Daga Saifullahi M Kabir
A yayin da Amirulmuminin (AS) yake ta sabgogin kokarin ganin ya yi wa Manzon Allah (S) sutura ya bizne shi, sai ya zama na su kuma Muhajirun da Ansar sun watsar da wannan sha’anin na jana’izar Annabi, suka dankara ma kansu hada-hadar kokarin sun fitar ma da kansu Khalifan da ya dace da son ransu.
Nan suka nufi wani waje da ake cema ‘Sakifar Bani Sa’ada, inda kowace Kabila daga Kabilun Madina kowannensu yake raya cewa lazim su ne za su samu matsayin su halifci Annabi (S). Abin mamaki sosai, ta yadda za mu ga cewa kwata-kwata, bai wuce wata 2 ba Manzon Allah (S) ya tara su a Ghadeer Khum ya halifantar da Imam Ali (AS) a matsayin halifansa a cikinsu a bayansa. Amma kuma yau ga Manzon nan ya koma ga Allah (T), ko bizne shi ba a yi ba, amma har sun juya ma umurninsa baya.
Dama a cikin Alkur’ani, Allah (T) yace: “Muhammadu ba kowa bane face Manzo, kuma Manzonni sun gabace shi. Shin idan ya mutu, ko kuma aka kashe shi, za ku (yi ridda) ne ku koma ga abin da diga-diginku ke kai (Jahiliyya)?” Sai kuwa mutanen nan suka ba Allah amsa a aikace da cewa Eh! Mun zabi mu watsar da abin da ya zo da shi, mu yi son ranmu. Wanda hakan shine Jahiliyya din.
Ba za ku yi mamakin juya bayansu da kin karban wasiccin Manzon Allah (S) ba a yayin da ya yi wafati, tunda a halin da yake da ransa ma, ya musu umurni da abubuwa da dama sun ki yi, kamar yadda muka kawo misalsalai a baya.
Daga misali, maganar kawo abin rubutu, wanda suka maid a abin hayaniya da hargowa, har ya kare yace duk su fita su bashi waje. Da kuma batun tura su yaki da ya yi a karkashin Usamatu Dan Zaidu, da suka ki su je, suka dawo suka tsaya a kansa, ya daga kai ya gansu yace Allah ya la’anci duk wanda bai kama hanya ya tafi ba. Kuma basu je din ba. Yana raye kenan. Ina kuma ga ace ga shi sun ga baya numfashi? Bai da halin yi musu magana? Sai su bi umurninsa a wannan lokacin? Eh, haka ya kamata, amma ba su yi hakan ba!
Toh, a Sakifa sai Muhajirun (Wato mutanen Makkah) suka yi ikirarin cewa lallai su ne suka fi dacewa da a samu halifan Annabi a cikinsu, saboda sun fi Ansar (mutanen Madina) dadewa da zama Musulmi, sun kasance tare da Annabin kafin Ansar. Gori ko fariya kala-kala, ciki harda cewa su ne suka iya baro gidajensu a Makkah da dukiyoyinsu da kuma kayayyakinsu suka biyo Manzon Allah zuwa Hijirar da ya yi.
Ansar kuma suka ce su ne ya kamata su zama Halifan Annabi saboda sun ba Annabi mafaka a Madina a yayin da aka kore shi daga Makkah. Kuma suka ba shi kariya a yayin da karfafan makiya suka taso shi a gaba da yaki. Suma cikin nasu gorin, har da cewa, ai shekara 13 Annabi ya yi a Makkah yana da’awa, amma sai ‘yan kadan suka karba masa. Amma tunda ya zo garesu, suka karba hannu bibiyu. Dan haka sune ya fi dacewa su halifance shi tunda sune suka taimaki Musuluncin da yazo da shi ya karfafa.
Wani abu da ya kamata ku sani shine, a daidai lokacin da suke can suna wannan hargowar, shi Imam Ali (AS) tare da Abbas (AS) da wasu tsiraru suna wajen jana’izar Annabi. To a nan ne Abbas yace ma Imam Ali (AS); “Ya Aliy, miko hannunka na yi maka mubayi’a.” Sai ya zama Ammin Manzon Allah (Abbas) ya yi ma ‘Dan Ammin Manzon Allah (Ali) mubayi’a kenan. Abbas yace: “Su ma mutanen da suke cikin gidan nan duk su yi maka bai’ar. Domin idan akai hakan to ba zai kwantu ba (cikin sauki ba).”
Sai Imam Ali (AS) yace masa: “Ah! Wane ne kake tunanin zai ce wannan al’amarin nashi ne ba namu ba?” (Amirulmuminin na masa tambayar a sigar yanke uzuri ba wai don bai san za a kwace masa din ba).
An ce Abbas ya je wajen Abubakar da Ummar ya tambaye su daya bayan daya, shin Manzon Allah ya muku wasicci da wani abu? Suka ce masa, a’a. Amma duk da hakan ya nemi Ali ya kawo hannunsa dai ya masa bai’a shi da mutanen gidan. Amma Imam Ali (AS) yace masa: “Mu shagaltu da al’amarin Jana’izar nan tukunna. Shine aula akan komai.”
Wannan kamar yadda mai littafin Imama Was-siyasa ya kawo kenan. Wanda idan abin muce, Ah! to ina ce Annabi ya sanar da Imam Ali abin da za a yin? Sai muce eh mana. Amma kana tsammanin Imam zai bar abin daya dace ne ya je ga rudin duniya saboda kar ta kubuce masa?
To mu komo ga Sakifar. A yayin da Abubakar ya ji labarin abin da ke wakana a Sakifa, sai ya yi maza ya sanar da Umar, sai sukai maza suka tafi suma, a hanya suka hadu da Abu Ubaida binil Jarra, sai suka rankaya. Yayin da suka isa, suka iske Ansar sun tsayar da Sa’ad bin Ubadah a matsayin wanda zai jagoranci Musulmi. Sai Umar yace ina, hakan ba zai yiwu ba fa. Lazim ne a samu halifan nan daga Muhajirun ne.
A nan sai Abubakar ya tashi ya musu huduba. Ya yabi Ansar a cikinta sosai ya musu godiya da duk abin da suka ma Musulunci, don ya kwantar musu da hankali, sannan yace musu, shi yana ganin wannan al’amarin ko dai ya kasance a hannun Abu Ubaidata ko ga Umar. Kowanne a cikinsu ya san kan wannan al’amarin.
Sai Umar da Abu Ubaida suka ce, bai cancanta ga wani a cikin mutane ya gabaceka ba Ya Ababakar. Suka ce miko hannu mun maka bai’a. To a nan sai Ansar wadanda suke da manyan kabiloli guda biyu, suka samu sabani a tsakaninsu (Aus da Khazraj). Dama sun kasance masu fada da juna kafin Manzon Allah ya zo ya hada kansu, aiko rannan suka sake ballewa. Bashir dan Sa’ad, wanda yake daga kabilar Aws ne, sai ya mike shima ya ma Abubakar bai’a, saboda ya kawar da yunkurin Ansar na yin bai’a ga Sa’ad bin Ubada, wanda yake shine shugaban kabilar Khazraj dama. Sai nan da nan dai ya zama rinjayen kuri’ar tana kan Muhajirin ne.
Labarin Sakifa na da tsawo, ba shi kawai muke son yi ba. A takaice, su Banu Hashin sun taru ga Imam Ali (AS) akan lallai shi za su ma bai’a, domin kuwa tunda tabbas Manzon Allah (S) ya bar Amirulmumin (AS) ne a matsayin halifansa a bayansa, to ba su ga dalilin da zai sa su yi mubayi’a ga wanin Ali ba alhali yana raye.
A cikin Imama Was-Siyasa, ya kawo cewa, Imam Ali da Abbas (AS) da wadanda suke tare da su na daga Banu Hashim, sun kasance a tare a gidan Sayyida Fatima, tare da su akwai Zubair binil Auwam (wanda yake shi mahaifiyarsa Bahashimiya ce, dan haka yake jingina kansa da Hashimawa).
Sai Umar ya debi tawaga suka nufi gidan, tare da shi akwai Usair Bin Hudair da Salamatu bin Salama, suka je kofar gidan suka ce, Ku fito ku ma Abubakar bai’a. Amma Imam (AS) suka ki. Sai suka ji Umar yana cewa ku saka ma gidan wuta! A nan sai Imam (AS) suka fito tare da Abbas da Zubair. Zubair ya daga takobi, sai Umar yace ma Salamat maza ka rike shi. Sai suka taru a kan su Imam (AS) suka tafi da su.
Suna ji a wannan lokacin Sayyida Zahara (SA) tana kai kara wajen Annabi, tana cewa: “Ya Babana, kaga daga wafatinka abin da yake samunmu daga dan Abu Quhafa. Dubi yadda cikin lokaci suka watsar da kalmomin da ka ambata a Ghadeer cewa; “Ali a wajenka kamar Harun ne a wajen Musa.” Sai ya zama wasu daga cikinsu har sun yanke cewa lallai ba da su a wannan aika-aikar ba. Tunda suka ji Tsokar jikin Annabi na kai kara gareshi. Wasu daga nan suka bar wajen. Amma su Umar da wadanda ke tare da shi da ba su da nufin yin nadama, sai suka daure Imam (AS) da igiya, wai don kar ya gudu, suka ja shi zuwa Masallaci akan ya yi bai’a.
Dubi abin ban mamaki, Alin da yake zakin Allah, gwarzon Badar, Uhudu, Khandaq, Kyaibar da Hunain, amma shi yau wannan mutumin da bai tana jurewa ya tsaya a fagen daga ba yake ja da igiya. Hakan na nuna girman hakuri da juriyan Imam ne da kuma sallamawa da bin umurninsa na Annabi (S) kamar yadda muka kawo a baya. Tare da kiyaye maslahar Musulunci a lokacin.
Da aka kai Imam Ali gaban Halifan nasu, Sai Umar yace idan har Imam bai yi mubayi’a ga Abubakar ba zai kashe shi. Sai Imam Ali yace masa: “Yanzu za ka kashe Bawan Allah, kuma dan’uwan Manzon Allah?” Imam Ali yace musu: “Ni bawan Allah ne kuma dan’uwan Manzon Allah. Ni ne naked a hakki akan wannan al’amarin (halifanci) akanku, ba zan muku mubayi’a ba alhali ku ne kuke da hakki akan ku min bai’a.” Yace musu: “Kun karbe wannan al’amarin (Halifanci) daga hannun Ansar, kun kafa musu hujja da kusancinku da Annabi, amma kuma sai ku kwace shi daga garemu mu iyalan gidan Annabin? Ashe ba ku ne kuka ce ma Ansar kun karbi wannan mulkin vane daga gare su saboda Annabi ya kasance ne daga cikinku? Suka sallama muku al’amarin.”
Imam ya cigaba da cewa: “Ni ina kafa muku hujja da irin abin da kuka kafawa Ansar hujja da shi; Mu muka fi cancanta da halifcin Annabi yana raye ko ba shi. Ku kyalemu idan kun kasance masu imani, idan kuwa ba haka ba, to za a yi muku bai’a bisa zalunci alhali kuna sane!”
Da Umar ya ga Abubakar ya yi shiru bai ce uffan ba a lokacin. Sai yace masa, ba za ka nemi da ya maka bai’a ba ko? Sai Abubakar yace masa, matukar Fatima tana raye, to ba zan tilasta mijinta ya min bai’a ba. Wannan yasa suka sake Imam Ali a lokacin. A nan sai Imam (AS) ya nufi kabarin Manzon Allah yana kai masa kukan yadda mutane suka canza daga barinsa wannan duniyar.
To, ta iya yiwuwa jin maganar Abubakar na cewa ba zai iya tilasta Imam ya yi bai’a ba matukar Sayyida Zahara tana raye. Wannan ne ya ba dan Sahhaqu karfin hali na ganin yadda zai bullo ma al’amarin. Nan ya ga to a kashe Fatima din mana, indai hakan zai sa Ali ya yi bai’a a huta! Wannan kuma shi ya kai ga komawa sake kai hari gidan Sayyida Zahra (S), wanda ya yi sanadiyyar karya kashin awazanta da kashe tayinta, kona gidanta da ma shahadarta. Kamar yadda insha Allah za mu zo da bayanin yadda abubuwan suka faru.
February 11, 2018
Tsage Gaskiya (9)
Daga Saifullahi M Kabir
Manzon Allah (S) wata rana ya kira Sayyida Zahara (S), sai yake ce mata: “Ya ke ‘ya ta, hakika za a zalunce ki a bayana. Kuma za a raunata ki a bayana. Duk wanda ya cutar da key a cutar da ni, wanda duk ya miki hujumi ya min hujumi ne, wanda kuwa ya sadar gareki, to ya sadar gareni ne, kuma wanda ya yanke miki ya yanke mini ne. Domin ke daga gareni kike, kuma ni ma daga ke nake, ku ma ke tsoka ce daga jikina, kuma kece ruhina.” Sannan Manzon Allah (S) yace mata: “Ga Allah kadai nake gama duk wanda ya zalunceki daga cikin al’ummata.”
Wata rana Manzon Allah (S) ya kira Imam Ali, Hasan, Husain da Sayyida Fatima (SA), sannan sai yace ma duk wadanda suke dakin su fita masa. Sanna yace ma Ummu Salma, ke ki tsaya a kofar dakin kar ki bar kowa ya shigo. Sannan sai yace ma Imam Ali (AS): “Ka matso kusa da ni.” Sai Imam ya matsa. Sannan sai ya kama hannun Sayyida Fatima ya daura shi akan kirjinsa na lokaci mai tsawo. Ya kuma rike hannun Imam Ali da dayan hannunsa. Yayin da Manzon Allah ya so ya musu Magana, sai ya kasa, sai kawai ya kama hawaye kawai. Ya yi kuka mai tsanani, sannan suma duka suka fashe da kuka tare da shi.
Sai Sayyida tace masa: “Ya Ma’aikin Allah zuciyata ta raunana saboda kukanka. Ya kai shugaban Manzonni daga farko har karshe, Ya kai amintaccen Ubangijinsa kuma ManzonSa, Ya Masoyinsa kuma Annabinsa. Wane ne zai kasance ga ‘Yayan nan (Hasan da Husaini) bayanka? Kuma musiba za ta sauka min a bayanka? Wane ne ga Ali dan’uwanka kuma mai taimakon addininka? Wane ne da Wahayin Allah da al’amarinsa? ”
Sai Manzon Allah (S) ya cigaba da hawaye har ya rufe fuskarsa saboda wannan kukan. Sannan Ali, Hasan da Husain (AS) suma duk kuka suke yi. Har zuwa lokacin da ya daga kansa, yana kallonsu. Hannun Fatima (SA) yana rike a hannunsa. Sai ya hada hannun da na Imam Ali (AS) sannan yace masa: “Ya kai Baban Hasan. Amanar Allah da na Annabinsa yana hannunka, Ka kiyaye ma Allah da ni a cikinsu, na san za ka aikata hakan.”
Manzon Allah (S) ya cigaba da cewa: “Ya Aliy. Ka kiyaye abin da duk Fatima ta umurceka da su, hakika na umurceta da abubuwan da Jabara’ilu ya mata umurni da su. Ka sani ya kai Ali, cewa ni mai yarda ne ga duk wanda Fatima ta yarda da shi, haka ma Ubangijina da Mala’ikunsa. Ya Ali, azaba ta tabbata ga duk wanda ya zalunceta, azaba ta tabbata ga duk wanda ya kwace mata hakkinta. Azaba ta tabbata ga duk wanda ya ya keta alfarmarta.” Aka ce a sanna sai Sayyida ta mika kanta ga Annabi (S), sai ya shafa kanta, yace mata: “Babanki fansarki ya ke Fatima.”
To, wannan kamar na kawo muku karishen wasu ruwayoyi ne kamar yadda na faro a darasin da ya gabata. Don ya zama bai buya mana ba cewa dama tun farko Manzon Allah (S) ya sanar da Sayyida Zahra (S) da iyalanta cewa za a zalunce su, za a kwace hakkinta da na mijinta kuma ma za a doke ta har a yi mata barin cikinta. Amma Manzon Allah ya musu wasiyya da su yi hakuri.
Allah mai cika alkawari kuwa, sai ya zama ba wani abu da basu gani ba a bayan Manzon Allah (S) cikin abubuwan da ya fada musu za su riske su.
Manzon Allah (s) yana komawa ga Allah (T), a yayin da Amirulmuminin (AS) yake ta sabgogin kokarin ganin ya yi masa sutura ya bizne shi, sai ya zamana su kuma Muhajirun da Ansar daga Sahabbai sun watsar da wannan sha’anin na jana’izar Annabi, suka dankara ma kansu hada-hadar kokarin sun fitar ma da kansu Khalifan da ya dace da son ransu. Nan suka nufi wani zuren taro da ake cema ‘Sakifar Banu Sa’ida, inda kowace Kabila daga Kabilun Madina kowannensu yake raya cewa lazim su ne za su samu matsayi na su halifci Annabi (S).
Abin mamaki sosai, ta yadda za mu ga cewa kwata-kwata, bai wuce watanni biyu ba Manzon Allah (S) ya tara su a Ghadeer Khum ya halifantar da Imam Ali (AS) a matsayin halifansa a cikinsu a bayansa. Labarin Ghadeer abu ne da yake kamar hasken rana, sam bai buya ma mutanen wannan lokacin ba bare na wancan zamanin. Amma kuma yau ga Manzon nan ya koma ga Allah (T), ko bizne shi ba a yi ba, amma har sun juya ma umurninsa baya.
Dama a cikin Alkur’ani, Allah (T) yace: “Muhammadu ba kowa bane face Manzo, kuma Manzonni sun gabace shi. Shin idan ya mutu, ko kuma aka kashe shi, za ku (yi ridda) ne ku koma ga abin da diga-diginku ke kai (Jahiliyya)?” Sai kuwa mutanen nan suka ba Allah amsa a aikace da cewa Eh! Mun zabi mu watsar da abin da ya zo da shi, mu yi son ranmu. Wanda hakan shine Jahiliyya din.
Ba za ku yi mamakin juya bayansu da kin karban wasiccin Manzon Allah (S) ba a yayin da ya yi wafati, tunda a halin da yake da ransa ma, ya musu umurni da abubuwa da dama sun ki yi. Ai bai buya ma mai bibiyan nazarin nan ba inda ya zama ya inganta cewa Manzon Allah (S) ya nemi su bashi abin rubutu sun hana, har ma Umar ya fadawa Annabi bakar magana ko? Da kuma inda yace kar su bashi abu suka dura masa, har ma wata tace sai suka dura masa alhali yana hana su, suka ki.
To, wani abu da ba mu yi magana a kansa da zurfi ba a baya shine batun tura su yaki da Annabi (S) ya yi a karkashin Usamatu Dan Zaidu, da suka ki su je, suka dawo suka tsaya a kansa, ya daga kai ya gansu yace Allah ya la’anci duk wanda bai kama hanya ya tafi ba. Kuma basu je din ba.
Yana raye kenan. Ina kuma ga ace ga shi sun ga baya numfashi? Bai da halin yi musu magana? Sai su bi umurninsa a wannan lokacin? Eh haka ya kamata. Amma ba su yi hakan ba.
Insha Allah, mu tsaya a nan sai mu cigaba da labarin Saqifa kamar yadda Imam Abu Muhammad, Ibn Qutaiba al-Dinawari, wannan malamin Ahlussunah da ya rasu a shekara ta 276 bayan hijira (yau kimanin shekara 1193 da rasuwarsa) ya kawo a littafinsa Al’imama was-Siyasa.
Manzon Allah (S) wata rana ya kira Sayyida Zahara (S), sai yake ce mata: “Ya ke ‘ya ta, hakika za a zalunce ki a bayana. Kuma za a raunata ki a bayana. Duk wanda ya cutar da key a cutar da ni, wanda duk ya miki hujumi ya min hujumi ne, wanda kuwa ya sadar gareki, to ya sadar gareni ne, kuma wanda ya yanke miki ya yanke mini ne. Domin ke daga gareni kike, kuma ni ma daga ke nake, ku ma ke tsoka ce daga jikina, kuma kece ruhina.” Sannan Manzon Allah (S) yace mata: “Ga Allah kadai nake gama duk wanda ya zalunceki daga cikin al’ummata.”
Wata rana Manzon Allah (S) ya kira Imam Ali, Hasan, Husain da Sayyida Fatima (SA), sannan sai yace ma duk wadanda suke dakin su fita masa. Sanna yace ma Ummu Salma, ke ki tsaya a kofar dakin kar ki bar kowa ya shigo. Sannan sai yace ma Imam Ali (AS): “Ka matso kusa da ni.” Sai Imam ya matsa. Sannan sai ya kama hannun Sayyida Fatima ya daura shi akan kirjinsa na lokaci mai tsawo. Ya kuma rike hannun Imam Ali da dayan hannunsa. Yayin da Manzon Allah ya so ya musu Magana, sai ya kasa, sai kawai ya kama hawaye kawai. Ya yi kuka mai tsanani, sannan suma duka suka fashe da kuka tare da shi.
Sai Sayyida tace masa: “Ya Ma’aikin Allah zuciyata ta raunana saboda kukanka. Ya kai shugaban Manzonni daga farko har karshe, Ya kai amintaccen Ubangijinsa kuma ManzonSa, Ya Masoyinsa kuma Annabinsa. Wane ne zai kasance ga ‘Yayan nan (Hasan da Husaini) bayanka? Kuma musiba za ta sauka min a bayanka? Wane ne ga Ali dan’uwanka kuma mai taimakon addininka? Wane ne da Wahayin Allah da al’amarinsa? ”
Sai Manzon Allah (S) ya cigaba da hawaye har ya rufe fuskarsa saboda wannan kukan. Sannan Ali, Hasan da Husain (AS) suma duk kuka suke yi. Har zuwa lokacin da ya daga kansa, yana kallonsu. Hannun Fatima (SA) yana rike a hannunsa. Sai ya hada hannun da na Imam Ali (AS) sannan yace masa: “Ya kai Baban Hasan. Amanar Allah da na Annabinsa yana hannunka, Ka kiyaye ma Allah da ni a cikinsu, na san za ka aikata hakan.”
Manzon Allah (S) ya cigaba da cewa: “Ya Aliy. Ka kiyaye abin da duk Fatima ta umurceka da su, hakika na umurceta da abubuwan da Jabara’ilu ya mata umurni da su. Ka sani ya kai Ali, cewa ni mai yarda ne ga duk wanda Fatima ta yarda da shi, haka ma Ubangijina da Mala’ikunsa. Ya Ali, azaba ta tabbata ga duk wanda ya zalunceta, azaba ta tabbata ga duk wanda ya kwace mata hakkinta. Azaba ta tabbata ga duk wanda ya ya keta alfarmarta.” Aka ce a sanna sai Sayyida ta mika kanta ga Annabi (S), sai ya shafa kanta, yace mata: “Babanki fansarki ya ke Fatima.”
To, wannan kamar na kawo muku karishen wasu ruwayoyi ne kamar yadda na faro a darasin da ya gabata. Don ya zama bai buya mana ba cewa dama tun farko Manzon Allah (S) ya sanar da Sayyida Zahra (S) da iyalanta cewa za a zalunce su, za a kwace hakkinta da na mijinta kuma ma za a doke ta har a yi mata barin cikinta. Amma Manzon Allah ya musu wasiyya da su yi hakuri.
Allah mai cika alkawari kuwa, sai ya zama ba wani abu da basu gani ba a bayan Manzon Allah (S) cikin abubuwan da ya fada musu za su riske su.
Manzon Allah (s) yana komawa ga Allah (T), a yayin da Amirulmuminin (AS) yake ta sabgogin kokarin ganin ya yi masa sutura ya bizne shi, sai ya zamana su kuma Muhajirun da Ansar daga Sahabbai sun watsar da wannan sha’anin na jana’izar Annabi, suka dankara ma kansu hada-hadar kokarin sun fitar ma da kansu Khalifan da ya dace da son ransu. Nan suka nufi wani zuren taro da ake cema ‘Sakifar Banu Sa’ida, inda kowace Kabila daga Kabilun Madina kowannensu yake raya cewa lazim su ne za su samu matsayi na su halifci Annabi (S).
