Sai ya zama kamar wannan ne ma’anar kashedin Shekau ga Shaikh Zakzaky da ’yan Shi’a, a yayin da yake cewa su tuba. Da ba su tuba ba, suka ci gaba da Shi’anci, ga shi ya kawo masu harin kunar bakin wake ma.

Sai dai Jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya, Shaikh Ibraheem Zakzaky, a yayin da yake jawabi a wajen rufe taron Arba’in, kwana uku bayan aukuwar harin, ya bayyana cewa ba kowa ke da alhakin kawo harin ba face jami’an tsaron Nijeriya, wa]anda dama suke da alhakin duk abubuwan da ke faruwa a kasar nan da sunan rashin tsaro.

Bayan Shaikh Zakzaky ya dora alhakin harin a kan jami’an tsaron, bisa dalilan da ya bayyana a cikin jawabinsa na ranar Arba’in din, wanda aka gudanar a ranar Alhamis, 3 ga watan Disambar 2015, ba a samu wata murya daga bangaren gwamnati ko jami’an tsaro da ta musanta zargin da Shaikh Zakzaky ya yi a wannan lokacin ba. Sai kawai martanin da sojoji suka bayar kwanaki tara bayan wannan jawabin, wanda shi ne ‘Kisan-Kiyashin Zariya’.

WAKI’AR ZARIYA DA YABAWAR SARKIN SAUDIYYA

Mun riga mun yi bayani a kan waki’ar Zariya tun a babin farko na wannan rubutun, kuma mun kawo yadda wata kafar ya]a labarai ta ‘Pars News Agency’ ta ruwaito a ranar 16/12/2015, kwanaki biyu bayan gama waki’ar ta Zariya, cewa Sarkin Saudiyya, Salman Bin Abdul’azeez ya kira Shugaban kasar Nijeriya, Buhari ya taya shi murna a kan aikin da ya yi na murkushe Harkar Musulunci da sunan wai fada da ta’addanci.

Sarki Salman, ya bayyana kisan-kiyashin Zariya a matsayin yaki da ta’addanci da murkushe ’yan ta’adda. Wanda a rahoton Wisal TV da ya gabata za mu iya gane suna nufin tasirin Iran a Afirka da yaduwar Shi’anci ne suke nufi da Ta’addancin, kamar yadda kuma za mu gani a gaba.

Za mu cigaba insha Allah.

February 19, 2019

An Yi Walimar Cika Shekaru 40 Da Shelanta Harkar Musulunci


Daga Wakilinmu

A wani sabon salon amfani da kafafen sadarwa ta hanyar gudanar da ayyukan alkairi, ’yan’uwa Musulmi almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky, sun gudanar da walimar cika shekaru 40 da shelanta Harkar Musulunci a zauren Khairul Amal da ke shafin WhatsApps.

Walimar, wacce ta gudana a tsawon kwanaki uku a jere, an fara ta ne daga ranar Juma’a, 19 zuwa Lahadi 21 ga Jimadal Ulan a shekarar 1440BH, inda aka gudanar da abubuwa kala-kala da suka hada da kacici-kacici a kan Tarihin Harkar Musulunci, wanda ya gudana a ranar farko.

A rana ta biyu aka gabatar da jawabi a kan tarihin Harkar Musulunci a tsawon shekaru 40 a takaice. Sannan a ranar karshe aka saurari labarurruka daga dukkanin ’yan uwan da ke zauren a kan yadda suka fahimci Harka har suka tsinci kansu ana tafiyar tare da su.

Yayin jawabinsa dangane da maudu’in ‘Harkar Musulunci A Shekaru 40’, wanda ya gudanar a salon rubutu, Jagoran zauren na Khairul Amal, Saifullahi M. Kabir, ya bayyana tarihin Harkar Musulunci tun daga tushenta, inda ya faro da bayani a kan tarihin Jagoran Harkar, wato Shaikh Ibraheem Zakzaky.