Abin mamaki sosai, ta yadda za mu ga cewa kwata-kwata, bai wuce watanni biyu ba Manzon Allah (S) ya tara su a Ghadeer Khum ya halifantar da Imam Ali (AS) a matsayin halifansa a cikinsu a bayansa. Labarin Ghadeer abu ne da yake kamar hasken rana, sam bai buya ma mutanen wannan lokacin ba bare na wancan zamanin. Amma kuma yau ga Manzon nan ya koma ga Allah (T), ko bizne shi ba a yi ba, amma har sun juya ma umurninsa baya.
Dama a cikin Alkur’ani, Allah (T) yace: “Muhammadu ba kowa bane face Manzo, kuma Manzonni sun gabace shi. Shin idan ya mutu, ko kuma aka kashe shi, za ku (yi ridda) ne ku koma ga abin da diga-diginku ke kai (Jahiliyya)?” Sai kuwa mutanen nan suka ba Allah amsa a aikace da cewa Eh! Mun zabi mu watsar da abin da ya zo da shi, mu yi son ranmu. Wanda hakan shine Jahiliyya din.
Ba za ku yi mamakin juya bayansu da kin karban wasiccin Manzon Allah (S) ba a yayin da ya yi wafati, tunda a halin da yake da ransa ma, ya musu umurni da abubuwa da dama sun ki yi. Ai bai buya ma mai bibiyan nazarin nan ba inda ya zama ya inganta cewa Manzon Allah (S) ya nemi su bashi abin rubutu sun hana, har ma Umar ya fadawa Annabi bakar magana ko? Da kuma inda yace kar su bashi abu suka dura masa, har ma wata tace sai suka dura masa alhali yana hana su, suka ki.
To, wani abu da ba mu yi magana a kansa da zurfi ba a baya shine batun tura su yaki da Annabi (S) ya yi a karkashin Usamatu Dan Zaidu, da suka ki su je, suka dawo suka tsaya a kansa, ya daga kai ya gansu yace Allah ya la’anci duk wanda bai kama hanya ya tafi ba. Kuma basu je din ba.
Yana raye kenan. Ina kuma ga ace ga shi sun ga baya numfashi? Bai da halin yi musu magana? Sai su bi umurninsa a wannan lokacin? Eh haka ya kamata. Amma ba su yi hakan ba.
Insha Allah, mu tsaya a nan sai mu cigaba da labarin Saqifa kamar yadda Imam Abu Muhammad, Ibn Qutaiba al-Dinawari, wannan malamin Ahlussunah da ya rasu a shekara ta 276 bayan hijira (yau kimanin shekara 1193 da rasuwarsa) ya kawo a littafinsa Al’imama was-Siyasa.
Tsage Gaskiya (8)
Daga Saifullahi M Kabir
Kun karanta a baya cewa akwai hadisi na 3714 a cikin Sahihul Bukhari, daga Abu Walid, da sanadinsa zuwa ga Miswari Dan Makhrama yace: Manzon Allah (S) yace: “Fatima tsokar jikina ce, duk wanda ya fusata ta, ni ya fusata.” Haka ne ko? Shi fusata mutum na daga nau’in cutar da mutum din ne. To, mun ji cewa fusatawa ko cutar da Sayyida Zahra (S) cutar da Manzon Allah (S) ne. To, mene ne sakamakon masu cutar da Manzon Allah (S)?
A aya ta 56 na Suratul Ahzab, Allah (T) yana cewa: “Wadannan wadanda suke cutar da Allah da ManzonSa Allah (T) ya la’ance su a duniya da Lahira, kuma ya tanada musu azaba mai kunyatarwa.” A aya ta 61 na cikin suratul Tauba, Allah (T) yace mana: “Kuma wadanda suke cutar da Manzon Allah suna da azaba mai radadi.”
Idan haka ne, to mene ne matsayin wadannan da suka cutar da Sayyida Zahra (S) kamar yadda aka ruwaito a cikin Sahihul Bukhari hadisi na 4240 da na 4241 da na 6726, cewa har ta yi fushi da su, kuma ta kaurace masa, har ta yi wafati bata sake masa magana ba. Kuma ta rayu ne bayan wafatin babanta da watanni shida (tsawon wata shidan nan tana fushi da shi har ta koma ga Allah). Tambayar da nake yi shine mene ne hukuncinsu, duba da yadda suka cutar da tsokar Manzon Allah (S), wanda yace cutar da ita cutar da shi (S) ne, kuma Allah yace mana masu cutar da Annabi suna da azaba mai radadi. Shin mai Imani da Allah zai aminta da wanda ke da tabbacin fuskantar azabar Allah a Duniya da Lahira ya zama shine abin kallonsa a addini!? Wallahil Azeem ni ban son su. Ra’ayina a kansu shine ra’ayin Sayyida Zahra a kansu. Ina fatan ya zama har na koma ga Allah ina fushi da su nima.
Shi cutarwar da sarakunan nan sukaiwa Sayyida Zahra (S) ba wani abu ne da yake boyayye ko kuma abin da ba a tsammace shi ba. Wato ina cewa ne dama su Sayyida Zahra da mijinta da ‘ya’yanta sun san cewa za a cutar da su bayan wafatin Manzon Allah (S) kamar yadda shi Annabi (S) din ya sanar da su tun kafin ya rabu da su, har kuma ya yi musu wasicci da hakuri. Don haka dama sun san za a cutar da su, kuma sun san ko su waye za su cutar da su din. Ba kowa bane face wadannan da suka cutar da Manzon Allah (S).
Wadanda suka tsaya a gaban Annabi (S) yace su aikata suka ki aikatawa, yace kar su aikata wani abin suka aikata, suka saba masa, karshe ma suka dura masa guba suka yi sanadin Shahadarsa, yaushe kake tsammanin za su saurarawa iyalan gidansa a bayansa!? Sai aka wayi gari ba kawai Fadak suka kwacewa Sayyida Zahra (S) ba, sun kwace mulki da shugabancin zahiri na Amirulmuminin (AS) duk kuwa da sun dauki alkawarin za su bi shi a bayan Manzon Allah (S) tun a Ghadeer.
A cikin wasiyar da Manzon Allah (S) ya ma Shugaba Ali (AS), kamar yadda aka ruwaito a cikin ‘Kitabu Sulaim Bin Kais, Jildi 2, shafi 917 (Wanda al-Ansari ya yi tahkikinsa). Manzon Allah (S) ya fada ma Imam Ali (AS) cewa: “Lallai Kuraishawa za su dira a kanku, za su yi muku taron dangi su zalunceku kuma su yi maka fin karfi” (Ma’ana, za su hadu su kwace hakkokinku, su yi maka fin karfi akan mulkinka na halifancinsu na zahiri da barka a kai).
Annabi (S) yace: “ (a wannan lokacin) Idan har ka samu mataimaka, to ka yake su (Su Quraishun da za su kwace hakkin naka). Idan kuwa ba ka samu mataimaka ba to ka rike hannayenka daga gare su, ka kiyaye jininka (a wannan lokacin), amma lallai shahada na jiranka, Allah ya la’anci makashinka.”
Allah Sarki Imam Ali (AS). Sai kuwa bayan wafatin Manzon Allah (S) ya kasance abin da Manzo ya fada masa ya auku din, ta yadda suka je suka hadu a Sakifar Banu Sa’ida suka nada Halifa daban ba shi ba, suka kuma dawo suka ce tilas Ali ya yi bai’a ga wannan halifan kwacen. Har kuma suka masa barazanar za su kashe shi idan har ya ja da su. Wanda hakan ya jefa Imam a cikin matsanancin yanayi, ta yadda ya tilasta ma kansa killacewa na tsawon lokaci. Kasancewar Manzon Allah ya bashi wasiccin cewa, idan ya samu mataimaka, to ya yaki wadannan masu masa kwacen mulkin ya karbi mulkinsa. Idan kuwa bai samu ba, to ya kame hannayensa daga yakin, sannan kuma ya tsare jininsa.
Hakan tasa Imam Amirulmuminin (AS) ya nemi taimakon mutane, daga Muhajirun da Ansar a kan su zo su fada masa don ya ga yadda abin za ta kasa. Tare da cewa Sayyida Zahara (S) ta kasance tana mai taya shi wannan neman, an ruwaito cewa suna fita ita da shi da daddare su je majalisun Sahabbai daidaikunsu da sukan zauna su yi hira da daddare, sai Sayyida Zahara ta musu jawabi, tana mai tuna musu abin da Manzon Allah (S) ya yi a Ghadir Khum a gabansu, ta kuma tambaye su akan me yasa suka sauya da yi ma wanda ba shi Annabi ya halifantar ba mubayi’a? Sai su ce mata, ya ‘Yar Manzon Allah. Hakika duk abin da kika fadi gaskiya ne, amma kuma wannan mutumin ya riga dan Amminki (wato Imam Ali) fuskantomu da al’amarin mubayi’a.
Dan haka sai ya zama Imam Ali (AS) ya rasa mataimaka kwarara. An ce da kyar da wannan zagayen ya iya samun mutum 40 da suka biyo shi zuwa kofar gidansa a kan sun amsa masa kiran neman taimakonsa. To, kun san Manzon Allah (S) yace idan ya samu mataimaka ya kwaci hakkinsa, kuma adadin mataimakan nan daga 40 ne zuwa sama kawai, kamar yadda Sulaim bin Qais ya kawo cewa, Imam Ali (AS) yace: “Da ace na samu mutum 40 nagartattu kuma masu min biyayya ta gaskiya da suka goya min baya, wadanda sukai tawaye ga mai kwacen, da na kaddamar da jihadi akansu.”
Kana iya cewa ai Imam (AS) ya samu mutum 40 din yanzu. Eh, ya samu mutum 40 a ranar, amma sai yace da su yanzu duk su tafi, gobe da safe kowa ya zo cikin shiri. Wayewan gari, sai ba wanda ya zo sai kasa da mutum 5 a cikin mutum 40 din nan. Wanda ya nuna lallai dama ba a shirye suke da goya masa baya da yi masa biyayya ba.
Ta wata fuska kuma Imam ya samu mutane fiye da hakan, amma tunda ba a nagartar da yake bukata bane sai ya kore samuwar. An ce Abusufyan ya zo ma da Imam Ali (S) wata magana, inda yake ce masa: “Ya kai dan Ammin Muhammad! (Yana nufin Imam Ali (AS), ina kake? Ina Abbas!? Kuka bar wannan abin (Mulkin Muhammad) a hannun kaskantattun kabilun ‘Taim’ da ‘Addiy’? Me ya faru ne? In ka shirya ka zo zan baka mayaka mutum dubu ka yake su ka kwace hakkinka.”
Sai Imam Ali (AS) ya yi dariya, sannan yace masa, Abu Sufyan na san waye kai. Na kuma san abin da ka ke nufi. Ni ina neman ‘Mulklisai’ ne masu takawa. Kai kuwa na san me ke zuciyarka a kan wannan addinin. Don haka sai Imam (AS) ya kore tayin Abu Sufyan, domin ya fahimci shi Abu Sufyan na da burin ya yi amfani da shi ne kawai ya zama al’ummar Musulmi sun fara yake-yake har a wayi gari addinin ya rushe, tunda abin da yake da buri kenan a tsawon rayuwarsa yasa ya yi ta yakar Manzon Allah (S) a Makkah da Madina.
To mutum na iya cewa, Ah! Shi Imam Ali (AS) shi kadai ba zai iya yakarsu bane, bayan ba wanda ya ke iya yin galaba a kansa a wajen yaki? Sai muce, Manzon Allah ne ya san hikimar cewa sai ya samu mutanen da suka kai 40 da za su dafa masa. Kila mu iya cewa babu mamaki hakan na nufin saboda in abin ya karbi mulkin ne bayan ya yake su, to su waye kuma Mulkisan da za su taimaka masa wajen gudanarwa? Idan ya zama masu gudanarwar lalatattu ne masu cuta a zukatansu kun ga ai ba kanta ko?
Cikin wasiyyoyin, Manzon Allah (S) ya cigaba da fada ma Amirulmuminin (AS) dangane da abubuwan da zai same su a bayan wafatinsa, kamar yadda Sheikh Saduk ya kawo a Amalinsa, da Fara’idus Simdain na Alhamiyuni cewa: “Amma ita ‘Ya ta Fatima, wacce ta kasance itace shugaban matan talikai, a yayin da na kalle ta sai na tuna da abubuwan da za su faru da ita bayan bani nan.”
Manzon Allah (S) yaci gaba da cewa: “Kamar ina ganinta a yayin da kaskantacce zai kusa dakinta, ya keta alfarmarta, a kwace mata hakkinta, a kuma hanata gadonta, a kassara mata tayin da ke cikinta, a barar da cikinta. A wannan halin za ta kasance tana kira tana cewa; ‘Ya Muhammadaa!’ Amma ba za ta ji amsa ba. Za ta nemi dauki, amma ba za ta samu mai taimako ba. Za ta wanzu a bayana tana cikin bakin ciki da damuwa, kuma tana mai yawan kuka. Za ta kasance kamar kaskantacciya (a wajen masu cutar da ita) bayan kuwa a lokacin rayuwar mahaifinta ta kasance mai daukaka.”
Manzon Allah (S) ya ci gaba da cewa: “Za ta kasance farkon wanda za ta sadu da ni a cikin Ahlulbaiti na bayan na tafi. Za ta riske ni a cikin damuwarta kuma tana raunatacciya wacce aka bakantawa rai, wacce akawa kwacen hakkinta, kuma wacce aka kashe ta. Allah ka la’anci wanda ya zalunceta, kuma ka yi wa wanda ya fusata ta azaba, ka kaskantar da wanda ya kaskantata, kuma ka dauwamar da wanda ya barar da tayin cikinta a wutarKa.”
A ruwayar aka ce, a daidai wannan lokacin sai Mala’iku suka amsa addu’ar Manzon Allah (S) da ‘Ameen’. Ba mu gushe ba muma muna cewa Allah ka la’ance su da duk wanda ya goyi bayansu bisa sani.
Insha Allah za mu cigaba.
Kun karanta a baya cewa akwai hadisi na 3714 a cikin Sahihul Bukhari, daga Abu Walid, da sanadinsa zuwa ga Miswari Dan Makhrama yace: Manzon Allah (S) yace: “Fatima tsokar jikina ce, duk wanda ya fusata ta, ni ya fusata.” Haka ne ko? Shi fusata mutum na daga nau’in cutar da mutum din ne. To, mun ji cewa fusatawa ko cutar da Sayyida Zahra (S) cutar da Manzon Allah (S) ne. To, mene ne sakamakon masu cutar da Manzon Allah (S)?
A aya ta 56 na Suratul Ahzab, Allah (T) yana cewa: “Wadannan wadanda suke cutar da Allah da ManzonSa Allah (T) ya la’ance su a duniya da Lahira, kuma ya tanada musu azaba mai kunyatarwa.” A aya ta 61 na cikin suratul Tauba, Allah (T) yace mana: “Kuma wadanda suke cutar da Manzon Allah suna da azaba mai radadi.”
Idan haka ne, to mene ne matsayin wadannan da suka cutar da Sayyida Zahra (S) kamar yadda aka ruwaito a cikin Sahihul Bukhari hadisi na 4240 da na 4241 da na 6726, cewa har ta yi fushi da su, kuma ta kaurace masa, har ta yi wafati bata sake masa magana ba. Kuma ta rayu ne bayan wafatin babanta da watanni shida (tsawon wata shidan nan tana fushi da shi har ta koma ga Allah). Tambayar da nake yi shine mene ne hukuncinsu, duba da yadda suka cutar da tsokar Manzon Allah (S), wanda yace cutar da ita cutar da shi (S) ne, kuma Allah yace mana masu cutar da Annabi suna da azaba mai radadi. Shin mai Imani da Allah zai aminta da wanda ke da tabbacin fuskantar azabar Allah a Duniya da Lahira ya zama shine abin kallonsa a addini!? Wallahil Azeem ni ban son su. Ra’ayina a kansu shine ra’ayin Sayyida Zahra a kansu. Ina fatan ya zama har na koma ga Allah ina fushi da su nima.
Shi cutarwar da sarakunan nan sukaiwa Sayyida Zahra (S) ba wani abu ne da yake boyayye ko kuma abin da ba a tsammace shi ba. Wato ina cewa ne dama su Sayyida Zahra da mijinta da ‘ya’yanta sun san cewa za a cutar da su bayan wafatin Manzon Allah (S) kamar yadda shi Annabi (S) din ya sanar da su tun kafin ya rabu da su, har kuma ya yi musu wasicci da hakuri. Don haka dama sun san za a cutar da su, kuma sun san ko su waye za su cutar da su din. Ba kowa bane face wadannan da suka cutar da Manzon Allah (S).
Wadanda suka tsaya a gaban Annabi (S) yace su aikata suka ki aikatawa, yace kar su aikata wani abin suka aikata, suka saba masa, karshe ma suka dura masa guba suka yi sanadin Shahadarsa, yaushe kake tsammanin za su saurarawa iyalan gidansa a bayansa!? Sai aka wayi gari ba kawai Fadak suka kwacewa Sayyida Zahra (S) ba, sun kwace mulki da shugabancin zahiri na Amirulmuminin (AS) duk kuwa da sun dauki alkawarin za su bi shi a bayan Manzon Allah (S) tun a Ghadeer.
A cikin wasiyar da Manzon Allah (S) ya ma Shugaba Ali (AS), kamar yadda aka ruwaito a cikin ‘Kitabu Sulaim Bin Kais, Jildi 2, shafi 917 (Wanda al-Ansari ya yi tahkikinsa). Manzon Allah (S) ya fada ma Imam Ali (AS) cewa: “Lallai Kuraishawa za su dira a kanku, za su yi muku taron dangi su zalunceku kuma su yi maka fin karfi” (Ma’ana, za su hadu su kwace hakkokinku, su yi maka fin karfi akan mulkinka na halifancinsu na zahiri da barka a kai).
Annabi (S) yace: “ (a wannan lokacin) Idan har ka samu mataimaka, to ka yake su (Su Quraishun da za su kwace hakkin naka). Idan kuwa ba ka samu mataimaka ba to ka rike hannayenka daga gare su, ka kiyaye jininka (a wannan lokacin), amma lallai shahada na jiranka, Allah ya la’anci makashinka.”
Allah Sarki Imam Ali (AS). Sai kuwa bayan wafatin Manzon Allah (S) ya kasance abin da Manzo ya fada masa ya auku din, ta yadda suka je suka hadu a Sakifar Banu Sa’ida suka nada Halifa daban ba shi ba, suka kuma dawo suka ce tilas Ali ya yi bai’a ga wannan halifan kwacen. Har kuma suka masa barazanar za su kashe shi idan har ya ja da su. Wanda hakan ya jefa Imam a cikin matsanancin yanayi, ta yadda ya tilasta ma kansa killacewa na tsawon lokaci. Kasancewar Manzon Allah ya bashi wasiccin cewa, idan ya samu mataimaka, to ya yaki wadannan masu masa kwacen mulkin ya karbi mulkinsa. Idan kuwa bai samu ba, to ya kame hannayensa daga yakin, sannan kuma ya tsare jininsa.
Hakan tasa Imam Amirulmuminin (AS) ya nemi taimakon mutane, daga Muhajirun da Ansar a kan su zo su fada masa don ya ga yadda abin za ta kasa. Tare da cewa Sayyida Zahara (S) ta kasance tana mai taya shi wannan neman, an ruwaito cewa suna fita ita da shi da daddare su je majalisun Sahabbai daidaikunsu da sukan zauna su yi hira da daddare, sai Sayyida Zahara ta musu jawabi, tana mai tuna musu abin da Manzon Allah (S) ya yi a Ghadir Khum a gabansu, ta kuma tambaye su akan me yasa suka sauya da yi ma wanda ba shi Annabi ya halifantar ba mubayi’a? Sai su ce mata, ya ‘Yar Manzon Allah. Hakika duk abin da kika fadi gaskiya ne, amma kuma wannan mutumin ya riga dan Amminki (wato Imam Ali) fuskantomu da al’amarin mubayi’a.
Dan haka sai ya zama Imam Ali (AS) ya rasa mataimaka kwarara. An ce da kyar da wannan zagayen ya iya samun mutum 40 da suka biyo shi zuwa kofar gidansa a kan sun amsa masa kiran neman taimakonsa. To, kun san Manzon Allah (S) yace idan ya samu mataimaka ya kwaci hakkinsa, kuma adadin mataimakan nan daga 40 ne zuwa sama kawai, kamar yadda Sulaim bin Qais ya kawo cewa, Imam Ali (AS) yace: “Da ace na samu mutum 40 nagartattu kuma masu min biyayya ta gaskiya da suka goya min baya, wadanda sukai tawaye ga mai kwacen, da na kaddamar da jihadi akansu.”
Kana iya cewa ai Imam (AS) ya samu mutum 40 din yanzu. Eh, ya samu mutum 40 a ranar, amma sai yace da su yanzu duk su tafi, gobe da safe kowa ya zo cikin shiri. Wayewan gari, sai ba wanda ya zo sai kasa da mutum 5 a cikin mutum 40 din nan. Wanda ya nuna lallai dama ba a shirye suke da goya masa baya da yi masa biyayya ba.
Ta wata fuska kuma Imam ya samu mutane fiye da hakan, amma tunda ba a nagartar da yake bukata bane sai ya kore samuwar. An ce Abusufyan ya zo ma da Imam Ali (S) wata magana, inda yake ce masa: “Ya kai dan Ammin Muhammad! (Yana nufin Imam Ali (AS), ina kake? Ina Abbas!? Kuka bar wannan abin (Mulkin Muhammad) a hannun kaskantattun kabilun ‘Taim’ da ‘Addiy’? Me ya faru ne? In ka shirya ka zo zan baka mayaka mutum dubu ka yake su ka kwace hakkinka.”
Sai Imam Ali (AS) ya yi dariya, sannan yace masa, Abu Sufyan na san waye kai. Na kuma san abin da ka ke nufi. Ni ina neman ‘Mulklisai’ ne masu takawa. Kai kuwa na san me ke zuciyarka a kan wannan addinin. Don haka sai Imam (AS) ya kore tayin Abu Sufyan, domin ya fahimci shi Abu Sufyan na da burin ya yi amfani da shi ne kawai ya zama al’ummar Musulmi sun fara yake-yake har a wayi gari addinin ya rushe, tunda abin da yake da buri kenan a tsawon rayuwarsa yasa ya yi ta yakar Manzon Allah (S) a Makkah da Madina.
To mutum na iya cewa, Ah! Shi Imam Ali (AS) shi kadai ba zai iya yakarsu bane, bayan ba wanda ya ke iya yin galaba a kansa a wajen yaki? Sai muce, Manzon Allah ne ya san hikimar cewa sai ya samu mutanen da suka kai 40 da za su dafa masa. Kila mu iya cewa babu mamaki hakan na nufin saboda in abin ya karbi mulkin ne bayan ya yake su, to su waye kuma Mulkisan da za su taimaka masa wajen gudanarwa? Idan ya zama masu gudanarwar lalatattu ne masu cuta a zukatansu kun ga ai ba kanta ko?
Cikin wasiyyoyin, Manzon Allah (S) ya cigaba da fada ma Amirulmuminin (AS) dangane da abubuwan da zai same su a bayan wafatinsa, kamar yadda Sheikh Saduk ya kawo a Amalinsa, da Fara’idus Simdain na Alhamiyuni cewa: “Amma ita ‘Ya ta Fatima, wacce ta kasance itace shugaban matan talikai, a yayin da na kalle ta sai na tuna da abubuwan da za su faru da ita bayan bani nan.”
Manzon Allah (S) yaci gaba da cewa: “Kamar ina ganinta a yayin da kaskantacce zai kusa dakinta, ya keta alfarmarta, a kwace mata hakkinta, a kuma hanata gadonta, a kassara mata tayin da ke cikinta, a barar da cikinta. A wannan halin za ta kasance tana kira tana cewa; ‘Ya Muhammadaa!’ Amma ba za ta ji amsa ba. Za ta nemi dauki, amma ba za ta samu mai taimako ba. Za ta wanzu a bayana tana cikin bakin ciki da damuwa, kuma tana mai yawan kuka. Za ta kasance kamar kaskantacciya (a wajen masu cutar da ita) bayan kuwa a lokacin rayuwar mahaifinta ta kasance mai daukaka.”
Manzon Allah (S) ya ci gaba da cewa: “Za ta kasance farkon wanda za ta sadu da ni a cikin Ahlulbaiti na bayan na tafi. Za ta riske ni a cikin damuwarta kuma tana raunatacciya wacce aka bakantawa rai, wacce akawa kwacen hakkinta, kuma wacce aka kashe ta. Allah ka la’anci wanda ya zalunceta, kuma ka yi wa wanda ya fusata ta azaba, ka kaskantar da wanda ya kaskantata, kuma ka dauwamar da wanda ya barar da tayin cikinta a wutarKa.”
A ruwayar aka ce, a daidai wannan lokacin sai Mala’iku suka amsa addu’ar Manzon Allah (S) da ‘Ameen’. Ba mu gushe ba muma muna cewa Allah ka la’ance su da duk wanda ya goyi bayansu bisa sani.
Insha Allah za mu cigaba.
Tsage Gaskiya (7)
Daga Saifullahi M Kabir
Rubutun tsage gaskiya da na faro tun kafin ranar Shahadar Annabi (S), sakamakon yanayoyi sai ya zama ya tsaya kusan wata biyu ban cigaba ba. In ba ku manta ba rubutun ya tsaya ne a kashi na 6, wanda na yi shi a farkon Rabi’ul Auwal, na fara da magana a kan hijirar Manzon Allah (S) da batun ‘Sahibin Annabi’ a kogo yayin hijirar, ko da yake mun yi magana ne sama-sama, sai kuma muka kawo batun yadda karfi da yaji aka kafirta iyayen Annabi (S) ake nuna su a matsayin kafirai kuma mushirikai alhali ba su kasance ba face muminai na gargaru kuma amintattu. To har nace za mu yi magana a kan haihuwar Manzon Allah (S) da yadda aka jirkita labarrurrukan haihuwar don a rage matsayin Annabin (s), sai kuma ya zama har lokacin ya wuce ba mu yi ba. Ina neman afuwan masu bibiyar nazarin.
Yau muna 1 ga Jimadal Ula ne, a cikin irin wannan watan ne ake tunawa tare da gudanar da juyayin shahadar tsokar jikin Manzon Allah (S), Sayyida Fatima (SA).
Da yake an samu ruwayoyi daban-daban a kan hakikanin kwanakin da ke tsakanin Shahadar Manzon Allah (S) wanda ya kasance a ranar 28 ga Safar 11bh, da Shahadar ‘Yarsa Sayyida Zahra (S). Mafi karancin kwanaki shine kwana 40, a yayin da akwai ruwayar da ta nuna cewa tsakaninsu watanni 6 ne (wannan shi ya fi shahara a wajen Ahlussunnah). Sai dai ruwayar da tafi inganci shine cewa Sayyida ta kara kwanaki 75 ko kuma kwanaki 95 bayan wafatin mahaifinta (S). Idan mun dauka kwanaki 75 din ne, shine zai kama ranar 13 ga watan Jimadal Ula. Ko da yake shima a kan yi kokari wajen raya munasabar ya zama an yi kwanaki uku ne a jere, 13, 14 da 15 ga Jimadal Ula din, kila don ya zama an dace da hakikanin kwanaki 75 din daga ranar 28 ga Safar din.
Ba tattauna ranar ne babban muhimmin abu ba a yanzu, tattauna abin da ranar ke kunshe da shi ne muhimmi. Ko da yake wasu suna da ra’ayin cewa ba su san amfanin tattauna abin da ya riga ya faru kuma ma ya wuce ba a yanzu. Har ma wasu kan bada wasu misalai da sam basu dacewa da inda ake aje su, dangane da cutarwar da sarakuna suka yi ma iyalan Manzon Allah (S) a bayan wafatin Annabi (S) din, wasu za ka ji suna cewa; Fada ne da ya faru tsakanin manya guda biyu, kai ina ruwanka!? Har ma su ce; Yanzu idan Babanka da Mamarka suna fada wa za ka tarewa? Wani ya taba fada min hakan, nace masa mai gaskiya zan tare wa mana.
Wai a cewarsu manya guda biyu sune Sahabban da suka yi sarautan Musulmi a bayan wafatin Annabi (S) bisa nadin kansu ga kansu, da kuma tsarkakakkun iyalan gidan Manzon Allah (S) wadannan da Allah (T) ya wajabtawa Sahabbai da duk masu Imani sonsu da bin su da girmama su, ya kuma tsarkake su tsarkakewa. Da wadannan Sahabban suka kwace mulkin al’ummar Annabi (S) daga gidan Annabi (S) suka dankarawa kansu, suka kuma cutar da iyalan Annabi (S) din, cutarwar da tarihi ya kasa boye birbishinsa ta kowane siga. Sai aka zo aka ce, eh an yarda an samu sabani tsakanin Sahabbai da Iyalan Annabi (S), amma ai to misalinsu kama misalin uwa da uba ne gare mu. Don haka tunda haka ne, kai naka kawai kallo, fadan mahaifa. Tambaya; Idan mahaifanka suka saba, kai ba za ka iya sanin wa ke da gaskiya wa ke da laifi ba? Ko ka gane sai ka rufe ido kawai kace su ta shafa? Ba wata hayar daza ka bi wajen gayawa mare gaskiya rashin gaskiyarsa ko ya gyara!?
Ballantana ba ma haka misalin yake ba. Tsakanin Sahabbai da Iyalan Annabi (S), kamar Uwa ne da ‘ya’yanta! Ahlulbait (AS) sune iyaye, sahabbai su ‘ya’yaye ne! Ai a cikin Alkur’ani ne Allah (T) yacewa Manzon Allah (S); “Kace musu bani bukatar wani lada daga gare ku, face soyayya ga makusanta na.” ko? Su wa Manzon Allah (S) zai fadawa hakan? Kace min Sahabbai. Su waye makusantan Manzon Allah (S)? Iyalan gidansa tsarkakan nan da Allah (T) yace ya tsarkake su tsarkakewa. Akwai makusanciyar da ta kai Sayyida Fatima (SA) kusanci da Manzon Allah (S)? Babu. Yauwa, to Sayyadina Abubakar ba Sahabi bane? Ba yana cikin wadanda Allah yasa Manzon Allah (s) ya fada musu cewa su so iyalan Annabin ba? Tambaya! Da ya inganta cewa Sayyida Zahra (S) ta koma ga Allah (T) tana mai fushi da shi, tana mai cewa sai ta kai karansa gaban Manzon Allah (S) a gaban zatin Allah (T) ranar Alkiyama, shin tsabar soyayyar da yake mata ne yasa ta fadi hakan?
Kar kace min ba a yi hakan ba, ai na yi magana a kan hakan a kashi na 3 na wannan nazarin (Tsage Gaskiya 3) ko? Har da bayanin yadda Sayyida Zahra (S) ta ma mijinta wasicci a kan ya bizne ta da daddare, kar ya bari Abubakar ko Umar su sallaci gawanta. Kuma haka aka yi ba su sallatan ba. Malam, soyayyarsu ga Sayyida Zahra (S) yasa ta yi wasicci a kan hakan? Ita wajibi ne su so ta. Shin a ina Allah (T) ya wajabta ita ta so su? Kai ma ba inda aka ce ka bi su balle ita tsokar jikin Manzon Allah (S).
Misalin Sayyida Zahra (SA) a kan dukkan sahabbai kamar uwa ce da ‘ya’yanta. Wanda duk ya bi ta ya yi zaman lafiya da ita, ya rabauta da bin mahaifiyarsa, wanda kuwa duk ya saba da ita har ta yi fushi da shi to yana cikin fushin Allah. Kai wallahi gumma uwar da ta haife ka ta yi fushi da kai a kan Sayyida Zahra (S) ta je wajen Allah (T) tana fushi da kai. Ko ba komai, uwarka na iya fushi da kai a kan son ranta. Amma ita Sayyida Fatima (S) ta samu sheda daga Allah (T) a kan cewa ba za ta taba yin fushi ba face da fushin Allah (T). Kamar dai yadda Mahaifinta yake, fusata shi fusata Allah (T) ne. A baya mun kawo hadisi na 3714 a cikin Sahihul Bukhari, inda aka ruwaito Manzon Allah (S) yana cewa: “Fatima tsokar jikina ce, duk wanda ya fusata ta, ni ya fusata.”
Ga duk wanda bai sani ba ma, idan har ya karanta rubutun nan kashi na 3, ya kuma koma cikin Sahihul Bukhari ya ga hadisan nan da na kawo, sam ba zai min musu a kan cewa sarakuna sun fusata Sayyida Fatima (SA) ba, har ta musu kaura, ta bar kula su har ta koma ga Allah. Ko da yake a kan ce wai saboda sun hana ta gado ne, wanda yake gaskiya ba kawai wannan bane. Shi Fadak dama ba gado bane mallakin Sayyida Zahra (S) ne. Manzon Allah (s) ya bata shi tun yana raye. Sai dai gadon ma sun rike, don haka sai suka yi amfani da hakan suka mai da Fadak ma gado, suka ce kuma ba a cin gadon Annabawa, wai abin da suka bari sadaka ne. Kun ga tunda kuma an haramta cin sadaka ga Annabi da Ahlulbait (AS), shikenan su Sayyida Zahra (S) su zauna a talauce kenan. Wannan ne babban burin masu rike hakkin Ahlulbait (AS).
Amma gaskiyar magana shine cutarwar da tasa Sayyida Zahra (S) ta yi fushi kuma ta furta bara’arta ga sarakunan nan ba kawai saboda sun hana ta Fadak ko wani gadonta bane. A’a cutarwa ce da ta yi sanadiyyar rasa rayuwarta gaba daya ma sakamakon aikinsu.
Da sannu za mu nazarci irin cutarwar da sarakunan Musulmi suka yi ga Sayyida Zahra (S) da mijinta Ali (AS) da ‘ya’yanta (AS) a bayan wafatin Manzon Allah (S) daga littafan Sunnah ba tare da waiwayan na Shi’a ba! Nan za mu ga shin sun nuna soyayya ne ga makusantan Annabi (S) a bayan Annabin ko kuwa kiyayya da gaba da hujumi suka rika zuwa musu da shi.
Daga cikin amfanin tuna irin wadannan har da cewa mutum ya san su wa yake bi a matsayin shugabanninsa. Kar a je Lahira ya ga an yi wuta da wasu kuma shi ya dauke su a matsayin jagororin shiriya ne, ya zo yana tuhuma a kan me yasa suka jagorance shi suna cewa ba su ce ya bi su ba ai. Domin gaskiyar magana shine tunda ya inganta cewa fushin Sayyida Fatima (S) fushin Annabi ne, kuma fushin Allah ne. kuma ya inganta cewa akwai wasu mutane da Sayyida ta koma ga Allah tana fushi da su, tana mai wasiyya a kan kar ma a bari su ga gawarta, kuma sai ta kai su kara wajen Allah, to wallahil azeem mutanen nan ba zai yiwu Allah ya musu makoma daya da Sayyida Zahra (S) ba! Kuma dai a Lahira in ba wuta ba Aljanna ko? Kuma Allah ba zai saka tsokar Annabi, wacce take fushi da fushinsa take yarda da yarsar sa a inda ba Aljanna ba. Ba kuma zai saka wadanda suka cutar da ita har ta yi shelar cewa ta yi fushi da su a Aljanna ba.
A ranar Lahira, wadannan sahabban da za a kada su wuta kamar yadda na kawo ruwayoyin a kashi na 5 na wanna rubutun daga Annabi (S), na gaba a cikinsu su ne wadanda suka cutar da Sayyida Zahra (S) har ta koma ga Allah tana fushi da su. Wallahi babu wani da ya canza wasiccin Annabi (addininsa) fiye da su. Tabbas Mu’awiyya da Yazidu sun bi tafarkinsu ne a aiki! Da ace su ne suka zo a zamanin su Mu’awiyya abin da za su yi kenan, domin wanda ya kashe Hasan da wanda ya kashe Husain (AS) ba zai fi zunubi a kan wanda ya fusata Fatima har ma ya kashe ta ba.
Za mu cigaba insha Allah.
Rubutun tsage gaskiya da na faro tun kafin ranar Shahadar Annabi (S), sakamakon yanayoyi sai ya zama ya tsaya kusan wata biyu ban cigaba ba. In ba ku manta ba rubutun ya tsaya ne a kashi na 6, wanda na yi shi a farkon Rabi’ul Auwal, na fara da magana a kan hijirar Manzon Allah (S) da batun ‘Sahibin Annabi’ a kogo yayin hijirar, ko da yake mun yi magana ne sama-sama, sai kuma muka kawo batun yadda karfi da yaji aka kafirta iyayen Annabi (S) ake nuna su a matsayin kafirai kuma mushirikai alhali ba su kasance ba face muminai na gargaru kuma amintattu. To har nace za mu yi magana a kan haihuwar Manzon Allah (S) da yadda aka jirkita labarrurrukan haihuwar don a rage matsayin Annabin (s), sai kuma ya zama har lokacin ya wuce ba mu yi ba. Ina neman afuwan masu bibiyar nazarin.
Yau muna 1 ga Jimadal Ula ne, a cikin irin wannan watan ne ake tunawa tare da gudanar da juyayin shahadar tsokar jikin Manzon Allah (S), Sayyida Fatima (SA).
Da yake an samu ruwayoyi daban-daban a kan hakikanin kwanakin da ke tsakanin Shahadar Manzon Allah (S) wanda ya kasance a ranar 28 ga Safar 11bh, da Shahadar ‘Yarsa Sayyida Zahra (S). Mafi karancin kwanaki shine kwana 40, a yayin da akwai ruwayar da ta nuna cewa tsakaninsu watanni 6 ne (wannan shi ya fi shahara a wajen Ahlussunnah). Sai dai ruwayar da tafi inganci shine cewa Sayyida ta kara kwanaki 75 ko kuma kwanaki 95 bayan wafatin mahaifinta (S). Idan mun dauka kwanaki 75 din ne, shine zai kama ranar 13 ga watan Jimadal Ula. Ko da yake shima a kan yi kokari wajen raya munasabar ya zama an yi kwanaki uku ne a jere, 13, 14 da 15 ga Jimadal Ula din, kila don ya zama an dace da hakikanin kwanaki 75 din daga ranar 28 ga Safar din.
Ba tattauna ranar ne babban muhimmin abu ba a yanzu, tattauna abin da ranar ke kunshe da shi ne muhimmi. Ko da yake wasu suna da ra’ayin cewa ba su san amfanin tattauna abin da ya riga ya faru kuma ma ya wuce ba a yanzu. Har ma wasu kan bada wasu misalai da sam basu dacewa da inda ake aje su, dangane da cutarwar da sarakuna suka yi ma iyalan Manzon Allah (S) a bayan wafatin Annabi (S) din, wasu za ka ji suna cewa; Fada ne da ya faru tsakanin manya guda biyu, kai ina ruwanka!? Har ma su ce; Yanzu idan Babanka da Mamarka suna fada wa za ka tarewa? Wani ya taba fada min hakan, nace masa mai gaskiya zan tare wa mana.
Wai a cewarsu manya guda biyu sune Sahabban da suka yi sarautan Musulmi a bayan wafatin Annabi (S) bisa nadin kansu ga kansu, da kuma tsarkakakkun iyalan gidan Manzon Allah (S) wadannan da Allah (T) ya wajabtawa Sahabbai da duk masu Imani sonsu da bin su da girmama su, ya kuma tsarkake su tsarkakewa. Da wadannan Sahabban suka kwace mulkin al’ummar Annabi (S) daga gidan Annabi (S) suka dankarawa kansu, suka kuma cutar da iyalan Annabi (S) din, cutarwar da tarihi ya kasa boye birbishinsa ta kowane siga. Sai aka zo aka ce, eh an yarda an samu sabani tsakanin Sahabbai da Iyalan Annabi (S), amma ai to misalinsu kama misalin uwa da uba ne gare mu. Don haka tunda haka ne, kai naka kawai kallo, fadan mahaifa. Tambaya; Idan mahaifanka suka saba, kai ba za ka iya sanin wa ke da gaskiya wa ke da laifi ba? Ko ka gane sai ka rufe ido kawai kace su ta shafa? Ba wata hayar daza ka bi wajen gayawa mare gaskiya rashin gaskiyarsa ko ya gyara!?
Ballantana ba ma haka misalin yake ba. Tsakanin Sahabbai da Iyalan Annabi (S), kamar Uwa ne da ‘ya’yanta! Ahlulbait (AS) sune iyaye, sahabbai su ‘ya’yaye ne! Ai a cikin Alkur’ani ne Allah (T) yacewa Manzon Allah (S); “Kace musu bani bukatar wani lada daga gare ku, face soyayya ga makusanta na.” ko? Su wa Manzon Allah (S) zai fadawa hakan? Kace min Sahabbai. Su waye makusantan Manzon Allah (S)? Iyalan gidansa tsarkakan nan da Allah (T) yace ya tsarkake su tsarkakewa. Akwai makusanciyar da ta kai Sayyida Fatima (SA) kusanci da Manzon Allah (S)? Babu. Yauwa, to Sayyadina Abubakar ba Sahabi bane? Ba yana cikin wadanda Allah yasa Manzon Allah (s) ya fada musu cewa su so iyalan Annabin ba? Tambaya! Da ya inganta cewa Sayyida Zahra (S) ta koma ga Allah (T) tana mai fushi da shi, tana mai cewa sai ta kai karansa gaban Manzon Allah (S) a gaban zatin Allah (T) ranar Alkiyama, shin tsabar soyayyar da yake mata ne yasa ta fadi hakan?
Kar kace min ba a yi hakan ba, ai na yi magana a kan hakan a kashi na 3 na wannan nazarin (Tsage Gaskiya 3) ko? Har da bayanin yadda Sayyida Zahra (S) ta ma mijinta wasicci a kan ya bizne ta da daddare, kar ya bari Abubakar ko Umar su sallaci gawanta. Kuma haka aka yi ba su sallatan ba. Malam, soyayyarsu ga Sayyida Zahra (S) yasa ta yi wasicci a kan hakan? Ita wajibi ne su so ta. Shin a ina Allah (T) ya wajabta ita ta so su? Kai ma ba inda aka ce ka bi su balle ita tsokar jikin Manzon Allah (S).
Misalin Sayyida Zahra (SA) a kan dukkan sahabbai kamar uwa ce da ‘ya’yanta. Wanda duk ya bi ta ya yi zaman lafiya da ita, ya rabauta da bin mahaifiyarsa, wanda kuwa duk ya saba da ita har ta yi fushi da shi to yana cikin fushin Allah. Kai wallahi gumma uwar da ta haife ka ta yi fushi da kai a kan Sayyida Zahra (S) ta je wajen Allah (T) tana fushi da kai. Ko ba komai, uwarka na iya fushi da kai a kan son ranta. Amma ita Sayyida Fatima (S) ta samu sheda daga Allah (T) a kan cewa ba za ta taba yin fushi ba face da fushin Allah (T). Kamar dai yadda Mahaifinta yake, fusata shi fusata Allah (T) ne. A baya mun kawo hadisi na 3714 a cikin Sahihul Bukhari, inda aka ruwaito Manzon Allah (S) yana cewa: “Fatima tsokar jikina ce, duk wanda ya fusata ta, ni ya fusata.”
Ga duk wanda bai sani ba ma, idan har ya karanta rubutun nan kashi na 3, ya kuma koma cikin Sahihul Bukhari ya ga hadisan nan da na kawo, sam ba zai min musu a kan cewa sarakuna sun fusata Sayyida Fatima (SA) ba, har ta musu kaura, ta bar kula su har ta koma ga Allah. Ko da yake a kan ce wai saboda sun hana ta gado ne, wanda yake gaskiya ba kawai wannan bane. Shi Fadak dama ba gado bane mallakin Sayyida Zahra (S) ne. Manzon Allah (s) ya bata shi tun yana raye. Sai dai gadon ma sun rike, don haka sai suka yi amfani da hakan suka mai da Fadak ma gado, suka ce kuma ba a cin gadon Annabawa, wai abin da suka bari sadaka ne. Kun ga tunda kuma an haramta cin sadaka ga Annabi da Ahlulbait (AS), shikenan su Sayyida Zahra (S) su zauna a talauce kenan. Wannan ne babban burin masu rike hakkin Ahlulbait (AS).
Amma gaskiyar magana shine cutarwar da tasa Sayyida Zahra (S) ta yi fushi kuma ta furta bara’arta ga sarakunan nan ba kawai saboda sun hana ta Fadak ko wani gadonta bane. A’a cutarwa ce da ta yi sanadiyyar rasa rayuwarta gaba daya ma sakamakon aikinsu.
Da sannu za mu nazarci irin cutarwar da sarakunan Musulmi suka yi ga Sayyida Zahra (S) da mijinta Ali (AS) da ‘ya’yanta (AS) a bayan wafatin Manzon Allah (S) daga littafan Sunnah ba tare da waiwayan na Shi’a ba! Nan za mu ga shin sun nuna soyayya ne ga makusantan Annabi (S) a bayan Annabin ko kuwa kiyayya da gaba da hujumi suka rika zuwa musu da shi.
Daga cikin amfanin tuna irin wadannan har da cewa mutum ya san su wa yake bi a matsayin shugabanninsa. Kar a je Lahira ya ga an yi wuta da wasu kuma shi ya dauke su a matsayin jagororin shiriya ne, ya zo yana tuhuma a kan me yasa suka jagorance shi suna cewa ba su ce ya bi su ba ai. Domin gaskiyar magana shine tunda ya inganta cewa fushin Sayyida Fatima (S) fushin Annabi ne, kuma fushin Allah ne. kuma ya inganta cewa akwai wasu mutane da Sayyida ta koma ga Allah tana fushi da su, tana mai wasiyya a kan kar ma a bari su ga gawarta, kuma sai ta kai su kara wajen Allah, to wallahil azeem mutanen nan ba zai yiwu Allah ya musu makoma daya da Sayyida Zahra (S) ba! Kuma dai a Lahira in ba wuta ba Aljanna ko? Kuma Allah ba zai saka tsokar Annabi, wacce take fushi da fushinsa take yarda da yarsar sa a inda ba Aljanna ba. Ba kuma zai saka wadanda suka cutar da ita har ta yi shelar cewa ta yi fushi da su a Aljanna ba.
A ranar Lahira, wadannan sahabban da za a kada su wuta kamar yadda na kawo ruwayoyin a kashi na 5 na wanna rubutun daga Annabi (S), na gaba a cikinsu su ne wadanda suka cutar da Sayyida Zahra (S) har ta koma ga Allah tana fushi da su. Wallahi babu wani da ya canza wasiccin Annabi (addininsa) fiye da su. Tabbas Mu’awiyya da Yazidu sun bi tafarkinsu ne a aiki! Da ace su ne suka zo a zamanin su Mu’awiyya abin da za su yi kenan, domin wanda ya kashe Hasan da wanda ya kashe Husain (AS) ba zai fi zunubi a kan wanda ya fusata Fatima har ma ya kashe ta ba.
Za mu cigaba insha Allah.
Tsage Gaskiya (6)
Daga Saifullahi M Kabir
Cigaban wannan nazarin zai sauya fasali kadan, kasancewar mun shigo watan da aka haifi fiyayyen halitta, Masoyinmu abin kaunarmu, Muhammad Dan Aminatu da Abdullahi (S). Ko da yake a watan akwai abubuwan da ya kamata ace mun waiwaye su mu ga abubuwa a hakikarsu, musamman abin da ya shafi batun Hijirar Annabi (S) daga Makkah zuwa Madina, wanda ya kasance fitan Annabi (S) daga Makka ya faru ne a ranar 1 ga Rabi’ul Auwal, shekara ta 13 bayan aike.
Wannan hijirar ce ta kasance silan kafa daular addinin Musulunci a garin Madina, daular da ta fadada har sai da ta mamaye duniya baki daya.
To, darussan da ke kunshe a cikin wannan Hijirar abubuwa ne da ya kamata ya zama mun yi nazarinsu, tun kama daga dalilin yin hijirar, da kwanciyar Shugaban Muminai a shimfidar Manzon Allah (S) a daren Hijira, da fitan Annabi (S) inda har ya samu dan rakiya masanin hanya, wanda ya amince zai raka Annabi (S) har garin Madina, amma da suka shiga cikin kogo suka ji alamun Kafirai za su gano inda suka buya, sai shi wannan dan rakiyan ya fara damuwa yana bakin ciki, akan me yasa ya yarda ya raka Annabi (S) alhali ana kama su kashe su za a yi?