Malam Saifullahi M. Kabir, ya yi bayani a kan tarihin haihuwar Shaikh Zakzaky, wanda ya faru a garin Zariya a shekarar 1953, wanda ya yi daidai da shekarar 1372 Hijiriyya. Da kuma yadda Shaikh din ya taso a gidan Malaman Alkur’ani, don haka ya zama tun yana karami ya shagaltu da karatun Alkur’ani ne da zuwa gona don taya Mahaifinsa aiki, har zuwa lokacin da ya sauke Alkur’ani yana da shekaru 14 da haihuwa. Inda daga nan ya fara karatun littattafai a gaban Malamai har ya karanta duk littattafan da ake karantawa a zaurukan ilimi a wancan lokacin.

Ya ci gaba da cewa, bayan da Shaikh Zakzaky ya karanta fannoni daban-daban na ilimin addini da Luggar Larabci, a shekarar 1969 (lokacin yana da shekaru 16) ne aka saka shi a makaranta Nizamiyya, inda ya fara da wata makaranta ta koyon Larabci a Zariya, wacce ake kira Zaria Provincial School. Bayan shekaru biyu, wato 1969 zuwa 1971, ya kammala ta.

Ya bayyana yadda Shaikh Zakzaky ya ci gaba da yin wata makaranta da ake kira Madarasatul Ulumul Arabiyya (School for Arabic Studies) a Kano, inda ya fara ta daga shekarar 1971 zuwa 1975. Ya ce, a wannan makarantar ne Shaikh din ya rika ware lokaci yana zuwa wasu azuzuwa na daban (Advance Level) yana karantar wasu fannoni na Boko da suka ha]a da English, Literature, Economics, Government, Hausa, Arabiyya da kuma Islamic Studies.

Ya ce, wannan ne ya sa Shaikh Zakzaky a yayin gama makarantar ya rubuta jarabawa kashi biyu; ta Grade II din da yake karatu a kansa da kuma na Advance Level ]in da ya karawa kansa. Kuma duk ya ci su. Don haka fitowar sakamakon a shekarar 1976 ya ba shi damar fara karatun Jami’a kai tsaye ba tare da share fage ba. Ya fara karanta Economic, Government da Sociology. Daga baya sai ya fi kwarewa a Economics, don haka sai ya dauke shi a matsayin ‘course’ dinsa. Ya yi Digiri a bangarensa, inda ya kammala a shekarar 1979.


Da ya shiga bayani a kan farkon Da’awar Harkar Musulunci kuwa, Malam Saifullahi M. Kabir, ya bayyana yadda Shaikh Zakzaky ya samu Jami’a a lokacinsa, akwai mutane wasu masu tunani dangane da makomar kasa kashi biyu; kashin farko sune kungiyar dalibai Kiristoci (FCS), wadanda suke da tunanin cewa tsarin da ke iko da kasar ya yi, don haka da bukatar a inganta shi ne kawai ba tare da sauyi ba.

Kashi na biyu kuma sune masu ra’ayin Kwaminisanci, wadanda suke sukar addini gaba daya, suke kuma sukar addinin Musulunci, musamman kan cewa addini kawai an samar da shi ne ma don a samu damar mulkar mutane.

Ya ce; “Kwaminisawa sun rika sukar addinin Musulunci ta hanyar ba da misali da mulkin wasu Sarakuna da Daulolin Gargajiya ko na Musulunci, irin su Mulkin Banu Umayya da Banul Abbas da irin ta’addancin da Sarakunansu suka yi. Haka ma irin mulkin Sarakunan Gargajiya a nan kasar. Sai suke nuna cewa wannan zaluncin da Sarakuna suka ri}a yi shi ne ma koyarwar addinin Musulunci. Don haka suna ganin ba zai taba yiwuwa addini ya zama tsarin adalci ga rayuwar mutane ba. Har ma suna cewa addinin Musulunci ya kafu, ya yi iko ne a duniya saboda lokacin duniya ba ta waye ba.”