Shine kamar yadda Allah (T) yake bamu labari a Alkur’ani, sai Manzon Allah (S) yace ma wannan dan rakiyar nasa; “Kar ka yi bakin ciki, Allah yana tare da mu.” Wato ka bar damuwa ba wani abu da zai same mu, Allah zai kiyaye mu. Wani yana iya cewa, ai Allah (T) yace masa ‘Sahibihi’, wato ‘Sahibinsa’ ne, wanda yake nufin yabo ne na musamman ga wannan dan rakiyar. Sai muce masa ai Allah (T) yace ma Annabi (S) Sahibin Mushirikai ma. Baka ji ba, a yayin da suka cewa Annabi (S) mahaukaci, sai Allah (T) yace musu: “Sahibinku (yana nufin Annabi) ba mahaukaci bane.” Ko a wani wajen yace; “Sahibinku ba batacce bane”? Don haka koma wane ne wannan dan rakiyar, wanda mai bai inganta cewa wanda ake cewa bane, ba ana nufin an yabe shi bane.
Wannan wani bahasi ne da zai zo nan gaba musamman da ruwayoyi insha Allah, ta yadda za mu fahimci karfi da yaji an yi kokarin kange matsayin Imam Ali (AS) ne na fansar rayuwar Manzon Allah (S) yana me neman yardar Allah da ya yi a daren hijira, a yayin da ya kwanta a shimfidar Annabin da Mushirikai sukai gangamin kashewa.
Kun san jarumtar Ali (AS) irin na Annabi (S), irin kuma na ‘ya’yan Hashim ne. Kila bamu sani ba, ko mun manta cewa Allah (T) bai halicci wasu mutane da suka kai Banu Hashim jarumta ba. Ya zo a cikin littafin Al-Irshad cewa; A yakin Hunaini, bayan da Sahabbai suka gudu suka bar Annabi (S), sai ya kasance daga shi sai mutum goma. To, mutum tara daga cikin goman nan dukkansu Banu Hashim ne. mutum na goma shine Aiman (dan gidan Ummu Aiman (RA)). Da aka kashe Aiman sai ya kasance saura mutum tara dukkansu Hashimawa ne tare da Manzon Allah (S).
Hashim shine kakan Manzon Allah (S) na biyu. Kamar yadda muka sani, mahaifin Annabinmu Tsarkakakke dan Tsarkaka shine Shugabanmu Abdullahi Dan Abdulmudallib dan Hashim (AS). Wadannan tsarkakan bayin da suka kasance masu sujuda a tsawon kasancewarsu. Allah (T) ya zabe su, ya fifita su a kan dukkan talikai, kuma ya sanya su masu Imani, masu sujuda, ya rika jujjuyawa da tsatson Annabinsa Muhammad (S) ta cikinsu tun daga Adamu (AS) har zuwa kan na karshensu Abdulmudallib (AS).
A cikin Khisal, daga Manzon Allah (S) yake cewa: “Allah Mai girma da daukaka ya kasa mutanen kasa zuwa gida biyu; sai ya sanya ni a kashin da ya fi alkairi. Sannan sai ya kasa wannan rabin (mafi alkairin) gida uku, sai na kasance fiyayyen kaso ukun. Sai Allah (T) ya zabi Larabawa daga cikin dukkan mutane, ya kuma zabi Kuraishawa daga dukkan Larabawa, sannan ya zabi Banu Hashim daga dukkan Kuraishawa, sannan ya kuma zaban Banu Abdulmudallib daga cikin Banu Hashim, sai Allah (T) ya zabe ni daga cikin dukkan Banu Abdulmudallib.”
A wajenmu, dangin Manzon Allah (S) sune mafiya kyawu da tsarkakan dangi. Mu mabiya Annabi Muhammad (S) mun yi Imani da cewa iyayensa tun daga kan Abdullahi har zuwa kan Annabi Isma’il zuwa Annabi Adam (AS) dukkansu Musulmai ne, masu Imani da Allah (T). Ba’a taba samun Mushiriki a tsatson Annabi (S). Wasu ruwayoyi da wasu suka kawo a cikin littafansu cewa wai wani ya tambayi Annabi cewa ina babansa yake? Sai Annabi wai yace wai da babanka da babana duk suna wuta (Wal iyazu billah) duk karyar banza da hofi ce. Kirkirarrun labarai ne don a kushe darajar Manzon Allah (S).
Yaushe Allah zai shaida mana cewa ya jujjuya Annabi a tsatson masu sujjada kuma ya zama an samu Mushiriki a cikin iyayensa? Ballantana kuma babu wani da ya isa ya kawo maka cewa an taba samun wani daga iyayen Manzon Allah (S) da a tarihi aka ganshi ya ma gunki sujada. Larabawa suna bautar gumaka ne kafin Musulunci, amma ko a lokacin su gidan iyaye da kakannin Annabinmu (S) ba su taba bautawa gunkin ba. Don haka ne ma Annabi (S) ya iya tasowa a hannunsu tsawon shekaru 40 kafin ai masa wahayi bai taba bautar gunki ba.
Abin da ya inganta shine iyayen Manzon Allah (S) sun kasance ne mabiya addinin Annabi Ibrahim (AS), wanda su ne suka kasance halifofi kuma wasiyan karshe na Annabi Ibraheem (AS) kafin bayyanar Annabi Muhammad (S).
Malam, ka kaddara cewa dukkansu Mushirikai ne, saboda a lokacin da suka rasu ba a aiko musu da Manzo ba, ba su samu mai kira ba, balle ya kira su su bi Allah. Sai suka mutu a yadda suke, ashe Allah (T) bai cewa: “Bamu kasance masu azabtarwa ba har sai mun tada dan sakonmu (Manzo)”? Ta ya Allah zai saka wadanda bai ake musu da Manzo ba a wuta? Ai sai Allah (T) ya aiko da Manzo ne, sakonsa ya riske ka kaki ka bi shi hark a mutu, sai ya azabtaka akan cewa an yanke maka hujja ka ki karba.
Ko da yake, mutanen nan ba su tsaya a kan cewa iyayen Annabi (S) ne kawai a wuta ba, sai dai suka rufe idonsu suka kirkiri karyar cewa wai wanda ya raini Annabi (S) ya bashi kulawa ma, wato Abudalib (AS) wai ya mutu yana Mushiriki ne. Wani da ya Musulunta ‘yan watanni kafin wafatin Annabi (S), bai ma san Abudalib ba, bai taba ganinsa ba, ya yi musu ruwaya cewa wai da Abudalib (AS) ya zo mutuwa, bayan ya shekara 13 yana taimakon Annabi (S) a wajen isar da sakon addinin nan, wai amma duk bai Musulunta ba, wai sai Annabi (S) yace masa; Ya baba, ka Musulunta, sai Abudalib (AS) wai ya ji nauyin hakan, ya duba yaga Mushirikai a gewaye da shi, sai yace ma Manzon Allah (S); Ya Dana. ‘Ni ina kan addinin iyayena.’
Don haka wai sai ya mutu yana Mushiriki. Saboda su sun dauka cewa iyayen Annabi (S) din Mushirikai ne. In da gaske ne Abudalib (AS) yace yana kan addinin iyayensa ne, ai iyayensa, wato kakannin Manzon Allah (S) dukkansu Musulmi ne masu bin Musuluncin da Allah (T) ya aiko Annabi Ibrahim (AS) da shi. Idan za ka taimaki kanka, sai ka yarda da ruwayoyin da aka samu daga ‘ya’ya da jikokin Annabi (S), da ke tabbatar da cewa Abudalib (AS) Musulmi ne, na farko-farko ma, sai dai ya boye imaninsa ne saboda ya samu damar taimakon Annabi (S). Wannan kuma bai buya ma kowa ba cewa an samu Mumini a cikin fadan Fir’auna da yake bin Musa (AS) amma ya boye imaninsa saboda ta hakan ne kawai zai iya taimakon Annabi Musa (AS).
Wato abin da ya faru shine, wasu tunda ya zama ba iyayensu kawai ba, har su kansu sun girma suna bautawa gumaka ne, iyayensu sun mutu suna Mushirikai, don haka suka gummace suce ai ba iyayensu ne kawai za su shiga wuta ba har da iyayen Manzon Allah (S) da iyayen Ali (AS) ma. Don haka kun ga sai ya zama in aka ce musu Allah (T) ya yi alkawarin wanzar da Shugabanci a tsatson Annabi Ibraheem (AS) wadanda ba su kasance azzalumai (kafirai ba), sai suce ai a tsatson Ibrahim din, da aka gangaro, su iyayen Annabi (S) sun kasance daga cikin azzalumai (Kafirai) ne. Don su kare maslahar sarautarsu suka dankara kafirci a kan iyayen Manzon Allah (S).
Gaskiyar Magana shine, Allah ya sanya iyayen Manzon Allah (S) su kasance akan addinin Annabi Ibrahim (AS) ne. Kuma ba kawai addini ba, sai da Allah (T) ya gadar musu da ilimi da kyawun sura da haibar Annabi Ibrahim (AS). Har ma yazo cewa; a yayin da Sarki Abrahata ya ga Abdulmudallib (kakan Annabi (S), sai ya tsaya yana ta kallon fuskarsa, ya yaba da kyawunta da haibar da ke tattare da ita, bai taba ganin kyakkyawa kamarsa ba. Sai yace masa; Shin a cikin iyayenka akwai mai irin kyawun nan da hasken da na gani a cikin fuskarka? Sai Abdulmudalib (AS) yace masa; ‘Kwarai kuwa ya kai wannan sarki! Dukkan iyayena sun kasance kyawawa, ma’abota haske da haiba.’ Malam, wannan haibar da hasken da kyawun, ajiyar Allah ne na ManzonSa (S) a cikin wannan tsarkakakken tsatson.
Yaushe zan aminta maka da wani tatsuniyar jingina kafirci ga mahaifan Fiyayyen halitta baki daya? A in azan yarda da kai a yayin da kake kokarin jefa Mahaifan Ma’abocin ceto a ranar Alkiyama a wuta? Iyayen Annabi na, Muminai ne, Fiyayyu akan dukkan al’ummar Annabi (S) ba kawai Sahabbansa ba. Ban gushe ba ina fatan Allah (T) ya yi mana makoma da makomar Abdullahi da Amina da Abudalib da Fatima bint Asad (AHS).
Insha Allah a cigaba za mu ji labarin haihuwar wannan Annabi (S) da irin karairaki da aka lafta a ciki don a rage kima da darajarsa ga al’ummarsa (S). Allah ya kara mana soyayyar Manzon Allah (S).
Cigaban wannan nazarin zai sauya fasali kadan, kasancewar mun shigo watan da aka haifi fiyayyen halitta, Masoyinmu abin kaunarmu, Muhammad Dan Aminatu da Abdullahi (S). Ko da yake a watan akwai abubuwan da ya kamata ace mun waiwaye su mu ga abubuwa a hakikarsu, musamman abin da ya shafi batun Hijirar Annabi (S) daga Makkah zuwa Madina, wanda ya kasance fitan Annabi (S) daga Makka ya faru ne a ranar 1 ga Rabi’ul Auwal, shekara ta 13 bayan aike.
Wannan hijirar ce ta kasance silan kafa daular addinin Musulunci a garin Madina, daular da ta fadada har sai da ta mamaye duniya baki daya.
To, darussan da ke kunshe a cikin wannan Hijirar abubuwa ne da ya kamata ya zama mun yi nazarinsu, tun kama daga dalilin yin hijirar, da kwanciyar Shugaban Muminai a shimfidar Manzon Allah (S) a daren Hijira, da fitan Annabi (S) inda har ya samu dan rakiya masanin hanya, wanda ya amince zai raka Annabi (S) har garin Madina, amma da suka shiga cikin kogo suka ji alamun Kafirai za su gano inda suka buya, sai shi wannan dan rakiyan ya fara damuwa yana bakin ciki, akan me yasa ya yarda ya raka Annabi (S) alhali ana kama su kashe su za a yi?
Shine kamar yadda Allah (T) yake bamu labari a Alkur’ani, sai Manzon Allah (S) yace ma wannan dan rakiyar nasa; “Kar ka yi bakin ciki, Allah yana tare da mu.” Wato ka bar damuwa ba wani abu da zai same mu, Allah zai kiyaye mu. Wani yana iya cewa, ai Allah (T) yace masa ‘Sahibihi’, wato ‘Sahibinsa’ ne, wanda yake nufin yabo ne na musamman ga wannan dan rakiyar. Sai muce masa ai Allah (T) yace ma Annabi (S) Sahibin Mushirikai ma. Baka ji ba, a yayin da suka cewa Annabi (S) mahaukaci, sai Allah (T) yace musu: “Sahibinku (yana nufin Annabi) ba mahaukaci bane.” Ko a wani wajen yace; “Sahibinku ba batacce bane”? Don haka koma wane ne wannan dan rakiyar, wanda mai bai inganta cewa wanda ake cewa bane, ba ana nufin an yabe shi bane.
Wannan wani bahasi ne da zai zo nan gaba musamman da ruwayoyi insha Allah, ta yadda za mu fahimci karfi da yaji an yi kokarin kange matsayin Imam Ali (AS) ne na fansar rayuwar Manzon Allah (S) yana me neman yardar Allah da ya yi a daren hijira, a yayin da ya kwanta a shimfidar Annabin da Mushirikai sukai gangamin kashewa.
Kun san jarumtar Ali (AS) irin na Annabi (S), irin kuma na ‘ya’yan Hashim ne. Kila bamu sani ba, ko mun manta cewa Allah (T) bai halicci wasu mutane da suka kai Banu Hashim jarumta ba. Ya zo a cikin littafin Al-Irshad cewa; A yakin Hunaini, bayan da Sahabbai suka gudu suka bar Annabi (S), sai ya kasance daga shi sai mutum goma. To, mutum tara daga cikin goman nan dukkansu Banu Hashim ne. mutum na goma shine Aiman (dan gidan Ummu Aiman (RA)). Da aka kashe Aiman sai ya kasance saura mutum tara dukkansu Hashimawa ne tare da Manzon Allah (S).
Hashim shine kakan Manzon Allah (S) na biyu. Kamar yadda muka sani, mahaifin Annabinmu Tsarkakakke dan Tsarkaka shine Shugabanmu Abdullahi Dan Abdulmudallib dan Hashim (AS). Wadannan tsarkakan bayin da suka kasance masu sujuda a tsawon kasancewarsu. Allah (T) ya zabe su, ya fifita su a kan dukkan talikai, kuma ya sanya su masu Imani, masu sujuda, ya rika jujjuyawa da tsatson Annabinsa Muhammad (S) ta cikinsu tun daga Adamu (AS) har zuwa kan na karshensu Abdulmudallib (AS).
A cikin Khisal, daga Manzon Allah (S) yake cewa: “Allah Mai girma da daukaka ya kasa mutanen kasa zuwa gida biyu; sai ya sanya ni a kashin da ya fi alkairi. Sannan sai ya kasa wannan rabin (mafi alkairin) gida uku, sai na kasance fiyayyen kaso ukun. Sai Allah (T) ya zabi Larabawa daga cikin dukkan mutane, ya kuma zabi Kuraishawa daga dukkan Larabawa, sannan ya zabi Banu Hashim daga dukkan Kuraishawa, sannan ya kuma zaban Banu Abdulmudallib daga cikin Banu Hashim, sai Allah (T) ya zabe ni daga cikin dukkan Banu Abdulmudallib.”
A wajenmu, dangin Manzon Allah (S) sune mafiya kyawu da tsarkakan dangi. Mu mabiya Annabi Muhammad (S) mun yi Imani da cewa iyayensa tun daga kan Abdullahi har zuwa kan Annabi Isma’il zuwa Annabi Adam (AS) dukkansu Musulmai ne, masu Imani da Allah (T). Ba’a taba samun Mushiriki a tsatson Annabi (S). Wasu ruwayoyi da wasu suka kawo a cikin littafansu cewa wai wani ya tambayi Annabi cewa ina babansa yake? Sai Annabi wai yace wai da babanka da babana duk suna wuta (Wal iyazu billah) duk karyar banza da hofi ce. Kirkirarrun labarai ne don a kushe darajar Manzon Allah (S).
Yaushe Allah zai shaida mana cewa ya jujjuya Annabi a tsatson masu sujjada kuma ya zama an samu Mushiriki a cikin iyayensa? Ballantana kuma babu wani da ya isa ya kawo maka cewa an taba samun wani daga iyayen Manzon Allah (S) da a tarihi aka ganshi ya ma gunki sujada. Larabawa suna bautar gumaka ne kafin Musulunci, amma ko a lokacin su gidan iyaye da kakannin Annabinmu (S) ba su taba bautawa gunkin ba. Don haka ne ma Annabi (S) ya iya tasowa a hannunsu tsawon shekaru 40 kafin ai masa wahayi bai taba bautar gunki ba.
Abin da ya inganta shine iyayen Manzon Allah (S) sun kasance ne mabiya addinin Annabi Ibrahim (AS), wanda su ne suka kasance halifofi kuma wasiyan karshe na Annabi Ibraheem (AS) kafin bayyanar Annabi Muhammad (S).
Malam, ka kaddara cewa dukkansu Mushirikai ne, saboda a lokacin da suka rasu ba a aiko musu da Manzo ba, ba su samu mai kira ba, balle ya kira su su bi Allah. Sai suka mutu a yadda suke, ashe Allah (T) bai cewa: “Bamu kasance masu azabtarwa ba har sai mun tada dan sakonmu (Manzo)”? Ta ya Allah zai saka wadanda bai ake musu da Manzo ba a wuta? Ai sai Allah (T) ya aiko da Manzo ne, sakonsa ya riske ka kaki ka bi shi hark a mutu, sai ya azabtaka akan cewa an yanke maka hujja ka ki karba.
Ko da yake, mutanen nan ba su tsaya a kan cewa iyayen Annabi (S) ne kawai a wuta ba, sai dai suka rufe idonsu suka kirkiri karyar cewa wai wanda ya raini Annabi (S) ya bashi kulawa ma, wato Abudalib (AS) wai ya mutu yana Mushiriki ne. Wani da ya Musulunta ‘yan watanni kafin wafatin Annabi (S), bai ma san Abudalib ba, bai taba ganinsa ba, ya yi musu ruwaya cewa wai da Abudalib (AS) ya zo mutuwa, bayan ya shekara 13 yana taimakon Annabi (S) a wajen isar da sakon addinin nan, wai amma duk bai Musulunta ba, wai sai Annabi (S) yace masa; Ya baba, ka Musulunta, sai Abudalib (AS) wai ya ji nauyin hakan, ya duba yaga Mushirikai a gewaye da shi, sai yace ma Manzon Allah (S); Ya Dana. ‘Ni ina kan addinin iyayena.’
Don haka wai sai ya mutu yana Mushiriki. Saboda su sun dauka cewa iyayen Annabi (S) din Mushirikai ne. In da gaske ne Abudalib (AS) yace yana kan addinin iyayensa ne, ai iyayensa, wato kakannin Manzon Allah (S) dukkansu Musulmi ne masu bin Musuluncin da Allah (T) ya aiko Annabi Ibrahim (AS) da shi. Idan za ka taimaki kanka, sai ka yarda da ruwayoyin da aka samu daga ‘ya’ya da jikokin Annabi (S), da ke tabbatar da cewa Abudalib (AS) Musulmi ne, na farko-farko ma, sai dai ya boye imaninsa ne saboda ya samu damar taimakon Annabi (S). Wannan kuma bai buya ma kowa ba cewa an samu Mumini a cikin fadan Fir’auna da yake bin Musa (AS) amma ya boye imaninsa saboda ta hakan ne kawai zai iya taimakon Annabi Musa (AS).
Wato abin da ya faru shine, wasu tunda ya zama ba iyayensu kawai ba, har su kansu sun girma suna bautawa gumaka ne, iyayensu sun mutu suna Mushirikai, don haka suka gummace suce ai ba iyayensu ne kawai za su shiga wuta ba har da iyayen Manzon Allah (S) da iyayen Ali (AS) ma. Don haka kun ga sai ya zama in aka ce musu Allah (T) ya yi alkawarin wanzar da Shugabanci a tsatson Annabi Ibraheem (AS) wadanda ba su kasance azzalumai (kafirai ba), sai suce ai a tsatson Ibrahim din, da aka gangaro, su iyayen Annabi (S) sun kasance daga cikin azzalumai (Kafirai) ne. Don su kare maslahar sarautarsu suka dankara kafirci a kan iyayen Manzon Allah (S).
Gaskiyar Magana shine, Allah ya sanya iyayen Manzon Allah (S) su kasance akan addinin Annabi Ibrahim (AS) ne. Kuma ba kawai addini ba, sai da Allah (T) ya gadar musu da ilimi da kyawun sura da haibar Annabi Ibrahim (AS). Har ma yazo cewa; a yayin da Sarki Abrahata ya ga Abdulmudallib (kakan Annabi (S), sai ya tsaya yana ta kallon fuskarsa, ya yaba da kyawunta da haibar da ke tattare da ita, bai taba ganin kyakkyawa kamarsa ba. Sai yace masa; Shin a cikin iyayenka akwai mai irin kyawun nan da hasken da na gani a cikin fuskarka? Sai Abdulmudalib (AS) yace masa; ‘Kwarai kuwa ya kai wannan sarki! Dukkan iyayena sun kasance kyawawa, ma’abota haske da haiba.’ Malam, wannan haibar da hasken da kyawun, ajiyar Allah ne na ManzonSa (S) a cikin wannan tsarkakakken tsatson.
Yaushe zan aminta maka da wani tatsuniyar jingina kafirci ga mahaifan Fiyayyen halitta baki daya? A in azan yarda da kai a yayin da kake kokarin jefa Mahaifan Ma’abocin ceto a ranar Alkiyama a wuta? Iyayen Annabi na, Muminai ne, Fiyayyu akan dukkan al’ummar Annabi (S) ba kawai Sahabbansa ba. Ban gushe ba ina fatan Allah (T) ya yi mana makoma da makomar Abdullahi da Amina da Abudalib da Fatima bint Asad (AHS).
Insha Allah a cigaba za mu ji labarin haihuwar wannan Annabi (S) da irin karairaki da aka lafta a ciki don a rage kima da darajarsa ga al’ummarsa (S). Allah ya kara mana soyayyar Manzon Allah (S).
Tsage Gaskiya (5)
Daga Saifullahi M Kabir
Cikin masu yin comment akan rubutun da nake yi, wani bawan Allah ya min nasiha, yana mai cewa: “Bawan Allah ka ji tsoron Allah. Dukkan Sahabban Annabi ‘yan Aljanna ne, ba wanda zai shiga wuta a cikinsu. Kuma mu muna tare da su, muna son su kome suka yi. Ka dena zagin Sahabbai. Annabi yace mu kame bakinmu daga abin da duk suka aikata, har ma yace musu ku aikata duk abin da kuka ga dama Allah ya ya gafarta muku.”
Da farko sai nace, na gode sosai, kuma na ji dadi da wannan nasiha, domin kamar yadda Manzon Allah (S) ya fada cewa: “Addini nasiha ne.” don haka ne ma na dage wajen yi ma mutane nasiha akan wajibcin nisantar wadanda suka bijirewa Manzon Allah (S), da kira zuwa ga bin wadanda aka ce mu bi su. Nagoda da nasiharka. Ko ba komai hakan ya nuna ana biye da abin da nake cewa. In da kuskure a ciki a sanar da ni kuskuren ne bisa hujja ba da kame-kame ba. Allah ya kara mana tsoronSa.
Mu fara da fadinka cewa: Dukkan Sahabban Annabi ‘yan Aljanna ne, ba wanda zai shiga wuta a cikinsu.” Sai nace maka, har da mutum 12 din nan da Manzon Allah (S) ya kira su da Sahabbansa! Kuma yace amma su Munafukai ne, kuma yace ba za su shiga Aljanna ba? Suma kana tare da su ko? Ka amince Allah ya maka makoma daya da su?
Hadisi na 7212 a cikin Sahihu Muslim, Huzaifa (Ma’abocin sirrin Manzon Allah) ya ba da labari cewa, Manzon Allah (S) yace: “A cikin SAHABBAINA akwai wasu munafukai guda goma sha biyu (12). Daga cikinsu akwai mutum takwas da ba zai yiwu su shiga Aljanna ba sai idan har rakumi zai iya wucewa ta hujin allura….”
A cikin ruwayar, Manzon Allah (S) cewa yayi fa; ‘Fi ashabiy….’ Wato, a cikin Sahabbaina. Kai kuma yanzu kace min duk Sahabban Annabi (S) ‘yan Aljanna ne. Manzon Allah (S) yace; Ba za su shiga Aljanna ba! Kai kace ba wanda zai shiga wuta a cikin Sahabban. Maganar wa za mu kama tsakanin taka da ta Annabinmu Muhammad (S)?
Ballantana ma, wannan kana iya kace, ai su Munafukai ne. Ah! To ka san adadin Munafukai a cikin Sahabban Manzon Allah (S) ne? Ka san suwaye Munafukai su waye ba su ba? Baka ji a cikin Alkur’ani Allah (T) yana fadawa Annabi (S) cewa daga cikin Sahabbansa akwai wadanda suka kware da Munafunci har ta kai ga cewa Annabin ma ba zai iya saninsu ba, Allah ne kawai ya san su?
Ba mamaki sune wadannan masu canza addinin Annabi (S) din a bayan wafatinsa. Wadanda Imamu Bukhari ya kawo mana hadisai a cikin Sahihinsa, Annabi (S) yana bada labarinsu cewa ranar Lahira za a kawo su wajensa ya gansu, sun san shi ya sansu, sai ya ga za a kada su, yace zuwa ina? Ace zuwa wuta! Yace Ya Rabbi Sahabbaina ne. Sai ace ma Annabi (S) baka san abin da suka aikata a bayan wafatinka ba. Sun canza addininka sun gayyara sunnarka!
Mu duba ruwayoyin mana kawai a yadda suke a cikin Sahihul Bukhari? Mu fara da Hadisi na 6576 da hadisi na 7049 a cikin Sahihul Bukhari, Mugira yace, ya ji Abu Wa’il daga Abdullahi yace: Manzon Allah (S) yace: “Ni ina tare da ku a bakin Tafki (a ranar Alkiyama), kuma na san wasu mutane daga cikinku, za a zo ana kore su, a raba su da ni. Zan ce; Ya Ubangijina, Sahabbaina ne. Sai ace min; ‘Hakika baka san abin da suka aikata a bayanka ba.”
A hadisi na 6583 a cikin Bukharin, Manzon Allah (S) yace ne, a yayin da yake shayar da mutane a tafki da ruwan da duk wanda ya sha ba zai kuma jin kishi ba har abada. Sai azo a kore wasu jama’a daga inda yake. Yace Jama’an ya sansu sun san shi (wato sun yi rayuwa ne tare da shi), amma sai a raba tsakaninsa da su.
A hadisin dake gaban wannan, na 6583 kenan, Abu Sa’idul Kudri yace; Manzon Allah (S) yace, a yayin da aka kore sahabban nashi daga gare ni, zan ce; “Ya Ubangijina su fa daga gareni suke. Sai ace min; Kai baka san abin da suka yi a bayanka ba.” A nan Manzon Allah (S) zai yi musu bara’a. Yace a nisanta shi da duk wanda ya haddasa wani abu a bayana daga gareni. Wato ai wuta da su.
Eh mana. Idan mutum na tare da Manzon Allah (S) a Lahira sai aka zo aka raba shi da Annabi wane makoma za a kais hi? Wuta! Kamar yadda idan muka koma Hadisi na 6587 a cikin Bukhari din, za mu ga ruwayar Abu Huraira daga Annabi (S) yana cewa: A yayin da yake tsaye a cikin mutanen, wadanda ya san su sun kuma san shi (Sahabbai kenan), sai WANI MUTUM ya fito ya shiga tsakanina da su. Sai yace musu; “Muje!!!” Manzon Allah (S) yace, sai nace, “Ina za su je?” Sai wannan Mutumin da yake kada su, yacewa Annabi (S), “Wuta za su je wallahi.” Sai Annabi (S) yace, “Me ya faru da su?” Sai mutumin yace ma Annabi (S): “Sun juya baya ma addini, sun yi ridda ne a bayan baka” (wato, sun canza addininka, sun komo da jahiliyyar da suka baro). Manzon Allah (s) yace; “Wadanda za su yi saura a cikinsu ba za su wuce misalin ‘hamalin ni’am’ ba.”
Ance; ‘hakan na nufin’, misali, idan makiyaya na tafe da garken shanu masu yawa, akan samu ‘yan kwarori da sukan mutu a hanya ko a yanka su sakamakon wahala ko ciwo ko su bace. To misalin wadanda za a bari tare da Manzon Allah (S) a wannan wajen a cikin sahabbansa basu wuce irin ‘yan kwarorin nan da kan salwanta a cikin garke ba. Sauran duk wuta za a tura su.
Wa zai tura su watan to? Ai kun ji a hadisi na 6587, Manzon Allah (S) yace mana, wani mutum ne zai zo ya shiga tsakaninsa da Sahabban nasa, ya kada su zuwa Jahannama. Yace masa baka san abin da suka aikata bayan wafatinka ba. Sun canza addininka sun bar koyarwarka, sun shimfida sarautansu, sun mai da addinin kamar tafiyar jahiliyyar da suka baro. Me yasa Mutum ne zai yi ba Mala’iki ba? Kun san mutumin? Shine wannan da Manzon Allah (S) yace mana shi zai raba wuta da Aljanna a ranar Alkiyama. Amirulmuminin Ali Dan Abudalib (AS), kamar yadda nan gaba za mu zo da ruwayoyi a kan hakan.
To, kai mai cewa dukkan Sahabban Annabi ‘yan Aljanna ne bad an wuta a cikinsu kuma kana tare da su ko me suka aikata. Har yanzu kana nan a bakanka? In ka kafe akan hakan, kana karyata Manzon Allah (S) ne? Ko masu ruwayar wadanda su Sahabban ne da kansu? Ko Imamu Bukhari din duk da amincin da ka bashi? Malam! Ka amince Allah ya maka makoma daya da wadannan mutanen da Imam Ali (AS) zai kora su wuta da umurnin Allah (T) da amincewar Manzon Allah (S)?
Kaga dai a nan Manzon Allah (S) bai ce munafukai bane. A’a, Sahabbansa ne, kila sun boye munafuncin ne, sai bayan da suka shayar da shi guba da sunan magani kamar yadda Mukai bayai a baya, Wafatinsa ke da wuya suka canza duk koyarwarsa. Suka bi ta kan iyalan gidansa. Suka canza duk wata sunnarsa, kamar yadda a baya muka kawo cewa hatta Sallah sai da suka canza. Bayan sun kwace hakkin shugabancin al’ummar Musulmi daga hannun masu hakkin. Sun kuma kwace dukiya da gadon masu gadon Annabi sun shirga masa karya cewa wai yace ba a gadonsa.
Malam, ba muna cewa a Sahabbai babu mutanen kirki da suka tsayu a kan addinin Annabi bane. A’a muna cewa ne akwai na kirki da suka wanzu a kan Addinin, akwai kuma masu juya baya, masu butulci, masu kangarewa koyarwar Annabi yana raye da bayan ransa. Don haka mu ba mu yi Imani da cewa wai dukkan Sahabban Annabi ababen riko bane. Face ma an ce ne su Sahabban da mu masu zuwa a bayansu mu yi riko da Ahlulbait (AS), wanda Imam Ali (AS) ne samansu.
Ba wanda muke zagi a cikinsu. Muna fadan gaskiya ne. Kuma ba Shi’a suka ruwaito ba, Sunnah ne. Amma gaskiyar magana ba wani waje da Annabi (S) yace mu kame baki daga abin da Sahabbai suka aikata. In kuma ka san wajen ka kawo min. Abin da na sani kawai shine tunda ya zama kun dauke su a matsayin masu koya muku Musulunci, to wajibi a sanar da ku cewa akwai abin da suka kirkira a bayan Annabi (S) wanda ba shine Musuluncin da Annabi ya koyar ba. Kuma mu da muka san hakan, hakki ne a kanmu mu sanar da ku gaskiya. Iyalan Manzon Allah (S) da Alkur’ani, su ne ababen riko ba waninsu ba ko waye!
Shin zai yiwu Manzon Allah (S) yace wa wani ya aikata duk abin da yaso, tun kafin ya aikata ma an yafe masa. Wannan a hankalce ma ya saba ga duk wanda kwakwalwarsa ba irin na dabba bane! Duk wanda ya aikata mummuna misalign kwayar zarra zai gani a ranar Alkiyama, haka ma duk wanda ya aikata mai kyau komai kankantarsa zai gani a ma’auninsa ranar Alkiyama. Koda wannan mutumin Annabi ne, ba sahabi kawai ba. In har Annabi zai ce su aikata abin da suka so an yafe musu, me zai sa kuma a kada su wuta ace sun canza a bayansa?
Za mu cigaba insha Allah.
Cikin masu yin comment akan rubutun da nake yi, wani bawan Allah ya min nasiha, yana mai cewa: “Bawan Allah ka ji tsoron Allah. Dukkan Sahabban Annabi ‘yan Aljanna ne, ba wanda zai shiga wuta a cikinsu. Kuma mu muna tare da su, muna son su kome suka yi. Ka dena zagin Sahabbai. Annabi yace mu kame bakinmu daga abin da duk suka aikata, har ma yace musu ku aikata duk abin da kuka ga dama Allah ya ya gafarta muku.”
Da farko sai nace, na gode sosai, kuma na ji dadi da wannan nasiha, domin kamar yadda Manzon Allah (S) ya fada cewa: “Addini nasiha ne.” don haka ne ma na dage wajen yi ma mutane nasiha akan wajibcin nisantar wadanda suka bijirewa Manzon Allah (S), da kira zuwa ga bin wadanda aka ce mu bi su. Nagoda da nasiharka. Ko ba komai hakan ya nuna ana biye da abin da nake cewa. In da kuskure a ciki a sanar da ni kuskuren ne bisa hujja ba da kame-kame ba. Allah ya kara mana tsoronSa.
Mu fara da fadinka cewa: Dukkan Sahabban Annabi ‘yan Aljanna ne, ba wanda zai shiga wuta a cikinsu.” Sai nace maka, har da mutum 12 din nan da Manzon Allah (S) ya kira su da Sahabbansa! Kuma yace amma su Munafukai ne, kuma yace ba za su shiga Aljanna ba? Suma kana tare da su ko? Ka amince Allah ya maka makoma daya da su?
Hadisi na 7212 a cikin Sahihu Muslim, Huzaifa (Ma’abocin sirrin Manzon Allah) ya ba da labari cewa, Manzon Allah (S) yace: “A cikin SAHABBAINA akwai wasu munafukai guda goma sha biyu (12). Daga cikinsu akwai mutum takwas da ba zai yiwu su shiga Aljanna ba sai idan har rakumi zai iya wucewa ta hujin allura….”
A cikin ruwayar, Manzon Allah (S) cewa yayi fa; ‘Fi ashabiy….’ Wato, a cikin Sahabbaina. Kai kuma yanzu kace min duk Sahabban Annabi (S) ‘yan Aljanna ne. Manzon Allah (S) yace; Ba za su shiga Aljanna ba! Kai kace ba wanda zai shiga wuta a cikin Sahabban. Maganar wa za mu kama tsakanin taka da ta Annabinmu Muhammad (S)?
Ballantana ma, wannan kana iya kace, ai su Munafukai ne. Ah! To ka san adadin Munafukai a cikin Sahabban Manzon Allah (S) ne? Ka san suwaye Munafukai su waye ba su ba? Baka ji a cikin Alkur’ani Allah (T) yana fadawa Annabi (S) cewa daga cikin Sahabbansa akwai wadanda suka kware da Munafunci har ta kai ga cewa Annabin ma ba zai iya saninsu ba, Allah ne kawai ya san su?
Ba mamaki sune wadannan masu canza addinin Annabi (S) din a bayan wafatinsa. Wadanda Imamu Bukhari ya kawo mana hadisai a cikin Sahihinsa, Annabi (S) yana bada labarinsu cewa ranar Lahira za a kawo su wajensa ya gansu, sun san shi ya sansu, sai ya ga za a kada su, yace zuwa ina? Ace zuwa wuta! Yace Ya Rabbi Sahabbaina ne. Sai ace ma Annabi (S) baka san abin da suka aikata a bayan wafatinka ba. Sun canza addininka sun gayyara sunnarka!
Mu duba ruwayoyin mana kawai a yadda suke a cikin Sahihul Bukhari? Mu fara da Hadisi na 6576 da hadisi na 7049 a cikin Sahihul Bukhari, Mugira yace, ya ji Abu Wa’il daga Abdullahi yace: Manzon Allah (S) yace: “Ni ina tare da ku a bakin Tafki (a ranar Alkiyama), kuma na san wasu mutane daga cikinku, za a zo ana kore su, a raba su da ni. Zan ce; Ya Ubangijina, Sahabbaina ne. Sai ace min; ‘Hakika baka san abin da suka aikata a bayanka ba.”
A hadisi na 6583 a cikin Bukharin, Manzon Allah (S) yace ne, a yayin da yake shayar da mutane a tafki da ruwan da duk wanda ya sha ba zai kuma jin kishi ba har abada. Sai azo a kore wasu jama’a daga inda yake. Yace Jama’an ya sansu sun san shi (wato sun yi rayuwa ne tare da shi), amma sai a raba tsakaninsa da su.
A hadisin dake gaban wannan, na 6583 kenan, Abu Sa’idul Kudri yace; Manzon Allah (S) yace, a yayin da aka kore sahabban nashi daga gare ni, zan ce; “Ya Ubangijina su fa daga gareni suke. Sai ace min; Kai baka san abin da suka yi a bayanka ba.” A nan Manzon Allah (S) zai yi musu bara’a. Yace a nisanta shi da duk wanda ya haddasa wani abu a bayana daga gareni. Wato ai wuta da su.
Eh mana. Idan mutum na tare da Manzon Allah (S) a Lahira sai aka zo aka raba shi da Annabi wane makoma za a kais hi? Wuta! Kamar yadda idan muka koma Hadisi na 6587 a cikin Bukhari din, za mu ga ruwayar Abu Huraira daga Annabi (S) yana cewa: A yayin da yake tsaye a cikin mutanen, wadanda ya san su sun kuma san shi (Sahabbai kenan), sai WANI MUTUM ya fito ya shiga tsakanina da su. Sai yace musu; “Muje!!!” Manzon Allah (S) yace, sai nace, “Ina za su je?” Sai wannan Mutumin da yake kada su, yacewa Annabi (S), “Wuta za su je wallahi.” Sai Annabi (S) yace, “Me ya faru da su?” Sai mutumin yace ma Annabi (S): “Sun juya baya ma addini, sun yi ridda ne a bayan baka” (wato, sun canza addininka, sun komo da jahiliyyar da suka baro). Manzon Allah (s) yace; “Wadanda za su yi saura a cikinsu ba za su wuce misalin ‘hamalin ni’am’ ba.”
Ance; ‘hakan na nufin’, misali, idan makiyaya na tafe da garken shanu masu yawa, akan samu ‘yan kwarori da sukan mutu a hanya ko a yanka su sakamakon wahala ko ciwo ko su bace. To misalin wadanda za a bari tare da Manzon Allah (S) a wannan wajen a cikin sahabbansa basu wuce irin ‘yan kwarorin nan da kan salwanta a cikin garke ba. Sauran duk wuta za a tura su.
Wa zai tura su watan to? Ai kun ji a hadisi na 6587, Manzon Allah (S) yace mana, wani mutum ne zai zo ya shiga tsakaninsa da Sahabban nasa, ya kada su zuwa Jahannama. Yace masa baka san abin da suka aikata bayan wafatinka ba. Sun canza addininka sun bar koyarwarka, sun shimfida sarautansu, sun mai da addinin kamar tafiyar jahiliyyar da suka baro. Me yasa Mutum ne zai yi ba Mala’iki ba? Kun san mutumin? Shine wannan da Manzon Allah (S) yace mana shi zai raba wuta da Aljanna a ranar Alkiyama. Amirulmuminin Ali Dan Abudalib (AS), kamar yadda nan gaba za mu zo da ruwayoyi a kan hakan.
To, kai mai cewa dukkan Sahabban Annabi ‘yan Aljanna ne bad an wuta a cikinsu kuma kana tare da su ko me suka aikata. Har yanzu kana nan a bakanka? In ka kafe akan hakan, kana karyata Manzon Allah (S) ne? Ko masu ruwayar wadanda su Sahabban ne da kansu? Ko Imamu Bukhari din duk da amincin da ka bashi? Malam! Ka amince Allah ya maka makoma daya da wadannan mutanen da Imam Ali (AS) zai kora su wuta da umurnin Allah (T) da amincewar Manzon Allah (S)?
Kaga dai a nan Manzon Allah (S) bai ce munafukai bane. A’a, Sahabbansa ne, kila sun boye munafuncin ne, sai bayan da suka shayar da shi guba da sunan magani kamar yadda Mukai bayai a baya, Wafatinsa ke da wuya suka canza duk koyarwarsa. Suka bi ta kan iyalan gidansa. Suka canza duk wata sunnarsa, kamar yadda a baya muka kawo cewa hatta Sallah sai da suka canza. Bayan sun kwace hakkin shugabancin al’ummar Musulmi daga hannun masu hakkin. Sun kuma kwace dukiya da gadon masu gadon Annabi sun shirga masa karya cewa wai yace ba a gadonsa.
Malam, ba muna cewa a Sahabbai babu mutanen kirki da suka tsayu a kan addinin Annabi bane. A’a muna cewa ne akwai na kirki da suka wanzu a kan Addinin, akwai kuma masu juya baya, masu butulci, masu kangarewa koyarwar Annabi yana raye da bayan ransa. Don haka mu ba mu yi Imani da cewa wai dukkan Sahabban Annabi ababen riko bane. Face ma an ce ne su Sahabban da mu masu zuwa a bayansu mu yi riko da Ahlulbait (AS), wanda Imam Ali (AS) ne samansu.
Ba wanda muke zagi a cikinsu. Muna fadan gaskiya ne. Kuma ba Shi’a suka ruwaito ba, Sunnah ne. Amma gaskiyar magana ba wani waje da Annabi (S) yace mu kame baki daga abin da Sahabbai suka aikata. In kuma ka san wajen ka kawo min. Abin da na sani kawai shine tunda ya zama kun dauke su a matsayin masu koya muku Musulunci, to wajibi a sanar da ku cewa akwai abin da suka kirkira a bayan Annabi (S) wanda ba shine Musuluncin da Annabi ya koyar ba. Kuma mu da muka san hakan, hakki ne a kanmu mu sanar da ku gaskiya. Iyalan Manzon Allah (S) da Alkur’ani, su ne ababen riko ba waninsu ba ko waye!
Shin zai yiwu Manzon Allah (S) yace wa wani ya aikata duk abin da yaso, tun kafin ya aikata ma an yafe masa. Wannan a hankalce ma ya saba ga duk wanda kwakwalwarsa ba irin na dabba bane! Duk wanda ya aikata mummuna misalign kwayar zarra zai gani a ranar Alkiyama, haka ma duk wanda ya aikata mai kyau komai kankantarsa zai gani a ma’auninsa ranar Alkiyama. Koda wannan mutumin Annabi ne, ba sahabi kawai ba. In har Annabi zai ce su aikata abin da suka so an yafe musu, me zai sa kuma a kada su wuta ace sun canza a bayansa?
Za mu cigaba insha Allah.
Tsage Gaskiya (4)
Daga Saifullahi M Kabir
A cigaba da rubutunmu na wannan nazarin da muka fara, da yake yazo daidai da cewa yau 28 ga watan Safar ne, wanda rana mai kamar yau ne aka Shahadantar da Manzon Allah Muhammad (S), ta hanyar guba da aka dura a cikin tsimi da sunan wai magani aka bashi.
Jiya naje wajen buga irin takardar nan da ake rabawa ‘articles’ mai kunshe da sakon Wafatin Manzon Allah (S), a wajen da ake min aikin, wani ya dauki daya ya zauna ya karance shi tsaf, duk kuwa da yake rubutu ne kanana kuma mai yawa. Kasancewar ‘article’ din ya fi karkata ma bayani akan hana abin rubutu da Umar Dan Khaddabi tare da wasu daga sahabbai suka yi, da kuma bayani akan illar da rashin bada wannan abin rubutun ga Annabi (S) ya jawowa al’ummar Musulmi, kamar dai yadda in mutum yana bibiyan wannan nazarin zai ga mun kawo wasu daga ciki.
To, bayan ya karance tsaf. Sai yace min, Malam kai Dan Shi’a ne, ko kuwa sun kawo maka aikin ‘printing’ ne? Sai nace masa Ni Musulmi ne, me ya faru? Sai yace, takardar nan koda yake abubuwan da suka fada a cikinta gaskiya ne, amma gaskiyar magana akwai matsala a bayyana irin wadannan Hadisan. Sai nace masa, haba dai Malam. In dai Hadisi ne kuma ingantacce ai ban jin da wani matsala a cikin yada shi. Me yasa Malamanmu suka rubuta a littafinsu tun shekaru daruruwa ko ma dubbai in sun san akwai matsala a sanar da al’umma su. Ni ina ganin wannan yada Hadisan Annabi (S) ne, kuma duk mabiyin Sunnah zai yi farin ciki da hakan.
Sai Malamin yace min, baka ganin idan jahilai suka karanta wannan takardar za su iya dena ganin girman Sayyidina Umar? Sai nace masa, Radiyallahu Anh! Lallai dai mai sauki ne hakan, amma ni abin da nake gani shine, mu cire komai da komai tukunna, mu dauko zahirin abin, mu saka a faifai. Sayyadina Umar ya zama Sayyadina Umar ne saboda Manzon Allah (S). Kila da bai bi Annabi (S) da ba ma wanda zai san sunansa. Saboda haka tunda ya samu girman da ake ganinsa da shi saboda Manzon Allah (S), idan ya zama ya sabawa Annabi (S) a wani waje, kana ganin Musulmi mai Imani da Allah da Manzon da baya kuskure, zai goyi bayan Umar ya bar goyon bayan Annabi (S) akan sabawarsu? Yace A’a. Amma ai wannan abin a yi shiru ne da shi tunda ya riga ya faru, kuma su Sahabbai sun fi mu sanin dalilin da yasa suka hana Annabi (S) wannan abin rubutun. Ba gashi an ce ciwo ya masa tsanani ba, kaga ko don tausayawa ma za a iya ce masa ya hutar da kansa ba sai ya yi ba. Ni ina ga saboda wannan ne suka hana a bashi.
Nan nace, Malam kar ka warware imaninka mana. Baka ga sun ce hankalin Annabi (S) ya gushe bane? Wanda yana nufin suna so suce Manzon Allah ya zautu ne zai rubuta musu bata? Alhali yace zai rubuta shiriya ne da in aka rike ba za a taba bacewa ba a bayansa? To idan da gaske Sayyadina Umar da sahabban da suka taya shi hana a ba Annabi abin rubuta shiriya din nan sun yi Imani da Allah da Alkur’anin Allah, ashe ba a cikin Alkur’ani Allah ke cewa: “Abin da Manzo ya zo muku da shi ku rike shi ba, kuma abin da ya hane ku ku hanu ba?” Ashe Allah bai ce akan Annabinsa (S): “Kuma baya furuci bisa son ransa face wahayi da aka masa” ba? Ashe bai kuma ce: “Wanda ya bi Manzo hakika ya bi Allah” ba? Don haka in har sun yi Imani da Alkur’ani wallahi ba za su sabawa Annabi ba.