Ya ce, da Shaikh Zakzaky ya riski wa]annan ra’ayoyin, sai ya samar da murya ta uku a karkashin inuwar Kungiyar Dalibai Musulmi (MSS), wanda yake a lokacin shi ne Sakataren kungiyar a Jami’ar Ahmadu Bello, kuma mataimakin Shugabanta na kasa kan harkokin kasashen waje. “Don haka sai ya fara kokarin mai da martani ga Kwaminisawa, ta hanyar wanke addinin Musulunci kan cewa, a kawo inda aka ga zalunci a gwamnatin da Manzon Allah (S) ya kafa. Ya kuma rika tabbatar wa da mutanen Jami’a cewa, komawa ga addinin Musulunci shi ne kadai mafita wajen samun adalci da wadatuwar arziki da samun aminci.

“Shaikh Zakzaky ya tsaya kyam a Jami’a wajen fa]akar da ]alibai da Malamai cewa, Musulunci kammalallen nizamin rayuwa ne ga mutum, addini ne, hanyar rayuwa ne, kuma ‘ideology’ ne a lokaci guda. Kuma a kan asasin adalci da ilimi da hujja aka kafa Musulunci. A yayin da shi Kirista yake ganin cewa Addini daban, rayuwa daban, Musulunci na ganin duk abu guda ne. Kwaminisanci na ganin ana danniya a kawo adalci. To, Shaikh Zakzaky ya tabbatar masu da cewa, ba inda za a samu adalci in ba a Musulunci ba.”

Malam Saifullah ya ce; “Da irin haka ne Shaikh Zakzaky ya fara kira ga komawa ga addinin Musulunci da yunkurin tabbatar da shi ya yi iko a doron kasa ma.”

Ya ce, tun daga wannan lokacin na Jami’a ne Hukuma ta fara daukar matakai a kan Shaikh Zakzaky da kiran da yake yi, wanda hakan ya yi sanadin kama shi a daure tun yana Jami’a a lokacin mulkin soja na Obasanjo, da hana shi takardar shaidar kammala Digirinsa.

Da yake magana a kan yadda Shaikh Zakzaky ya sha gwagwarmaya tun daga farkon al’amari, Saifullahi ya bayyana cewa tun da Shaikh Zakzaky ya shelanta da’awar kira a komawa Musulunci a ranar Asabar 5/4/1980 daidai da 20 ga Jimadal Ula, 1400H, daga nan Hukuma ta fara daukan matakan kama shi ta daure a kurkuku na tsawon shekaru.

Ya kawo jerin kame-kamen da aka wa Shaikh Zakzaky da adadin lokacin da ya yi, tun daga kamun gwamnatin Shagari, wanda aka kama Malam Zakzaky a garin Sakkwato a watan Mayun 1981 zuwa May 1984, sannan aka sake shi.

Ya ce; “Shaikh Zakzaky na kurkukun Shagari ne Buhari ya yi juyin mulki ya hambare Shagari. Don haka Shaikh ]in ya fito ne a lokacin Buhari na mulkin Soja. Wata shida bayan fitowarsa kuma, sai Buhari a lokacin yana yayin kame-kamen mutane ya daure, ya sake kama Shaikh Zakzaky ya daure shi tun a watan Disambar 1984, a lokacin Shaikh din bai jima da aure ba. Don haka ma har aka haifa wa Shaikh Zakzaky yaronsa na farko da aka saka wa suna Muhammad, Shaikh din na tsare a kurkukun Buhari soja. Sai a watan Agustan 1985, bayan an hambare Buhari daga mulki, Shaikh Zakzaky ya fito, bayan ya shafe watanni tara a tsare a kurkuku.”

Ya ci gaba da cewa; “Babangida kuwa ya kama Shaikh Zakzaky ne ya tsare tun a watan Maris din 1987 bayan shekaru biyu, a shekarar 1989, sannan aka sake shi. Daga nan ne kuma ba a sake kama Malam Zakzaky ba sai a lokacin Mulkin Janaral Sani Abacha, wanda ya kama shi a shekarar 1996. Bayan mutuwar Abacha, a shekarar 1999 Shaikh din ya fito a lokacin rikon kwaryar Abdussalami Abubakar.

Ya ce; “A yanzu haka Shaikh Zakzaky ya kasance a tsare tun kimanin shekaru uku da suka gabata, bayan da sojoji suka yi dirar mikiya a kansa, suka kashe iyalai, dangi da almajiransa fiye da 1,000 a Zariya bisa umurnin Shugaban kasa, Muhammadu Buhari.”