Nace, Malam idan kuma kace wai tausayawa ne yasa Umar yace ma Annabi zafin ciwo ya galabaitar da shi kar a bashi. Wai hakan yana tausayawa ne gare shi. Nan ma fadin Umar; “Hasbuna Kitabullah”, wato ‘Littafin Allah ya ishe mu’ ya karyata uzurin cewa suna tausayin Annabi ne. Domin kamar suna cewa ne bamu da bukatar Hadisin Annabi (S), ba su bukatar Sunnar Manzon Allah (S), Littafin Allah kawai ya ishe su, ba sai Annabi ya musu Hadisinsa ba. Wanda wannan kuma in muka ma Umar uzuri a kansa to wajibi ne mu ma duk wani Dan Qala-Qato, masu cewa basu yarda da Hadisai ba a yanzu sai Alkur’ani. Sai ya zama Sayyadina Umar ne farkon shugabansu.
Muna cikin maganar nan ne mutumin nan ya tubure aka cewa ni dan Shi’a ne, kuma gakiya da ma ya san ni dan Shi’a ne ba zai tsaya yin magana da ni yana bata lokacinsa ba. “Na zaci dan uwana Musulmi ne, ashe kai dan Shi’a ne. Allah ya shiryeku, ya ganar da ku hanya madaidaiciya.” Yace min. Ba wani jayayya sai nace masa, Amin.
To, labari ya cike mana rubutu yau. Sai nace gaskiyar magana akwai gayar rashin wayewa ga mutum, ya zama kiri-da-muzu ga hujja ana bashi yana bijirewa hujjar. Wani ya taba min magana, yace min, kaga ni ba dan Shi’a bane, amma ina rokonka ka sanar da ni gaskiyar magana, Manzon Allah (S) an kashe shi ne ya yi Shahada ko kuwa ya rasu ne kawai sakamakon rashin lafiya? Sai nace masa, ka nemi Sahihin Bukhari, ka je da shi wajen wani daga cikin Malaman garinku, idan kaje kace ya maka bayani akan Hadisi na 4458 da na 5712 da na 5714 da na 6886 da kuma na 6897. Ya bani labara cewa da yaje, ya budewa Malamin hadisan, sai Malamin ya karanta su kafin ya biya masa, ya koma ga wani ya karanta, ya kuma komawa ga wani ya karanta. Sai yace masa, ‘Yaro, kar ka biyewa wanda suka ce kazo ka karanci wadannan hadisan, ka tafi ka kyale su kawai.’ Karatun da bai masa ba kenan. A lokaci guda sai ya zama hakan da suka yi ne ya sa shi wannan ya fara zargin cewa lallai akwai damuwa kenan.
Idan ka duba Kilabul Magazi, Babin rashin lafiyar Annabi da Wafatinsa, Hadisi na 4458 a cikin Sahihul Bukhari, daya daga cikin matan Annabi (S), tana cewa; Mun yi masa dure a lokacin rashin lafiyarsa. Sai ya daga hannu yana mana nuni akan ‘Kar ku dura min.’ Sai muka ce, ai an sa mare lafiya dama da kin magani. Yayin da ya farka, sai yace; “Ashe ban hane ku a kan kar ku dura min ba?” Sai muka ce, ai kin magani ne kawai kake irin na mare lafiya. Sai yace da mu: “Kar wata a cikinku ta/ya bar wajen nan face ya sha ko ta sha (abin da kuka bani), kuma ina kallo, in banda Abbas, domin shi bai yi tarayya da ku ba.”
Me suka durawa Annabi (S)? Aka ce tsumi ne mai dauke da magani a ciki. Me yasa suka dura masa alhali yana cewa kar su dura masa? Sun sabawa Annabi (S) kenan ko? “Wanda ya bi Manzo hakika ya bi Allah.”, “Abin da Manzo ya zo muku da shi ku rike shi, abin da ya hane ku a kansa ku hau.” Inji Allah (T). Ina ce Manzon Allah (S) yace kar su dura masa!? Me yasa suka dura masa!?
Wata tambayar shine, da yaushe ya daga hannun ya musu nuni da kar su bashi tsimin? Kafin su bada ko? A ruwayar ance; ‘Yayin da ya farka.’ Ya farka daga mene? Kenan da suka bashi ya suma ne ko? Sai bayan da ya farfado sannan yace kar wani ko wata dake dakin su fita face Abbas, domin shi bai san abin da suka kulla ba. Ance Abbas ya shigo ne a lokacin, bashi suka durawa Annabi tsimin.
An kawo irin wannan hadisin har ila yau lamba ta 5712 a cikin Sahihul Bukhari, Kitabud Dibbu, Babul Ludud. Har ila yau, an kuma kawo irin Hadisin a Babin Diyya, Babin ‘Iza asaba kaumin…’ Hadisi na 6897. Kai, ka duba Babin Kisasi tsakanin mace da namiji a karkashin littafin Diyya, za ka ga irin wanna Hadisin na cewa wasu daga matan Manzon Allah (S) sun dura masa abin da suka kira magani alhali yana musu kashedi akan kar su dura masa. Yana nan a hadisi na 6889. Ko me yasa Imamu Bukhari ya kawo wannan Hadisin a babin Kisasin Oho?
To, duk ma ba wadannan ba. Wai me yasa Imamu Bukhari bai karishe mana hadisin ba mu ji yadda ta kaya. Da Manzon Allah (S) yace dole kowacce ta sha ko basu sha ba? Da ya kamata a karishe mana ace kowacce bata fita daga dakin ba sai da aka dura mata. Idan an yi hakan. Ko a nan din ma an saba umurnin Manzon Allah (S) ne?
Muna magana ne da gaskiya. Kuma muna cewa, gaskiyar magana mutane kar su bari a kunkume su a daji. Ya kamata su shigo gari. Mu gane cewa, gaskiyar magana fa wasu da ke kusa da Manzon Allah (S) sun cutar da shi. Kuma ba sau daya ko biyu ba kawai, so da dama suna saba umurninsa ne. Yasha yace ku bani, suce ba za su bada ba. Yace kar ku bani kuma su bashi din. Ya yi su kushe. Ya ki yi su ce don me bai yi ba. Ba kuma ta yadda zai yiwu wadannan da a zahiri suke wa Annabi (S) hakan, mun sani kuma ya zama wai a wajensu za mu karbi addini.
Za mu karbi addininmu ne a wajen wadannan shugabanni goma sha biyun da Manzon Allah (s) yace za su kasance a bayansa. Kamar yadda ya zo a cikin Sahihul Bukhari, Hadisi na 7222 da na 7223, daga Jabir Dan Samura, yace; Na ji Annabi (S) yana cewa: “Shugabanni goma sha biyu za su kasance.” Sai ya fadi wata kalma da ban ji me yace ba. Sai babana yace, Annabi (S) yace ne; “Dukkansu daga Quraishu suke.” Mun yi Imani da cewa wadannan 12 din sune halifofin Manzon Allah (S), kuma na farkonsu shine Imam Ali (AS) na karshensu Imam Mahdi (AS).
Ina kara jajantawa al’ummar Musulmi dangane da zagayowar ranar Shahadar Manzon Allah (S). Insha Allah za mu dora da rubutunmu gwargadon yadda hali ya bada.
A cigaba da rubutunmu na wannan nazarin da muka fara, da yake yazo daidai da cewa yau 28 ga watan Safar ne, wanda rana mai kamar yau ne aka Shahadantar da Manzon Allah Muhammad (S), ta hanyar guba da aka dura a cikin tsimi da sunan wai magani aka bashi.
Jiya naje wajen buga irin takardar nan da ake rabawa ‘articles’ mai kunshe da sakon Wafatin Manzon Allah (S), a wajen da ake min aikin, wani ya dauki daya ya zauna ya karance shi tsaf, duk kuwa da yake rubutu ne kanana kuma mai yawa. Kasancewar ‘article’ din ya fi karkata ma bayani akan hana abin rubutu da Umar Dan Khaddabi tare da wasu daga sahabbai suka yi, da kuma bayani akan illar da rashin bada wannan abin rubutun ga Annabi (S) ya jawowa al’ummar Musulmi, kamar dai yadda in mutum yana bibiyan wannan nazarin zai ga mun kawo wasu daga ciki.
To, bayan ya karance tsaf. Sai yace min, Malam kai Dan Shi’a ne, ko kuwa sun kawo maka aikin ‘printing’ ne? Sai nace masa Ni Musulmi ne, me ya faru? Sai yace, takardar nan koda yake abubuwan da suka fada a cikinta gaskiya ne, amma gaskiyar magana akwai matsala a bayyana irin wadannan Hadisan. Sai nace masa, haba dai Malam. In dai Hadisi ne kuma ingantacce ai ban jin da wani matsala a cikin yada shi. Me yasa Malamanmu suka rubuta a littafinsu tun shekaru daruruwa ko ma dubbai in sun san akwai matsala a sanar da al’umma su. Ni ina ganin wannan yada Hadisan Annabi (S) ne, kuma duk mabiyin Sunnah zai yi farin ciki da hakan.
Sai Malamin yace min, baka ganin idan jahilai suka karanta wannan takardar za su iya dena ganin girman Sayyidina Umar? Sai nace masa, Radiyallahu Anh! Lallai dai mai sauki ne hakan, amma ni abin da nake gani shine, mu cire komai da komai tukunna, mu dauko zahirin abin, mu saka a faifai. Sayyadina Umar ya zama Sayyadina Umar ne saboda Manzon Allah (S). Kila da bai bi Annabi (S) da ba ma wanda zai san sunansa. Saboda haka tunda ya samu girman da ake ganinsa da shi saboda Manzon Allah (S), idan ya zama ya sabawa Annabi (S) a wani waje, kana ganin Musulmi mai Imani da Allah da Manzon da baya kuskure, zai goyi bayan Umar ya bar goyon bayan Annabi (S) akan sabawarsu? Yace A’a. Amma ai wannan abin a yi shiru ne da shi tunda ya riga ya faru, kuma su Sahabbai sun fi mu sanin dalilin da yasa suka hana Annabi (S) wannan abin rubutun. Ba gashi an ce ciwo ya masa tsanani ba, kaga ko don tausayawa ma za a iya ce masa ya hutar da kansa ba sai ya yi ba. Ni ina ga saboda wannan ne suka hana a bashi.
Nan nace, Malam kar ka warware imaninka mana. Baka ga sun ce hankalin Annabi (S) ya gushe bane? Wanda yana nufin suna so suce Manzon Allah ya zautu ne zai rubuta musu bata? Alhali yace zai rubuta shiriya ne da in aka rike ba za a taba bacewa ba a bayansa? To idan da gaske Sayyadina Umar da sahabban da suka taya shi hana a ba Annabi abin rubuta shiriya din nan sun yi Imani da Allah da Alkur’anin Allah, ashe ba a cikin Alkur’ani Allah ke cewa: “Abin da Manzo ya zo muku da shi ku rike shi ba, kuma abin da ya hane ku ku hanu ba?” Ashe Allah bai ce akan Annabinsa (S): “Kuma baya furuci bisa son ransa face wahayi da aka masa” ba? Ashe bai kuma ce: “Wanda ya bi Manzo hakika ya bi Allah” ba? Don haka in har sun yi Imani da Alkur’ani wallahi ba za su sabawa Annabi ba.
Nace, Malam idan kuma kace wai tausayawa ne yasa Umar yace ma Annabi zafin ciwo ya galabaitar da shi kar a bashi. Wai hakan yana tausayawa ne gare shi. Nan ma fadin Umar; “Hasbuna Kitabullah”, wato ‘Littafin Allah ya ishe mu’ ya karyata uzurin cewa suna tausayin Annabi ne. Domin kamar suna cewa ne bamu da bukatar Hadisin Annabi (S), ba su bukatar Sunnar Manzon Allah (S), Littafin Allah kawai ya ishe su, ba sai Annabi ya musu Hadisinsa ba. Wanda wannan kuma in muka ma Umar uzuri a kansa to wajibi ne mu ma duk wani Dan Qala-Qato, masu cewa basu yarda da Hadisai ba a yanzu sai Alkur’ani. Sai ya zama Sayyadina Umar ne farkon shugabansu.
Muna cikin maganar nan ne mutumin nan ya tubure aka cewa ni dan Shi’a ne, kuma gakiya da ma ya san ni dan Shi’a ne ba zai tsaya yin magana da ni yana bata lokacinsa ba. “Na zaci dan uwana Musulmi ne, ashe kai dan Shi’a ne. Allah ya shiryeku, ya ganar da ku hanya madaidaiciya.” Yace min. Ba wani jayayya sai nace masa, Amin.
To, labari ya cike mana rubutu yau. Sai nace gaskiyar magana akwai gayar rashin wayewa ga mutum, ya zama kiri-da-muzu ga hujja ana bashi yana bijirewa hujjar. Wani ya taba min magana, yace min, kaga ni ba dan Shi’a bane, amma ina rokonka ka sanar da ni gaskiyar magana, Manzon Allah (S) an kashe shi ne ya yi Shahada ko kuwa ya rasu ne kawai sakamakon rashin lafiya? Sai nace masa, ka nemi Sahihin Bukhari, ka je da shi wajen wani daga cikin Malaman garinku, idan kaje kace ya maka bayani akan Hadisi na 4458 da na 5712 da na 5714 da na 6886 da kuma na 6897. Ya bani labara cewa da yaje, ya budewa Malamin hadisan, sai Malamin ya karanta su kafin ya biya masa, ya koma ga wani ya karanta, ya kuma komawa ga wani ya karanta. Sai yace masa, ‘Yaro, kar ka biyewa wanda suka ce kazo ka karanci wadannan hadisan, ka tafi ka kyale su kawai.’ Karatun da bai masa ba kenan. A lokaci guda sai ya zama hakan da suka yi ne ya sa shi wannan ya fara zargin cewa lallai akwai damuwa kenan.
Idan ka duba Kilabul Magazi, Babin rashin lafiyar Annabi da Wafatinsa, Hadisi na 4458 a cikin Sahihul Bukhari, daya daga cikin matan Annabi (S), tana cewa; Mun yi masa dure a lokacin rashin lafiyarsa. Sai ya daga hannu yana mana nuni akan ‘Kar ku dura min.’ Sai muka ce, ai an sa mare lafiya dama da kin magani. Yayin da ya farka, sai yace; “Ashe ban hane ku a kan kar ku dura min ba?” Sai muka ce, ai kin magani ne kawai kake irin na mare lafiya. Sai yace da mu: “Kar wata a cikinku ta/ya bar wajen nan face ya sha ko ta sha (abin da kuka bani), kuma ina kallo, in banda Abbas, domin shi bai yi tarayya da ku ba.”
Me suka durawa Annabi (S)? Aka ce tsumi ne mai dauke da magani a ciki. Me yasa suka dura masa alhali yana cewa kar su dura masa? Sun sabawa Annabi (S) kenan ko? “Wanda ya bi Manzo hakika ya bi Allah.”, “Abin da Manzo ya zo muku da shi ku rike shi, abin da ya hane ku a kansa ku hau.” Inji Allah (T). Ina ce Manzon Allah (S) yace kar su dura masa!? Me yasa suka dura masa!?
Wata tambayar shine, da yaushe ya daga hannun ya musu nuni da kar su bashi tsimin? Kafin su bada ko? A ruwayar ance; ‘Yayin da ya farka.’ Ya farka daga mene? Kenan da suka bashi ya suma ne ko? Sai bayan da ya farfado sannan yace kar wani ko wata dake dakin su fita face Abbas, domin shi bai san abin da suka kulla ba. Ance Abbas ya shigo ne a lokacin, bashi suka durawa Annabi tsimin.
An kawo irin wannan hadisin har ila yau lamba ta 5712 a cikin Sahihul Bukhari, Kitabud Dibbu, Babul Ludud. Har ila yau, an kuma kawo irin Hadisin a Babin Diyya, Babin ‘Iza asaba kaumin…’ Hadisi na 6897. Kai, ka duba Babin Kisasi tsakanin mace da namiji a karkashin littafin Diyya, za ka ga irin wanna Hadisin na cewa wasu daga matan Manzon Allah (S) sun dura masa abin da suka kira magani alhali yana musu kashedi akan kar su dura masa. Yana nan a hadisi na 6889. Ko me yasa Imamu Bukhari ya kawo wannan Hadisin a babin Kisasin Oho?
To, duk ma ba wadannan ba. Wai me yasa Imamu Bukhari bai karishe mana hadisin ba mu ji yadda ta kaya. Da Manzon Allah (S) yace dole kowacce ta sha ko basu sha ba? Da ya kamata a karishe mana ace kowacce bata fita daga dakin ba sai da aka dura mata. Idan an yi hakan. Ko a nan din ma an saba umurnin Manzon Allah (S) ne?
Muna magana ne da gaskiya. Kuma muna cewa, gaskiyar magana mutane kar su bari a kunkume su a daji. Ya kamata su shigo gari. Mu gane cewa, gaskiyar magana fa wasu da ke kusa da Manzon Allah (S) sun cutar da shi. Kuma ba sau daya ko biyu ba kawai, so da dama suna saba umurninsa ne. Yasha yace ku bani, suce ba za su bada ba. Yace kar ku bani kuma su bashi din. Ya yi su kushe. Ya ki yi su ce don me bai yi ba. Ba kuma ta yadda zai yiwu wadannan da a zahiri suke wa Annabi (S) hakan, mun sani kuma ya zama wai a wajensu za mu karbi addini.
Za mu karbi addininmu ne a wajen wadannan shugabanni goma sha biyun da Manzon Allah (s) yace za su kasance a bayansa. Kamar yadda ya zo a cikin Sahihul Bukhari, Hadisi na 7222 da na 7223, daga Jabir Dan Samura, yace; Na ji Annabi (S) yana cewa: “Shugabanni goma sha biyu za su kasance.” Sai ya fadi wata kalma da ban ji me yace ba. Sai babana yace, Annabi (S) yace ne; “Dukkansu daga Quraishu suke.” Mun yi Imani da cewa wadannan 12 din sune halifofin Manzon Allah (S), kuma na farkonsu shine Imam Ali (AS) na karshensu Imam Mahdi (AS).
Ina kara jajantawa al’ummar Musulmi dangane da zagayowar ranar Shahadar Manzon Allah (S). Insha Allah za mu dora da rubutunmu gwargadon yadda hali ya bada.
Tsage Gaskiya (3)
Daga Saifullahi M Kabir
A rubutun da ya gabata na yi kokarin tunatar da mu yadda suka canza koyarwar Manzon Allah (S) da gangan, sakamakon kin bari ya rubuta mana wannan shiriyar. Ko da yake duk da sun hana rubutun, Manzon Allah (S) ya fada mana abin da zai rubuta, cewa: Bayansa mu yi riko da Iyalan gidansa tsarkaka ne.
Wani abu da ya kamata mu waiwaya a nan shine, shin sun bi iyalan gidan nasa a bayansa? Shin sun yi riko da iyalan gidan nashi a bayan wafatinsa ne?
Babba a cikin iyalan gidan Manzon Allah (S) it ace Maulatana Sayyida Zahra (SA). Wannan da a hadisi na 3714 a cikin Sahihul Bukhari, aka ruwaito daga Abu Walid, da isnadinsa zuwa ga Miswari Dan Makhrama yace: Manzon Allah (S) yace: “Fatima tsokar jikina ce, duk wanda ya fusata ta, ni ya fusata.” To, sun fusata Fatima (S) din ne, tare da cewa sun san cewa fusata ta fusata Annabi (S) ne. Suna sane da cewa kuma duk wanda Fatima (S) ta yi fushi da shi Manzon Allah (S) na fushi da shi. Kuma fushin Manzon Allah (S) fushin Allah (T) ne.
Malam, bance ka dauko littafin Alkafiy ba, ballantana k ace ai Shi’a ne. Ban kuma ce ka dauko Imama Was- Siyasa ba, bare kace ai bai ingata ba. Wannan Sahihul Bukhari din da ke hannunka nake so ka sake budewa ka je kan Hadisi na 4240 da na 4241, za ka ga ruwaya daga A’isha matar Annabi (S), tace: Fatima ‘yar Annabi (SA) ta aikawa Abubakar da sako tana mai tambayarsa a kan abin da ta gada daga Manzon Allah (S) na daga abin da Allah ya bashi a Madina da Fadak, da kuma abin da ya yi saura daga Kumusin Khaibar. Sai Abubakar yace mata; Ai Manzon Allah (S) yace: ‘Ba a gadonmu! Abin da muka bari sadaka ne…’
Ta cigaba da cewa: Sai Abubakar yaki yaba Fatima komai. Sai Fatima ta yi sabani da Abubakar a kan wannan, (cewa babanta yace ba a gadonsu), sai ta kaurace masa, har ta yi wafati bata sake masa magana ba. Kuma ta rayu ne bayan wafatin babanta da watanni shida. A yayin da ta yi wafati, mijinta Ali ne ya birne ta a cikin dare. Ba a gabatar da Abubakar gareta ba kuma bai sallaci gawarta ba.”
Wannan kunga Nana A’isha ke tabbatar da cewa Fatima ‘yar Annabi (S), wacce Allah ke fushi da fushinta, yake yarda da yardarta ta yi kauracewa Abubakar har ta koma ga Allah bata masa magana. Wato tsawon rabin shekara tana mai kaurace masa. Ba ma kawai hakan ba, har ta yi wafati ta bar wasicci ga mijinta akan ya bizne ta ne da daddare kar ya bari Abubakar ko Umar su sallaci gawarta. Don haka Imam Ali (AS) ya ma tsokar Annabi (S) janaza ya bizne ta a cikin duhun dare ba tare da sun sani din ba.
Wannan ke tabbatar maka da cewa, Sayyida Zahra (S) har ta koma ga Allah tana mai fushi da Abubakar ne, ba kawai da ta yi wafati shikenan ba. A’a, har yau din nan da muke ciki bata bar fushi da shi ba. Kuma kamar yadda aka ruwaito ta fada a wani waje, cewa sai ta kai karansa gaban Manzon Allah (S) a gaban zatin Allah (T) akan cewa sun fusata ta, kuma sun danne hakkinta.
Haka ma a Hadisi na 6726 a Bukharin, aka ce bayan da ta nema yace mata Manzon Allah (S) yace ba a gadonsu… Sai Sayyida Fatima (S) ta kauracewa Abubakar, ba ta sake masa magana ba har ta koma ga Allah (T).
Duk wadannan kila kace gaba daya hadisan guda uku da na kawo ba a ce ta yi fushi da shi ba, an ce ta kaurace masa ne. Sai nace idan ka kasa bambance ma’anar kauracewa mutum da kuma yin fushi da mutum, ka koma baya zuwa ga Hadisi na 3093, an kawo cewa, da Abubakar yace wa Fatima (SA), ai Manzon Allah (S) yace; “Ba a gadonmu, duk abin da muka bari sadaka ne.” Sai Fatima ‘yar Manzon Allah (S) ta yi fushi, ta kaurace ma Abubakar. Bata gushe ba tana mai kaurace masa har ta yi wafati. Kuma ta rayu ne bayan wafatin mahaifinta da watanni shida.
Wasu sukan ce to ai Abubakar ya ba Sayyida Zahra (SA) uzurinsa na hana ta gonarta ta Fadak da gadonta na Mahaifinta, da cewa wai Annabi (S) yace ba a gadon Annabawa. Sai nace maka ka tausawa zuciyarka mana, ka zamar da ita mai ‘yantacciyar tunani da nazari. Amfanin hankalin da Allah yam aka ya bambanta ka da dabba shine ka iya gane hankali da rashin hankali ko da rainin hankali.
Manzon Allah (S) da ya san cewa zai koma ga Allah, kuma ‘yarsa kwara daya da zai bari a Duniya ita ce Fatima (SA), kuma tana da hakkin ya sanar da ita duk wani abu da ya shafeta daga gare shi, don Allah zai yiwu Manzon nan ya tafi ya san ba za a gaje shi ba amma ba zai fadawa wannan ‘yar tasa kwara daya ba? Zai yiwu ya zama ya san cewa ba makawa za ta nemi ta gaje shi, amma sai ya kasa sanar da ita cewa kar ta nemi gadonsa abin da ya bari sadaka ne?
Ka budo Hadisi na 3715 da na 3716 a cikin Sahihin Bukharin da ke hannunka; A’isha matar Manzon Allah (S) tace, Annabi (S) ya kira ‘yarsa Fatima (SA) a lokacin rashin lafiyar da ya yi wafati a cikinta. Sai ya yi magana (cikin sirri) da ita, sai ta yi kuka. Sai ya kuma kiranta ya yi sirri da ita, sai ta yi dariya.’
A’isha ta cigaba da cewa: Sai na tambaye ta akan wannan sirrikan da ya mata (Bayan wafatin Annabi (S). Sai tace min, “Annabi (S) ya sirranta min cewa zai yi wafati a cikin wannan rashin lafiyar da ya yi wafati a cikinsa. Sai na yi kuka. Sai ya kara sirranta min cewa ni ce farkon wacce zan bi shi a cikin iyalan gidansa. Sai na yi dariya.”
Ashe in har Manzon Allah (S) zai yi wannan sirrin da ‘yarsa, zai mance ya fada mata cewa kuma ba za ki gajeni ba, har sai ta ji a wajen Abubakar, wanda dama kuma kaf cikin sahabbai shi kadai ne kawai ya san da wannan maganar cewa ba a gadon? Ko kana so kace min wannan da Allah (T) ya sanya yardarta da fushinta su zama nashi za ta nemi hakkinta ne bisa karya da zalunci? Kana so kace Sayyida Zahra ta san bata da gadon Manzon Allah (S) amma ta nema a bata? Har ta yi fushi akan hanata da aka yi?
Na sani, nan wajen ma muhalli ne na rabuwar ra’ayi tsakanin Musulmi, akwai masu ra’ayin cewa Abubakar ke da gaskiya kila kai kana cikinsu, amma ni da masu irin ra’ayina shine tsokar jikin Manzon Allah (S) ce mai gaskiya, kuma ita ke kan daidai, kuma fushin da ta yi da Abubakar ya tabbata a gare shi har abada. Domin da shaidar ‘yarsa A’isha ta ce har Sayyida Zahra (SA) ta koma ga Allah bata dena fushi da shi ba. Kuma fushinta fushin babanta ne, fushin babanta fushin Allah (T) ne. Don haka duk mumini wajibinsa ne ya yi fushi da wanda Allah ke fushi da shi!
Da sannu za mu zo da bayani a kan yadda kiri da muzu suka shure Imam Ali (AS) daga Khalifancin Manzon Allah (S), suka dauki sarauta, alhali Manzon Allah da kansa a bisa ingantattun ruwayoyi ya tabbatar musu da cewa Imam Ali (AS) ne halifansa a bayansa. Har ma nake cewa, wai ko son zama shugabanni da kuma bukatuwarsu ga cinye dukiyar Annabi (S) da sunan sadaka ne yasa aka kosa Manzon Allah (S) ya bar duniya, har ma aka ruwaito a cikin Sahihin Bukhari wasu na bada labarin cewa sun durawa Annabi magani alhali yana hana su? Suka ki hanuwa, suka dura masa, har ya suma, yayin da ya farka yace ashe ban hana ku akan kar ku dura min ba? Kar dayarku ta bar wajen nan face ta durawa kanta, in banda Abbas, domin shi bai san abin da kuka kulla ba!
Hadisai ne a cikin Sahihul Bukhari, insha Allah za mu biyo ta wajen a cigaban nasarinmu. Amma ina cewa ne, mutum ya sani, idan zai ma Manzon Allah (S) tawaye da gangan, to ya bi wadanda suka yi hannun riga da koyarwar Manzon Allah (S). Kuma abin da nake fada bai taba zama zagi ba, ina fadan zahiri ne, kuma gaskiya. Kuma dai Allah ya nufa ya zama yanzu mutane sun san gaskiya din ne, in suka ga dama su bi, in suka ga hagu kuma su cigaba da bin son zukatansu.
A wannan ‘issue’ din, muna bayan Sayyida Fatima (S) ‘Yar Annabi (S), kamar yadda a ‘issue’ din hana abin rubutu muke bayan Manzon Allah (S). Kai a ‘yar wanne kake?
Zan cigaba insha Allah.
A rubutun da ya gabata na yi kokarin tunatar da mu yadda suka canza koyarwar Manzon Allah (S) da gangan, sakamakon kin bari ya rubuta mana wannan shiriyar. Ko da yake duk da sun hana rubutun, Manzon Allah (S) ya fada mana abin da zai rubuta, cewa: Bayansa mu yi riko da Iyalan gidansa tsarkaka ne.
Wani abu da ya kamata mu waiwaya a nan shine, shin sun bi iyalan gidan nasa a bayansa? Shin sun yi riko da iyalan gidan nashi a bayan wafatinsa ne?
Babba a cikin iyalan gidan Manzon Allah (S) it ace Maulatana Sayyida Zahra (SA). Wannan da a hadisi na 3714 a cikin Sahihul Bukhari, aka ruwaito daga Abu Walid, da isnadinsa zuwa ga Miswari Dan Makhrama yace: Manzon Allah (S) yace: “Fatima tsokar jikina ce, duk wanda ya fusata ta, ni ya fusata.” To, sun fusata Fatima (S) din ne, tare da cewa sun san cewa fusata ta fusata Annabi (S) ne. Suna sane da cewa kuma duk wanda Fatima (S) ta yi fushi da shi Manzon Allah (S) na fushi da shi. Kuma fushin Manzon Allah (S) fushin Allah (T) ne.
Malam, bance ka dauko littafin Alkafiy ba, ballantana k ace ai Shi’a ne. Ban kuma ce ka dauko Imama Was- Siyasa ba, bare kace ai bai ingata ba. Wannan Sahihul Bukhari din da ke hannunka nake so ka sake budewa ka je kan Hadisi na 4240 da na 4241, za ka ga ruwaya daga A’isha matar Annabi (S), tace: Fatima ‘yar Annabi (SA) ta aikawa Abubakar da sako tana mai tambayarsa a kan abin da ta gada daga Manzon Allah (S) na daga abin da Allah ya bashi a Madina da Fadak, da kuma abin da ya yi saura daga Kumusin Khaibar. Sai Abubakar yace mata; Ai Manzon Allah (S) yace: ‘Ba a gadonmu! Abin da muka bari sadaka ne…’
Ta cigaba da cewa: Sai Abubakar yaki yaba Fatima komai. Sai Fatima ta yi sabani da Abubakar a kan wannan, (cewa babanta yace ba a gadonsu), sai ta kaurace masa, har ta yi wafati bata sake masa magana ba. Kuma ta rayu ne bayan wafatin babanta da watanni shida. A yayin da ta yi wafati, mijinta Ali ne ya birne ta a cikin dare. Ba a gabatar da Abubakar gareta ba kuma bai sallaci gawarta ba.”
Wannan kunga Nana A’isha ke tabbatar da cewa Fatima ‘yar Annabi (S), wacce Allah ke fushi da fushinta, yake yarda da yardarta ta yi kauracewa Abubakar har ta koma ga Allah bata masa magana. Wato tsawon rabin shekara tana mai kaurace masa. Ba ma kawai hakan ba, har ta yi wafati ta bar wasicci ga mijinta akan ya bizne ta ne da daddare kar ya bari Abubakar ko Umar su sallaci gawarta. Don haka Imam Ali (AS) ya ma tsokar Annabi (S) janaza ya bizne ta a cikin duhun dare ba tare da sun sani din ba.
Wannan ke tabbatar maka da cewa, Sayyida Zahra (S) har ta koma ga Allah tana mai fushi da Abubakar ne, ba kawai da ta yi wafati shikenan ba. A’a, har yau din nan da muke ciki bata bar fushi da shi ba. Kuma kamar yadda aka ruwaito ta fada a wani waje, cewa sai ta kai karansa gaban Manzon Allah (S) a gaban zatin Allah (T) akan cewa sun fusata ta, kuma sun danne hakkinta.
Haka ma a Hadisi na 6726 a Bukharin, aka ce bayan da ta nema yace mata Manzon Allah (S) yace ba a gadonsu… Sai Sayyida Fatima (S) ta kauracewa Abubakar, ba ta sake masa magana ba har ta koma ga Allah (T).
Duk wadannan kila kace gaba daya hadisan guda uku da na kawo ba a ce ta yi fushi da shi ba, an ce ta kaurace masa ne. Sai nace idan ka kasa bambance ma’anar kauracewa mutum da kuma yin fushi da mutum, ka koma baya zuwa ga Hadisi na 3093, an kawo cewa, da Abubakar yace wa Fatima (SA), ai Manzon Allah (S) yace; “Ba a gadonmu, duk abin da muka bari sadaka ne.” Sai Fatima ‘yar Manzon Allah (S) ta yi fushi, ta kaurace ma Abubakar. Bata gushe ba tana mai kaurace masa har ta yi wafati. Kuma ta rayu ne bayan wafatin mahaifinta da watanni shida.
Wasu sukan ce to ai Abubakar ya ba Sayyida Zahra (SA) uzurinsa na hana ta gonarta ta Fadak da gadonta na Mahaifinta, da cewa wai Annabi (S) yace ba a gadon Annabawa. Sai nace maka ka tausawa zuciyarka mana, ka zamar da ita mai ‘yantacciyar tunani da nazari. Amfanin hankalin da Allah yam aka ya bambanta ka da dabba shine ka iya gane hankali da rashin hankali ko da rainin hankali.
Manzon Allah (S) da ya san cewa zai koma ga Allah, kuma ‘yarsa kwara daya da zai bari a Duniya ita ce Fatima (SA), kuma tana da hakkin ya sanar da ita duk wani abu da ya shafeta daga gare shi, don Allah zai yiwu Manzon nan ya tafi ya san ba za a gaje shi ba amma ba zai fadawa wannan ‘yar tasa kwara daya ba? Zai yiwu ya zama ya san cewa ba makawa za ta nemi ta gaje shi, amma sai ya kasa sanar da ita cewa kar ta nemi gadonsa abin da ya bari sadaka ne?
Ka budo Hadisi na 3715 da na 3716 a cikin Sahihin Bukharin da ke hannunka; A’isha matar Manzon Allah (S) tace, Annabi (S) ya kira ‘yarsa Fatima (SA) a lokacin rashin lafiyar da ya yi wafati a cikinta. Sai ya yi magana (cikin sirri) da ita, sai ta yi kuka. Sai ya kuma kiranta ya yi sirri da ita, sai ta yi dariya.’
A’isha ta cigaba da cewa: Sai na tambaye ta akan wannan sirrikan da ya mata (Bayan wafatin Annabi (S). Sai tace min, “Annabi (S) ya sirranta min cewa zai yi wafati a cikin wannan rashin lafiyar da ya yi wafati a cikinsa. Sai na yi kuka. Sai ya kara sirranta min cewa ni ce farkon wacce zan bi shi a cikin iyalan gidansa. Sai na yi dariya.”
Ashe in har Manzon Allah (S) zai yi wannan sirrin da ‘yarsa, zai mance ya fada mata cewa kuma ba za ki gajeni ba, har sai ta ji a wajen Abubakar, wanda dama kuma kaf cikin sahabbai shi kadai ne kawai ya san da wannan maganar cewa ba a gadon? Ko kana so kace min wannan da Allah (T) ya sanya yardarta da fushinta su zama nashi za ta nemi hakkinta ne bisa karya da zalunci? Kana so kace Sayyida Zahra ta san bata da gadon Manzon Allah (S) amma ta nema a bata? Har ta yi fushi akan hanata da aka yi?
Na sani, nan wajen ma muhalli ne na rabuwar ra’ayi tsakanin Musulmi, akwai masu ra’ayin cewa Abubakar ke da gaskiya kila kai kana cikinsu, amma ni da masu irin ra’ayina shine tsokar jikin Manzon Allah (S) ce mai gaskiya, kuma ita ke kan daidai, kuma fushin da ta yi da Abubakar ya tabbata a gare shi har abada. Domin da shaidar ‘yarsa A’isha ta ce har Sayyida Zahra (SA) ta koma ga Allah bata dena fushi da shi ba. Kuma fushinta fushin babanta ne, fushin babanta fushin Allah (T) ne. Don haka duk mumini wajibinsa ne ya yi fushi da wanda Allah ke fushi da shi!
Da sannu za mu zo da bayani a kan yadda kiri da muzu suka shure Imam Ali (AS) daga Khalifancin Manzon Allah (S), suka dauki sarauta, alhali Manzon Allah da kansa a bisa ingantattun ruwayoyi ya tabbatar musu da cewa Imam Ali (AS) ne halifansa a bayansa. Har ma nake cewa, wai ko son zama shugabanni da kuma bukatuwarsu ga cinye dukiyar Annabi (S) da sunan sadaka ne yasa aka kosa Manzon Allah (S) ya bar duniya, har ma aka ruwaito a cikin Sahihin Bukhari wasu na bada labarin cewa sun durawa Annabi magani alhali yana hana su? Suka ki hanuwa, suka dura masa, har ya suma, yayin da ya farka yace ashe ban hana ku akan kar ku dura min ba? Kar dayarku ta bar wajen nan face ta durawa kanta, in banda Abbas, domin shi bai san abin da kuka kulla ba!
Hadisai ne a cikin Sahihul Bukhari, insha Allah za mu biyo ta wajen a cigaban nasarinmu. Amma ina cewa ne, mutum ya sani, idan zai ma Manzon Allah (S) tawaye da gangan, to ya bi wadanda suka yi hannun riga da koyarwar Manzon Allah (S). Kuma abin da nake fada bai taba zama zagi ba, ina fadan zahiri ne, kuma gaskiya. Kuma dai Allah ya nufa ya zama yanzu mutane sun san gaskiya din ne, in suka ga dama su bi, in suka ga hagu kuma su cigaba da bin son zukatansu.
A wannan ‘issue’ din, muna bayan Sayyida Fatima (S) ‘Yar Annabi (S), kamar yadda a ‘issue’ din hana abin rubutu muke bayan Manzon Allah (S). Kai a ‘yar wanne kake?
Zan cigaba insha Allah.
Tsage Gaskiya (2)
Daga Saifullahi M Kabir
A rubutun da ya gabata, idan mutum yana biye, zai ga cewa mun kawo sabani mai ban takaici da Umar dan Khaddabi ya haifar ga Sahabbai a gaban Manzon Allah (S) a ranar Alhamis din 24 ga Safar, shekara ta 11bh. Wanda wannan sabanin, wanda ya biyo bayan hana Manzon Allah (S), abin rubutu, shi ya jefa al’ummar nan cikin rudu da bin bata, da kauracewa hakikar shiriya. Domin Manzon Allah (S) yace ne; “Zan rubuta muku abin da in kuka yi riko da shi ba za ku taba bata ba har abada.” Kenan idan ba a yi riko da shi ba za a bace. To ina kuma ga ma ba a bari an rubuta din ba? To kun ga sai Umar yace ba za a bayar ba. A kyale Annabi zafin ciwo ke cinsa, ko ma kamar yadda ya zo a wata ruwayar, yace ne Annabi ya fita daga hayyacinsa, littafin Allah ya wadatar da su
Don haka nake cewa, wannan hana Annabi (S) ya rubuta Hadisi mai muhimmanci wanda yake dauke da wasiyar shiriya ta dindindin, ta tabbatar maka da cewa wanda ya hana din da wanda ya goyi bayan hanawan, dukkansu wasu mutane ne masu boyayyun al’amari a zukatansu. Wato ina cewa ne, ya kamata ka yi tunani, me yasa Umar zai tsaya tsayin-daka yace ba a isa a ba Annabi abin rubutu a wanan lokacin da ya nema ba? Anya zai zama haka kawai ne ba wani abin shi da wadanda suka goyi bayansa a wajen suke gudu ba? Mene ne wannan abin? Muna da bukatar mu ji shi ko?
Kar a manta, hadisan da muka kawo a rubutun da ya gabata dangane da jayayyar Umar ga Annabi (S) gaba daya daga littafin Sahihin Bukhari ne, mun kawo Hadisi na 114 da na 3053 da 4431 da 4432 da 5669 da na 7366. Allah ya so ya zama wannan batun bai buya ga al’ummar Muhammad (S) ba, cewa Umar dan Khaddabi ne ya shiga tsakanin shiriyarsu da Mai shiryarwa. Kamar yadda Ibn Abbas (RA) ke cewa: “Mafi munin abin bakin ciki shine abin da ya shiga tsakanin Manzon Allah (S) da rubutunsa na shiriya.” Kuma ba komai bane wannan abin da ya shiga tsakanin face Umar din da ya hana Annabi (S) da wadanda suka goyi bayansa.
Kar kace ina ta cewa Umar, Umar, Umar bance Sayyadina ko abin da ya kamaci haka ba. Ina magana ne akan shi a gaban Manzon da babu wani Sayyid a gabansa a duk talikai. Ina magana ne akan Umar a yayin da ya sabawa Shugaba (S) da gangan, saboda abin da suka boye a zukatansu na cewa ba su so ya zama shiriya ta tabbata a cikin wannan al’ummar ba, sun ma kansu alkawarin ba makawa sai sun canza duk wani abu da yake daidai da yadda Annabi (S) ya zo da shi. Kamar yadda kuma sun yi iyakar kokarinsu wajen ganin sun canza addinin nan a bayan Manzon Allah (S).
Inda za ka san cewa hana Annabi yin rubutun nan ya jawo halakar da yawa daga ‘yan wannan al’ummar, ka shiga cikin Sahihul Bukhari ka binciko hadisi mai lamba ta 530, daga Abu Rawwada, dan uwan Abdul’azeez, yace; Na ji Zuhri yana cewa: Wata rana na shiga wajen Anas Dan Malik (hadimin Manzon Allah (S) a garin Dimashk, sai na tarar da shi yana kuka. Sai nace da shi me yasa kake kuka? Sai yace min; ‘Ban san wani abu daga abubuwan da na riska a lokacin Manzon Allah (S) da yanzu yake nan (a yadda yake) ba in banda wannan Sallar, kuma ita ma sallar an canza ta!’
Innalillahi wa inna ilaihi raji’un! Ku duba ku gani, Sahabi ke kuka, shekara kasa da 30 daga wafatin Manzon Allah (S), amma yana ba da tabbacin cewa duk wani abu da Manzon Allah (S) ya koyar na ibada, hatta sallah da ake yinta kullum sai da aka canza ta daga irin wacce Manzon Allah (S) yake yi kuma ya koyar. Malam, ina kuma ga kai yanzu da kake cikin shekara ta kusan 1330 bayan wafatin Manzon Allah (S)?
Hadisi na 529 a cikin Buharin dai, daga Anas din, yace; “Ban san wani abu da yake a zamanin Manzon Allah (S) wanda yake a yanzu (a yadda yake a da din) ba.” Sai aka ce da shi, ga Sallah. Sai yace; “Ashe ba ku canza abin da kuka canza a cikinta ba!?”
Masu tambayar nashi fa Sahabbai ne suma, sun ga Annabi (S), sun yi Sallah tare da Annabi (S), amma an wayi gari a kasa da shekaru 30 da wafatin Annabi (S) halifofin da suka mulki al’ummar Annabi sun tilasta canza wasu abubuwa daga yadda suke a hakika. Muna iya cewa sun canza koyarwar Manzon Allah (S) zuwa abin da suka ga dama. Sai aka wayi gari Sahabbai ma sun dena yin irin ibadar Manzon Allah (S). Ina kuma ga tabi’ai da mabiyansu har zuwa yau da muke?
Kun ga shiriyar da Annabi ya so ya rubuta din nan wacce da Umar da wasu daga Sahabbai sun bari ya rubuta mana, kuma suka bar al’umma suka bi, da ba a kai ga wannan baganniyar ba. Amma da suka hana, sai ya zama Manzon Allah (S) ya fadi wasiyyar da baki, nan ma kamar yadda suka kawo a cikin Hadisi na 4431 a cikin Bukhari, sai aka ce wai Annabi (S) ya yi wasiyya da abubuwa guda uku ne, aka fadi guda biyu aka ce wai an mance wasiyya ta uku da ya yi.
Har mukan ce, don Allah kar a mai da mu wawaye mana. Ace Manzon Allah (S) da kansa ya yi wasiyya da abubuwa kwara uku kacal, amma duk wadanda suke wajen ace guda biyu suka iya tunawa sun mance na karshen? Ashe da ace Annabi (S) ya yi wasiyya da abubuwa 313 ne bai zama wajibi a kiyaye su ba? Ballantana guda uku kacal!? Da sannu za mu zo da bayanin wasiyyar da Annabi (S) ya yi ta ukun da aka ce an mance ta. Wacce ita ce ya so ya rubuta ta ma don tabbatarwa. Wannan wasiyyar kuwa itace riko da Imam Ali (AS) a bayansa, domin shi ba zai taba canza addininsa ba har abada! Don haka riko da shi da koyi da shi a bayan Manzon Allah (S) ne kawai shiriyar da za ta wanzar ma da mutum imaninsa har abada.
Ba ku ji ba? Har a lokacin da aka canza komai din, Sahabban Annabi (S) suka koma yin ibada irin wanda sarakuna suka amince da su yi. Imam Ali (AS) ne da kadan din da suke bi shi suka cigaba da yin duk wata ibada irin yadda Annabi (S) ya yi.
Hadisi na 784 a cikin Bukhari, daga Imrana bin Husyn, yace: Mun yi salla tare da Aliyu dan Abudalib (RA) a garin Basra. Sai muka ce: Wannan mutumin (wato Imam Ali) ya tuna mana da irin sallar da muke yi tare da Manzon Allah (S). A nan muka tuna cewa Manzon Allah (S) fa idan yana sallah, yana yin kabbara a duk lokacin da ya dago ko ya duka.”
Hadisi na 786 da na 826 duk a Sahihul Bukhari din, daga Mudarrif dan Abdullahi, yace; Mun yi salla a bayan Aliyu Dan Abudalib (RA) ni da Imrana Dan Husyn. (Ali) ya kasance idan zai yi sujada yana yin kabbara, idan ya dago daga sujada yana yin kabbara, idan zai tashi daga raka’a ta biyu yana kabbara. A yayin da muka idar da sallar. Sai Imran Dan Husyn ya kama hannuna yace; Hakika wannan (suna nufin Imam Ali) ya tuna min da sallar Manzon Allah (S). Ko kuma yace ne; “Hakika ya yi mana irin sallar Manzon Allah (S).”
Ya kai ma’abocin neman shiriya, don Allah ka yi nazari a karan kanka akan wannan al’amarin. Nan fa dukkansu da mai sallar da masu bin sallar Sahabban Manzon Allah (S) ne, sun yi sallah a bayansa, amma kalli yadda mafiya yawansu suka mance ma da yadda Annabi (S) yake Sallah sai da suka gani Imam Ali (AS) yana yi, sannan suka tuna cewa ashe fa ga yadda Annabi (S) yake yin Sallarsa. To, don Allah, da sallar wa suke yi kenan?
Malam, wadannan sune fa wadanda suka ruwaitowa al’ummar Annabi addinin Annabi. Dubi yadda har sallah ma su kansu ba suna yin irin na Annabin (S) bane, ina kuma ga kai yanzu? Amma kun ga sun ba da shaidar Imam Ali (AS) na yin salla ne irin yadda Annabi (S) ke yi ko? To kuma don me za ka bi wadanda suka dena yin irin ibadar Manzon Allah (S) ka bar wanda yake yin irin na Annabi (S)?
Ashe za mu zama ababen zargi a wajen mai hankali, idan muka ce ba za mu bi wadanda suka hana Annabi ya rubuta mana tabbatacciyar shiriya ba? Idan muka ce mun ki mu koyi addini daga wadanda suka dena yin irin ibadar Manzon Allah (S)? Abin mamaki yanzu idan wanda ake kira Shi’a, mabiyin Imam Ali (AS) ya zo yana Sallah, tun daga alwala za ka ga mutane suna nuna shi, suna cewa dubi yadda yake alwala. Malam! An canza addininka ne daga koyarwar Annabi (S), mu kuma muna yin addini da ibada ne irin wanda kofar ilimin Manzon Allah (S) ya ruwaito mana, ‘ya’yansa suka koyar da mu.
Na tsaya wani misali har rubutun nawa ya yi tsawo yau ma. Sai nace gaskiyar magana ni dai bani ba wanda ya yi jayayya da Manzon Allah (S) akan rubuta mana shiriya, wallahi ina fada maka GASKIYA ne cewa ban sonsa, ban kuma goyon bayansa, ina son Annabi (S) ne, kuma ina goyon bayan Annabi (S) ne! Allah ya riga ya tsare; amma wallahi idan da Annabi Adamu, ko Ibraheem ko Isa (AS) waninsu zai sabawa Annabi Muhammad (S) akan wata magana bare umurni, da ba zan bi su ba, b azan so su ba, kuma b azan musu uzuri ba. (Sun kubuta daga aikata hakan), to, ballantana wani da ba ma waliyi bane, bisa shaidar ruwayoyi ma yana cikin Jahilan cikin sahabban Mazon Allah (S) kamar yadda za mu ji a can gaba.