Ya bayyana babban darasin da ke cikin bitar tarihi, inda ya ce shi ne don a koyi abubuwan kirki. Ya ce; “Tabbas daga waiwayen tarihin Harkar Musulunci da Jagoranta ’yan’uwa za su koyi dakewa, kamar yadda Shaikh Zakzaky ya iya fuskantar wannan baranaza da jarabawowin a tsawon wa]annan shekarun, amma har yau bai sauya hadafi, ko manufarsa ba.”

A yayin taron, an raba kyaututtukan katin waya, ga wadanda suka lashe gasar kacici-kacici a kan Tarihin Harkar Musulunci, wanda Malam Adamun Adamawa ya jagoranta.

Daga jaridar ALMIZAN ta 26/5/1440

Shekaru 3 da Kisan-kiyashin Zariya (6)


Daga Saifullahi M. Kabir

WAKI’AR FREE ZAKZAKY A KADUNA DA ABUJA

A ranar 6/1/2018 labari ya iske ’yan’uwa daga dangi da makusantan Shaikh Zakzaky, cewa jikinsa ya tashi sosai har ma yana fuskantar barazanar shanyewar barin jiki! Wannan ya sa hankalin ’yan’uwa ya tashi. A cikin wannan daren na ranar 6/1/2018 aka rika gudanar da Muzaharori a wasu garuruwa, musamman a Bauchi da Kano.

An ci gaba da Muzaharar kira ga gwamnati ta saki Shaikh Zakzaky domin ya je ya nema ma kansa lafiya a safiyar Lahadi, 7/8/2018 a kusan dukkan birane da kauyukan kasar nan.

A wannan ranar ta Lahadi ’yan sanda sun bude wuta a kan masu Muzaharar a Kaduna, inda suka jikkata mutane biyar, har biyu daga cikin su suka samu Shahada; Shahid Muhammad Auwal Kakuri da Shahid Abdulmalik Sani. Shaikh Zango ya jagoranci yi masu janaza washe-gari Litinin a Kaduna.

Litinin 8/1/2018 ne ’yan’uwa suka fara cincirindon shiga Abuja don fara gudanar da Muzaharorin kira a saki Shaikh Zakzaky na sai baba-ta-gani. A wannan ranar ’yan sanda sun bude wa masu muzaharar wuta, inda suka kama wasu, kuma suka jikkata da dama, amma ba a samu Shahidi ba.

Ranar Talata 9/1/2018 ’yan’uwa almajiran Shaikh Zakzaky sun sake fitowa Muzaharar kira a sake shi a tsakiyar garin Abuja. A ran nan ma ’yan sandan sun kuma bude wuta a kan ’yan’uwa, inda suka jikkata da dama, suka kama ’yan’uwa masu yawa. A wannan ranar ne ’yan sanda suka harbi Shaikh Kasim Umar Sakkwato a cinyarsa, wanda bayan jinya da ya sha na tsawon kimanin kusan wata guda, ya yi shahada a ranar 5/2/2017.

Shaikh Saleh Lazare na jagorantar janazar Shaheed Qaseem Umar 

Washegari Laraba 10/1/2018 ’yan’uwa suka sake fitowa don Muzaharar Free Zakzaky a Abuja din. Ran nan ma jami’an tsaron sun bude wuta a kan masu Muzaharar, inda suka datse gaba da bayan Muzaharar, suka rika amfani da wasu mashina suna ratsa cikin ’yan’uwa suna watsa musu Tiyagas, bayan sun galabaitar da su, sai suka fara harbi da harsasai masu rai, inda nan take suka kashe mutum biyu; Shahid Aminu Ibrahim Gashua da kuma Shahid Usman Dunari, wanda shi sai bayan kwanaki 9 da shahadarsa sannan ’yan sanda suka ba da gawarsa aka yi mata janaza. Sun kuma jikkata gomomi a yayin da suka kama ’yan’uwa masu yawa.

Alhamis 11/1/2018 aka ci gaba da Muzaharar, sai dai an tashi lafiya a wannan ranar. Amma a ranar Juma’a 12/1/2018 an yi Muzaharar ne daga Babban masallacin Kasa na Abuja, inda ’yan sanda suka harba Tiyagas a kan masu Muzaharar.

A ci gaba da Muzaharar kullum a garin Abuja don fafutukar ganin an saki Jagoran Harkar Musulunci daga haramtaccen tsarewar da gwamnatin Buhari ke masa, yanzu haka Muzaharar ta kullum, wadda ake kira Fafutukar Abuja ko ‘Abuja Struggle’ a Turance, ta cika shekara guda cur ba tare da fashi ba.

Sai dai kuma, yana daga cikin natijojin wadannan waki’o’in na mako guda a jere, yadda ya zama ranar Asabar 13/1/2018 gwamnatin Nijeriya ta nuna Shaikh Ibraheem Zakzaky a Talabijin, inda ya yi bayani a kan yanayin halin da yake ciki, ya kuma yi godiya ga ’yan Nijeriya da ke yi masa addu’a.

Kodayake sun yayyanke video din (editing), amma dai ya faranta ran masoyansa, ko ba komai ran nan ne karon farko da aka gan shi a ‘Video’ aka ji maganarsa tun bayan kama shi da Sojoji suka yi a ranar 14/12/2015, kimanin shekaru biyu da wata daya tsakanin kamun nasa da nuna shi a farko.

WAKI’O’IN GABAN OFISHIN NHRC

A ranar Litinin 16/4/2018 ’yan sanda suka sake bude wa ’yan’uwa masu Muzaharar kira a saki Shaikh Ibraheem Zakzaky wuta a kusa da ofishin Hukumar Kare Hakkin Dan’adam (NHRC) da ke Abuja. Sun jikkata ’yan’uwa da dama a yayin harbi da Tiyagas, ruwan zafi da kuma harsashi mai rai.

Cikin wadanda suka raunata har da Ahmad Rufa’i Abubakar Dodo, wanda Allah ya kaddara shahadarsa bayan kwana biyu. A ranar 19/4/2018 ya yi Shahada a wani asibiti a garin Kano. A wannan ranar ’yan sanda sun kama ’yan’uwa kusan 100.

An sanya ranar 23/4/2018 ne a matsayin ranar da za a yi jana’izar Shahid Ahmad Rufa’i, inda aka yi Muzahara zuwa Ofishin Hukumar Kare Hakkin na Dan’adam (NHRC) a Abujan, bayan an kai masu koke cewa wannan gawar ’yan sanda sun harbe ta ne a gaban ofishinsu a makon da ya gabata, sun dauki hoton gawar sun yi bayanai, har ma an gudanar da Sallah ga Shahidin. A gaban ofishin Hukumar ’yan sanda suka sake bude wa ’yan uwa wuta, inda suka kama fiye da 100, tare da jikkata gomomi.

WAKI’O’IN KAI SHAIKH ZAKZAKY KOTU

Bayan dawo da Shaikh Zakzaky da matarsa garin Kaduna da kuma gurfanar da su a gaban wata kotu don yi masu haramtacciyar Shari’ar da El-Rufa’i ya shigar da su a madadin gwamnatin Jihar Kaduna, a ranar Laraba 20 ga Yuni, 2018, jajiberin ranar komawa kotu da Shaikh din, ’yan’uwa a Kaduna sun gudanar da gagarumar Muzaharar kira a saki Shaikh Zakzaky din da kuma yin Allah wadai da kai shi wannan kotun, alhali wata kotun ta yi umurni a sake shi tun fiye da shekara guda gwamnati ba ta bi umurnin ba. Nan ’yan sanda suka bude wuta a kan masu Muzaharar, inda suka raunata mutane uku, amma ba a samu Shahidi a wannan ranar ba.