Kuma da sannu za mu ji cewa ba a ranar Alhamis din nan ne kawai ya fara jayayya da Annabi (S) ba, ingantattun ruwayoyi a cikin Sahihul Bukhari sun tabbatar da cewa har cin-kwala (shake) Manzon Allah (S) ya taba yi. Muhammad (S) ne Annabina kuma shine abin riko na.
Za mu cigaba insha Allah.
A rubutun da ya gabata, idan mutum yana biye, zai ga cewa mun kawo sabani mai ban takaici da Umar dan Khaddabi ya haifar ga Sahabbai a gaban Manzon Allah (S) a ranar Alhamis din 24 ga Safar, shekara ta 11bh. Wanda wannan sabanin, wanda ya biyo bayan hana Manzon Allah (S), abin rubutu, shi ya jefa al’ummar nan cikin rudu da bin bata, da kauracewa hakikar shiriya. Domin Manzon Allah (S) yace ne; “Zan rubuta muku abin da in kuka yi riko da shi ba za ku taba bata ba har abada.” Kenan idan ba a yi riko da shi ba za a bace. To ina kuma ga ma ba a bari an rubuta din ba? To kun ga sai Umar yace ba za a bayar ba. A kyale Annabi zafin ciwo ke cinsa, ko ma kamar yadda ya zo a wata ruwayar, yace ne Annabi ya fita daga hayyacinsa, littafin Allah ya wadatar da su
Don haka nake cewa, wannan hana Annabi (S) ya rubuta Hadisi mai muhimmanci wanda yake dauke da wasiyar shiriya ta dindindin, ta tabbatar maka da cewa wanda ya hana din da wanda ya goyi bayan hanawan, dukkansu wasu mutane ne masu boyayyun al’amari a zukatansu. Wato ina cewa ne, ya kamata ka yi tunani, me yasa Umar zai tsaya tsayin-daka yace ba a isa a ba Annabi abin rubutu a wanan lokacin da ya nema ba? Anya zai zama haka kawai ne ba wani abin shi da wadanda suka goyi bayansa a wajen suke gudu ba? Mene ne wannan abin? Muna da bukatar mu ji shi ko?
Kar a manta, hadisan da muka kawo a rubutun da ya gabata dangane da jayayyar Umar ga Annabi (S) gaba daya daga littafin Sahihin Bukhari ne, mun kawo Hadisi na 114 da na 3053 da 4431 da 4432 da 5669 da na 7366. Allah ya so ya zama wannan batun bai buya ga al’ummar Muhammad (S) ba, cewa Umar dan Khaddabi ne ya shiga tsakanin shiriyarsu da Mai shiryarwa. Kamar yadda Ibn Abbas (RA) ke cewa: “Mafi munin abin bakin ciki shine abin da ya shiga tsakanin Manzon Allah (S) da rubutunsa na shiriya.” Kuma ba komai bane wannan abin da ya shiga tsakanin face Umar din da ya hana Annabi (S) da wadanda suka goyi bayansa.
Kar kace ina ta cewa Umar, Umar, Umar bance Sayyadina ko abin da ya kamaci haka ba. Ina magana ne akan shi a gaban Manzon da babu wani Sayyid a gabansa a duk talikai. Ina magana ne akan Umar a yayin da ya sabawa Shugaba (S) da gangan, saboda abin da suka boye a zukatansu na cewa ba su so ya zama shiriya ta tabbata a cikin wannan al’ummar ba, sun ma kansu alkawarin ba makawa sai sun canza duk wani abu da yake daidai da yadda Annabi (S) ya zo da shi. Kamar yadda kuma sun yi iyakar kokarinsu wajen ganin sun canza addinin nan a bayan Manzon Allah (S).
Inda za ka san cewa hana Annabi yin rubutun nan ya jawo halakar da yawa daga ‘yan wannan al’ummar, ka shiga cikin Sahihul Bukhari ka binciko hadisi mai lamba ta 530, daga Abu Rawwada, dan uwan Abdul’azeez, yace; Na ji Zuhri yana cewa: Wata rana na shiga wajen Anas Dan Malik (hadimin Manzon Allah (S) a garin Dimashk, sai na tarar da shi yana kuka. Sai nace da shi me yasa kake kuka? Sai yace min; ‘Ban san wani abu daga abubuwan da na riska a lokacin Manzon Allah (S) da yanzu yake nan (a yadda yake) ba in banda wannan Sallar, kuma ita ma sallar an canza ta!’
Innalillahi wa inna ilaihi raji’un! Ku duba ku gani, Sahabi ke kuka, shekara kasa da 30 daga wafatin Manzon Allah (S), amma yana ba da tabbacin cewa duk wani abu da Manzon Allah (S) ya koyar na ibada, hatta sallah da ake yinta kullum sai da aka canza ta daga irin wacce Manzon Allah (S) yake yi kuma ya koyar. Malam, ina kuma ga kai yanzu da kake cikin shekara ta kusan 1330 bayan wafatin Manzon Allah (S)?
Hadisi na 529 a cikin Buharin dai, daga Anas din, yace; “Ban san wani abu da yake a zamanin Manzon Allah (S) wanda yake a yanzu (a yadda yake a da din) ba.” Sai aka ce da shi, ga Sallah. Sai yace; “Ashe ba ku canza abin da kuka canza a cikinta ba!?”
Masu tambayar nashi fa Sahabbai ne suma, sun ga Annabi (S), sun yi Sallah tare da Annabi (S), amma an wayi gari a kasa da shekaru 30 da wafatin Annabi (S) halifofin da suka mulki al’ummar Annabi sun tilasta canza wasu abubuwa daga yadda suke a hakika. Muna iya cewa sun canza koyarwar Manzon Allah (S) zuwa abin da suka ga dama. Sai aka wayi gari Sahabbai ma sun dena yin irin ibadar Manzon Allah (S). Ina kuma ga tabi’ai da mabiyansu har zuwa yau da muke?
Kun ga shiriyar da Annabi ya so ya rubuta din nan wacce da Umar da wasu daga Sahabbai sun bari ya rubuta mana, kuma suka bar al’umma suka bi, da ba a kai ga wannan baganniyar ba. Amma da suka hana, sai ya zama Manzon Allah (S) ya fadi wasiyyar da baki, nan ma kamar yadda suka kawo a cikin Hadisi na 4431 a cikin Bukhari, sai aka ce wai Annabi (S) ya yi wasiyya da abubuwa guda uku ne, aka fadi guda biyu aka ce wai an mance wasiyya ta uku da ya yi.
Har mukan ce, don Allah kar a mai da mu wawaye mana. Ace Manzon Allah (S) da kansa ya yi wasiyya da abubuwa kwara uku kacal, amma duk wadanda suke wajen ace guda biyu suka iya tunawa sun mance na karshen? Ashe da ace Annabi (S) ya yi wasiyya da abubuwa 313 ne bai zama wajibi a kiyaye su ba? Ballantana guda uku kacal!? Da sannu za mu zo da bayanin wasiyyar da Annabi (S) ya yi ta ukun da aka ce an mance ta. Wacce ita ce ya so ya rubuta ta ma don tabbatarwa. Wannan wasiyyar kuwa itace riko da Imam Ali (AS) a bayansa, domin shi ba zai taba canza addininsa ba har abada! Don haka riko da shi da koyi da shi a bayan Manzon Allah (S) ne kawai shiriyar da za ta wanzar ma da mutum imaninsa har abada.
Ba ku ji ba? Har a lokacin da aka canza komai din, Sahabban Annabi (S) suka koma yin ibada irin wanda sarakuna suka amince da su yi. Imam Ali (AS) ne da kadan din da suke bi shi suka cigaba da yin duk wata ibada irin yadda Annabi (S) ya yi.
Hadisi na 784 a cikin Bukhari, daga Imrana bin Husyn, yace: Mun yi salla tare da Aliyu dan Abudalib (RA) a garin Basra. Sai muka ce: Wannan mutumin (wato Imam Ali) ya tuna mana da irin sallar da muke yi tare da Manzon Allah (S). A nan muka tuna cewa Manzon Allah (S) fa idan yana sallah, yana yin kabbara a duk lokacin da ya dago ko ya duka.”
Hadisi na 786 da na 826 duk a Sahihul Bukhari din, daga Mudarrif dan Abdullahi, yace; Mun yi salla a bayan Aliyu Dan Abudalib (RA) ni da Imrana Dan Husyn. (Ali) ya kasance idan zai yi sujada yana yin kabbara, idan ya dago daga sujada yana yin kabbara, idan zai tashi daga raka’a ta biyu yana kabbara. A yayin da muka idar da sallar. Sai Imran Dan Husyn ya kama hannuna yace; Hakika wannan (suna nufin Imam Ali) ya tuna min da sallar Manzon Allah (S). Ko kuma yace ne; “Hakika ya yi mana irin sallar Manzon Allah (S).”
Ya kai ma’abocin neman shiriya, don Allah ka yi nazari a karan kanka akan wannan al’amarin. Nan fa dukkansu da mai sallar da masu bin sallar Sahabban Manzon Allah (S) ne, sun yi sallah a bayansa, amma kalli yadda mafiya yawansu suka mance ma da yadda Annabi (S) yake Sallah sai da suka gani Imam Ali (AS) yana yi, sannan suka tuna cewa ashe fa ga yadda Annabi (S) yake yin Sallarsa. To, don Allah, da sallar wa suke yi kenan?
Malam, wadannan sune fa wadanda suka ruwaitowa al’ummar Annabi addinin Annabi. Dubi yadda har sallah ma su kansu ba suna yin irin na Annabin (S) bane, ina kuma ga kai yanzu? Amma kun ga sun ba da shaidar Imam Ali (AS) na yin salla ne irin yadda Annabi (S) ke yi ko? To kuma don me za ka bi wadanda suka dena yin irin ibadar Manzon Allah (S) ka bar wanda yake yin irin na Annabi (S)?
Ashe za mu zama ababen zargi a wajen mai hankali, idan muka ce ba za mu bi wadanda suka hana Annabi ya rubuta mana tabbatacciyar shiriya ba? Idan muka ce mun ki mu koyi addini daga wadanda suka dena yin irin ibadar Manzon Allah (S)? Abin mamaki yanzu idan wanda ake kira Shi’a, mabiyin Imam Ali (AS) ya zo yana Sallah, tun daga alwala za ka ga mutane suna nuna shi, suna cewa dubi yadda yake alwala. Malam! An canza addininka ne daga koyarwar Annabi (S), mu kuma muna yin addini da ibada ne irin wanda kofar ilimin Manzon Allah (S) ya ruwaito mana, ‘ya’yansa suka koyar da mu.
Na tsaya wani misali har rubutun nawa ya yi tsawo yau ma. Sai nace gaskiyar magana ni dai bani ba wanda ya yi jayayya da Manzon Allah (S) akan rubuta mana shiriya, wallahi ina fada maka GASKIYA ne cewa ban sonsa, ban kuma goyon bayansa, ina son Annabi (S) ne, kuma ina goyon bayan Annabi (S) ne! Allah ya riga ya tsare; amma wallahi idan da Annabi Adamu, ko Ibraheem ko Isa (AS) waninsu zai sabawa Annabi Muhammad (S) akan wata magana bare umurni, da ba zan bi su ba, b azan so su ba, kuma b azan musu uzuri ba. (Sun kubuta daga aikata hakan), to, ballantana wani da ba ma waliyi bane, bisa shaidar ruwayoyi ma yana cikin Jahilan cikin sahabban Mazon Allah (S) kamar yadda za mu ji a can gaba.
Kuma da sannu za mu ji cewa ba a ranar Alhamis din nan ne kawai ya fara jayayya da Annabi (S) ba, ingantattun ruwayoyi a cikin Sahihul Bukhari sun tabbatar da cewa har cin-kwala (shake) Manzon Allah (S) ya taba yi. Muhammad (S) ne Annabina kuma shine abin riko na.
Za mu cigaba insha Allah.
Tsage Gaskiya (1)
Daga Saifullahi M Kabir
Ina fara wannan rubutu da sunan Ubangijin da ya yi ma AnnabinSa (S) shaida a cikin littafinSa mai tsarki da cewa: “Kuma baya furuci bisa son ransa, face (duk abin da ya fada) wahayi ne aka yi a gare shi.” Allah (T) da yake wasiyya ga Muminai a cikin Alkur’ani da cewa: “Abin da Manzo (S) ya zo muku da shi ku rike shi, kuma abin da ya haneku a kansa ku hanu.”
SalatinKa Allah da na Mala’ikunKa da na Muminai baki-daya, su kara ninkuwa ga wannan Annabin naKa, zababbe, wanda Ka saukar dangane da shi a cikin Alkur’aninKa mai tsarki kana yabonsa da cewa: “Kuma lallai Kai (Annabi) kana bisa dabi'u masu girma.” Ka kuma yi masa garkuwa daga masu jingina masa gushewar hankali, a yayin da Kake cewa: “Kuma sahibinku (Annabi (S) ba mahaukaci bane!”
Muhimmi kuma mafi girman jaje da Ta’aziyya gare ku baki-daya, dangane da zagayowar lokacin Shahadar Manzon Allah Muhammad (S), wanda ya zo a cikin ingantattun ruwayoyi cewa ta kasance ne a ranar 28 ga watan Safar din shekara ta 11 bayan Hijira.
Yau muna 24 ne ga watan Safar, 1439bh. Wanda rana ce da tarihi ba zai taba mancewa da ita, ko ya kyaleta ta rika zuwa tana wucewa ba tare da raya musiba da ambaton bala’in da ta kunsa ba. Domin kuwa a irin wannan ranar ne na 24 ga Safar, 11bh aka shiga tsakanin Annabi (S) da wanzarwa al’ummarsa dauwamammiyar shiriya. A rana mai kamar yau 24 ga Safar ne aka tabbatarwa da Manzon Allah (S) cewa ba za a taba bari shiriyar da ya zo da ita ta wanzu a kan gaba dayan al’ummarsa ba sai ga ‘yan kadan daga cikinsu, wanda muna fatan Allah ya sa muna cikin kadan masu riko da shiriyar nan.
Ranar 24 ga watan Safar, wanda a wancan shekarar ta 11 bayan hijira, ta kasance ranar Alhamis ne, ta kasance ranar da kamar yadda Ibn Abbas (RA) ke siffata ta, da ranar da mafi bakin cikin abin bakin-ciki ya auku.
A yayin da muke magana da al’umma, mu kan yi iyakan kokarinmu wajen ganin mun yi magana da su ne bisa hujja daga littatafan da suka aminta da su, don idan abin mu ce a cikin littafin Allama Majlisi ya kawo cewa, kaza da kaza ne. Ahlussunnah zai ce, ina ruwanmu da tatsuniyar Shi’a!? Amma idan kace ma Ahlussunah Imaminsa Bukhari ya fada a cikin Sahihinsa. Yanzun nan zai ce, Na’am! Me yace? To a nan, duk girma da nauyin maganar, zai yarda da ita, sai dai kawai idan ta saba da son zuciyarsa ta kau da kai daga shiriyar da kake kokarin haska masa a ciki.
Wana yasa na yi kokarin ya zama na yi wannan rubutun ne bisa rinjayar da dogarona ga Hadisan da Imamin Ahlussunah, Bukhari ya kawo su a cikin ingantaccen littafinsa da aka fi sani da Sahihul Bukhari. A yayin da madogarar da ke biye da shi dan’uwansa ne Muslim a cikin Sahihinsa shima. Ina fatan mai karatu zai bude zuciyarsa ne ya yi ta bina tare da karbar gaskiyar da ke cikin wannan rubutun, har i zuwa kashin karshe da ban san ina ne birki na ba.
Ina magana a kan ranar Alhamis, 24 ga Safar, shekara ta 11 bayan hijirar Annabi (S) me ya faru a wannan ranar?
Dauko littafin Sahihul Bukhari, imma wand aka saya da kudinka, ko wand aka gada, ko kuma ma ka aro daga wani a unguwarku, ka bude ka lalubo Hadisi na 4431 da na 4432, bayan duk isnadin da aka jero a karkashin wadannan Hadisai guda biyu wanda ya tuke zuwa ga Abdullahi Ibn Abbas (RA), za ka ga yana cewa:
“Ranar Alhamis! Ko ka san abin da ya faru a ranar Alhamis din? Yace: Itace ranar da rashin lafiyar Annabi (S) ta tsananta. Sai Annabi (S) yace: “Ku kawo min abin rubutu na rubuta muku rubutun da ba za ku taba bata a bayansa ba har abada.”
Na katse hadisin na muku tambaya? Wannan me Manzon Allah (S) ya yi? Kila ku ce min umurni ko? Su wa ya umurta? Kila kace min Sahabban da a gabansu Allah (T) ya saukar da cewa: ‘Abin da Manzo ya zo muku da shi ku rike shi’ ko? Yanzu Annabi (S) ya zo musu da umurnin cewa su bashi abin rubutu. Me ya hau kan duk wadanda suke cikin wajen su yi? Su bi umurnin nan su bashi ko? To sun bashi? Mu cigaba da Hadisin mu ji.
Ibn Abbas yace; Sai suka yi jayayya, kuma bai cancanta su yi jayayya a gaban Annabi (S) ba! Sai suka ce; “Me ya dameku da shi? Ya fita hayyacinsa!” Inna lillahi wa inna ilaihi Raji’un!
To, su waye suka yi jayayyar? A kan me suka yi jayayya? Kuma da wa suka yi jayayya din? Ibn Abbas ya bamu amsar a Hadisi na 5669, a cikin Sahihul Bukhari.
Hadisi na 5669, Hadisin Ibrahim bin Musa da Isinadinsa na mutane 7 wanda ya tuke izuwa ga Abdullahi Dan Abbas (RA), yace: “Yayin da ajali ya fuskato Manzon Allah (S), a dakin akwai mazaje (Sahabbai), daga cikinsu akwai Umar dan Khaddabi, sai Manzon Allah (S) yace; ‘Ku kusantoni (da abin rubutu) na rubuta muku rubutu wanda ba za ku bace ba a bayansa.’ Sai Umar yace: ‘Lallai rashin lafiya ya galabaitar da Annabi, kuma a wajenku akwai Alkur’ani, Littafin Allah ya wadatar da mu!’
Na kara tsayar da mu a nan na nemi karin bayani; Shin Manzon Allah (S) bai san cewa akai Alkur’ani bane yace a bashi abin rubutun ya rubuta wasiyya? Ba a cikin Alkur’ani din ne Allah ya yi ma Muminai umurni da barin wasiyya ba? Ina fadin Allah (T), cewa Manzon Allah (S) baya furuci bisa son ransa, face duk abin da ya fada wahayi ne aka masa? Ashe umurnin Annabi (S) ba abin bi bane a kowane hali? To me yasa Umar ya hana, ya kuma bai yi shiru ba ma har sai da yake fadawa mutane a gaban Annabi cewa Alkur’ani ya ishe su? Basu bukatar shiriyar da Annabi zai rubuta musu kenan?
A cigaban Hadisin, Ibn Abbas yace: (Da Umar ya fadi hakan), Sai mutanen da ke cikin dakin suka samu sabani, (suka rabu gida biyu), suna masu husuma da junansu. Daga cikinsu akwai masu cewa; ‘Ku kawo wa Manzon Allah (S) ya rubuta muku abin da ba za ku bace ba a bayansa.’ Daga cikinsu kuma akwai masu cewa abin da Umar yace. (Wato kar a bayar, zafin ciwo ne ke damun Manzon Allah (S)).
Tambaya; Ashe Allah (T) bai ce; “Baku da zabi (Ku Muminai) idan Allah da ManzonSa suka yi hukunci akan wani al’amari” ba? Yanzu har Manzon Allah (S) yace a bashi, wani yace ba za a bada ba! Ba a da bukata! Littafin Allah ya isa! Kuma Mumini, ace mumininma Sahabi a gaban Annabi ya goyi bayan mai sabawa Annabi din nan, har ya zama akwai bangaren Manzon Allah da bangaren Umar? Wane ne Umar da za ku bi ra’ayinsa ku bar umurnin Manzon Allah, in dai kun yi Imani da Allah da ManzonSa!?
Dan Abbas ya cigaba da cewa: Yayin da wargi da sabaninsu ya yawaita a gaban Manzon Allah (S), sai Annabi (S) yace dasu; ‘Ku tashi daga gareni (ku fice min)!”
A Hadisin aka karkare da cewa, Ubaidullahi yace; Ibn Abbas (RA) ya kasance yana cewa “Mafi girman dukkan abin bakin ciki shine abin da ya katange tsakanin Manzon Allah (S) da ya rubuta musu wannan rubutun, saboda sabaninsu da kuma warginsu.”
Akwai shigen hadisin da ya gabata, hadisi na 7366. Haka ma a Hadisi na 114 a cikin Bukhari din, makamancin wanda ya gabata, Manzon Allah (S) yace musu ne; “Ku fice daga gare ni, domin bai cancanta ku yi jayayya a gabana ba!” Sai Ibn Abbas ya fito, yana cewa: “Mafi bakin cikin abin bakin ciki, shine abin da ya shiga tsakanin Manzon Allah (S) da rubutunsa.”
A hadisi na 3053 a Sahihul Bukhari, Ibn Abbas yace, bayan da suka yi jayayyan, wasu daga cikinsu sai suka ce: ‘Hankalin Manzon Allah (S) ya gushe!’ Manzon Allah (S) sai yace musu; “Ku kyale ni, abin da nake a kansa ya fi abin da kuke jingina min” (Wato ni ba hauka nake yi ba, na san abin da nake fadi muku).
Ya kai Musulmi mai Imani! Har yanzu duniyar Musulmi suna rabe ne gida biyu, gado daga Sahabban da ke cikin wannan dakin. Har yau din nan da masu goyon bayan Manzon Allah (S) ne da kuma masu goyon bayan abin da Umar yace ga Annabi (S); cewa zafin ciwo ya rinjaye shi; cewa hankalinsa ya gushe; cewa ba mu da bukatar abin da zai rubuta mana; cewa a tare da ku akwai Alkur’ani, ya ishemu daga abin da Manzon Allah (S) zai rubuta mana! Tir!!! Kai a wanne bangare kake?
Wannan ba zagin Sahabbai bane, in ka fahimce shi a zagin Sahabbai ko raina su, sai nace ka fara komar da laifi ga Imaminka Bukhari da ya ruwaito abin da sahabban suka aikata daga bakin sahabi Ibn Abbas. Amma wallahi muna fada ne don mutum ya farka. Ya fahimci cewa addinin nan fa na Musulunci, Allah ne ya aiko Annabi Muhammadu (S) da shi, kuma ya wajabta a bi shi a kowace lahazar rayuwarsa da bayan ransa, kuma ya sanya sabawa Annabin nan a matsayin saba masa a yayin da yace: “Wanda ya bi Manzo hakika ya bi Allah.”
Idan har ta bayyana wasu gungun Sahabban Annabi (S) sun saba masa, ba kawai saba masa masa ba, sun ji ma jayayya da shi, ba kawai jayayya ba har fito-na-fito sun yi da shi, yace kaza su ce kaza ne, kamar yadda za mu ci a can gaba a cikin wannan nazarin, don me za su zama maka abin bi? Ashe Allah (T) bai ce; “Babu biyayya ga halitta a kan sabawa Allah ba?”
Hana abin rubutu da Umar tare da wasu gungun sahabbai suka yi, har ta kai ga Annabi (S) ya yi fushi da su yace su tashi daga kansa su fice su bashi waje, ba sabawa Allah bane? Don me suka zama maka abin bi a yanzu!?
Me yasa suka yi abin da suka yi a wannan lokacin? Shin sun yi makamancinsa kafin rannan? Me suka aikata bayan hanawan? Meye ra’ayi da isharar Manzon Allah (S) akan su a bayansa?
Insha Allah a cigaban rubutunmu za mu ji su.
Subscribe to:
Posts (Atom)