Ranar Alhamis 21/6/2018 aka ayyana don dawowa kotu da ci gaba da shari’ar Shaikh Zakzaky (H), kodayake ba a yi zaman kotun ba, amma ’yan’uwa sun sake fitowa Muzaharar kira a saki Shaikh Zakzaky a garin na Kaduna, inda ’yan sanda suka sake bude wuta, sun shahadantar da mutum 3 masu suna; Shahid Imrana Ringim, Shahid Idris Alhasan Kaduna da kuma Shahid Sagir Adamu (Baba Bauchi), sun kuma jikkata da dama.

’Yan sandan sun tafi da gawar Shahid Sagir suka hada ta da ta wani dan sanda da suka kashe a wannan ranar, suka kai su dakin ajiye gawa a wani asibiti. Har zuwa yanzu (kimanin watanni hudu ke nan) ba su ba da gawarsa an masa jana’iza ba.

WAKI’O’IN RANAR ASHURA 1440/2018

Ranar 20/9/2018 ta dace da ranar Ashura ta shekarar 1440H, ’yan’uwa sun gudanar da Muzaharorin Ashura a dukkan birane da kauyukan kasar nan ciki har da birnin Tarayya Abuja.

Sai dai a Zariya ’yan sanda sun harba Tiyagas a kan masu Muzaharar bayan an tashi, inda suka raunata ’yan’uwa guda hudu. Wasu zauna-gari-banza sun dira a kan masu Muzaharar ta Ashura a garin Suleja, inda suka jikkata wasu mata da kananan yara. Sannan kuma wasu zauna-gari-banzan bisa rakiyar jami’an tsaro sun je da nufin kona Fudiyyar Anchau da Pambeguwa da ke Jihar Kaduna, sun wargaza ta suka tafi.

A Abuja kuwa, jami’an tsaron sun yi mummunan shiri, don kuwa har jami’an da ke kula da tsaron Shugaban kasa (Guards Brigade) sun fito sun rika bin Muzaharar, amma Allah ya nufi an kammala lafiya.

Sai a garin Potiskum da ke Jihar Yobe ne sojoji suka bude wuta bayan an kammala Muzaharar, suka raunata mutane hudu, daya mutumin gari ne, wanda a nan take Allah ya yi masa cikawa, mutum na biyu kuma da suka kashe shi ne Shahid Ali Zakariyya, wanda ya yi shahada bayan jinyar kwanaki 10 da harbin nasa.

WAKI’AR TATTAKI 2018 A ABUJA

Ranar Asabar 27/10/2018 aka fara waki’ar Tattakin Arba’in a garin Abuja. Sojoji sun bude wuta a kan masu Tattakin a daidai gadar Zuba, inda suka kashe mutum 6 a wannan ranar, tare da jikkata da dama.

Litinin 29/10/2018 sojojin suka sake bude wuta a kan masu Tattakin Arba’in ta yankin Maraba, inda suka kashe mutum akalla 40, tare da jikkata fiye da mutum 100.

Wanda ya jagoranci wannan kisan-kiyashin shi ne Kwamandan jami’an tsaro masu kula da fadar Shugaban kasa (Guards Brigade), Birgediya-Janar Musa Yusuf.

Washegari Talata, 30/10/2018, daidai da ranar Arba’in din Imam Husain (AS), gamayyar soja da ’yan sanda suka kuma bude wuta a kan ’yan’uwa a Abuja, suka kashe mutum biyar da jikkata da dama.

A jerin kwanaki uku din nan, an samu Shahidai akalla 49, yayin da fiye da mutum 110 suka jikkata. Sun kuma kama fiye da ’yan’uwa 200 har zuwa yanzu wasu suna tsare.

KARKAREWA

A takaice, wadannan wasu ne daga waki’o’in da na iya taskacewa sun auku a tsawon shekaru uku, tun bayan waki’ar Zariya ta Disambar 2015. Duk wannan yana daga cikin yunkurin gwamnatin Nijeriya karasa kwangilar da ta karbo daga Amurka da Isra’ila da Saudiyya na kokarin ganin bayan Shaikh Zakzaky da kawo karshen Harkar Musulunci a Nijeriya.

Insha Allah a rubutu na gaba za mu duba hannun Saudiyya da gudummawar Malaman Wahabiyawa a cikin wannan Waki’ar ta Zariya da abubuwan da suka biyo bayanta.