January 11, 2019

Shekaru 3 Da Kisan Kiyashin Zariya (5)

Daga Saifullahi M. Kabir

WAKI’O’IN DA SUKA BIYO BAYAN TA ZARIYA

Bayan waki’ar Zariya, wacce ta auku a tsakanin 12-14 ga Disamba, 2015, Gwamnatin Nijeriya ta rika daukar matakai na karfi, baya ga matakan karairayi don kawo karshen Harkar Musulunci da hana ta kowane irin motsi ko da na numfashi.

Yana daga makaman da Harkar Musulunci ke amfani da shi, shi ne su fito kan tituna a garuruwa su yi Muzaharori don bayyana wa Duniya halin da ake ciki, tare da kiran a saki Jagoransu daga haramtacciyar tsarewar da ake masa.

Wannan kuwa shi ne babban abin da Hukumar Nijeriya ta rika fada da shi. Duk sad da aka fito don yin Muzaharar, sai ta turo jami’anta su yi kokarin dakatarwa, a wasu lokutan ma har su bude wuta, su kashe wasu daga almajiran Shaikh Zakzaky.

An yi waki’o’i da dama bayan waki’ar Zariya, wasu a lokutan Muzaharar kiran a saki Shaikh Zakzaky, wasu kuma a wasu munasabobi kamar na Ashura da Tattakin Arba’in din Imam Husaini (AS).

Har ila yau, a wasu waki’o’in jami’an tsaron kan jikkata ’yan uwa ne, a wasu lokuta kuma har ma da kisan rayuka. Zan so in dan kawo wasu daga manya-manyan waki’o’in da suka auku a tsawon wadannan shekaru ukun da suka gabata.

WAKI’AR KADUNA

Waki'ar farko da aka yi a yayin Muzaharar kira a saki Shaikh Zakzaky (FreeZakzaky) a garin Kaduna ne, ranar Talata 15/12/2015, kwana guda bayan kama Malam Zakzaky (H). ’Yan sanda sun bude wuta suka kashe mutum bakwai nan take, suka kuma raunata wasu. Wasu ’yan’uwa shida kuwa, ’yan sanda sun kama, suka tafi da su da ransu ne, suka je suka kashe su. Ba su ba da gawarsu ba sai a ranar Litinin, bayan sun shafe kwanaki shida a hannunsu. Wannan ya sa Shahidan wannan waki’ar suka zama mutum 13. Akwai kuma mutane 10 da aka tsare su a wannan waki’ar, wadanda kotu ta wanke su daga tuhumar da ake yi masu bayan sun kwashe shekaru biyu a tsare.

An kuma samun Shahidi na 14, wato Shahid Idris Mando, wanda ya cika a ranar 17/4/2016, kimanin watanni 5 bayan waki'ar, bayan jinyar da ya sha na harbin da jami’an tsaron suka yi masa. An yi yi jana’izar Shahidai hudu a ranar Alhamis, Juma’a aka kuma yi ta mutum 3. Sauran mutum 6 din sai a ranar Litinin din da aka samu gawawwakinsu aka yi masu jana’iza.

Wannan ne farkon zaluncin da ya biyo bayan waki’ar Zariya. Duk da haka, bayan mako biyu da wannan ta’addancin, a ranar 2/1/2016 wasu matasa sun sake fitowa Muzaharar Free Zakzaky a Kaduna, inda suka faro daga Katsina Roundabout zuwa Leventis a cikin garin na Kaduna.

An ci gaba da gudanar da Muzaharori da tarukan da aka saba gudanarwa na Harkar Musulunci, duk da kuwa wasu ana yi lafiya, wasu kuma ana samun waki’o’i.

'Yan uwa a sahun Muzaharar #FreeZakzaky a Kaduna

TUNAWA DA SHAHIDAN KUDUS, 2016

Abin da ya biyo bayan wannan waki'ar shi ne taron tunawa Shahidan Kudus da aka yi Darur Rahma ranar 25/7/2016, inda Mopol suka zo da dukkan shirinsu na auka wa, suka nemi hana gudanar da taron.

’Yan’uwa ba su fasa ba sai da suka yi addu’o’i da jawabai suka tashi. Bayan an watse suka harba Tiyagas da kokarin kama wasu ’yan’uwa, amma sai Allah (T) ya takaita lamarin.

A shekarar 2017 ma ’yan sandan sun kuma zuwa wajen taron a Darur-Rahma, inda suka harbi mutane hudu bayan an tashi a taron.

Jami'an tsaro na fitowa daga Darur Rahma kafin su dirar ma Yan uwa 

YUNKURIN DIRAR WA MASU TATTAKI ZUWA ABUJA

Sai kuma a ranar 6/8/2016, da wasu sojoji suka yi kokarin dira a kan wasu matasa da suka yi Tattaki daga Zariya suka nufi Abuja da nufin kiran a saki Shaikh Zakzaky. Sakamakon ido da aka saka masu a wannan lokacin da takardar manema labarai da Harka ta fitar dangane da mummunan nufin sojojin a kan matasan, sai Allah ya tunkude sharrinsu, sai bai zama waki'a ba, ba su harba ko kama kowa ba. Suka tilasta matasan su juya, amma duk da haka sai da matasan suka san yadda suka yi suka shiga garin Abuja a wannan lokacin a kokarinsu na bayyana wa duniya halin da Shaikh Zakzaky ke ciki.

'Yan uwa na tattaunawa da Sojojin a yayin Tattakin a hanyar Abuja 

MUZAHARAR FREE ZAKZAKY A ZARIYA

Alhamis, 11/8/2016 ’yan sanda suka bude wa masu Muzaharar Free Zakzaky wuta da harbi da Tiyagas a daidai Kofar Doka Zariya, suka kama mutum 1, amma ba su harbi kowa da harsashi mai rai ba.

WAKI’AR FARKO A MUZAHARAR ABUJA

Mako biyu bayan hakan, aka kira gagarumar Muzaharar ‘Free Zakzaky’ a Abuja a ranar Alhamis 22/9/2018. A wannan ranar ’yan sanda sun yi ruwan Tiyagas da ma harsashi, sun raunata ’yan’uwa da dama. Sannan suka kama wasu mutum 12. Daga baya suka ba da belin yara biyar a ranar. Mutum bakwai din, wadanda Sistoci guda 3 ne da Burazu 4, sun kai su kurkukun Keffi suka tsare.

'Yan uwa mata da jami'an tsaron suka kama, bayan sun fito daga Kurkuku

Wannan ne karon farko da jami’an tsaro suka fara dira a kan masu Muzahara da harbi a Abuja. Amma Allah bai nufi an samu Shahidi ba.

SOME-SOMEN WAKI’AR ASHURA 2016

Bayan haka aka fara some-somen waki'ar Ashura ta shekarar 2016. Kafin zuwan ranar Ashura din a garin Jos, jami’an tsaron soji sun rika yin barazana ga duk mai tafiya da bakin kaya zuwa wajen zaman juyayin Ashura. Haka ma a Kaduna, jami’an ’yan sanda sun rika bi suna kokarin dakile masu Tattaki zuwa wajen zaman Ashura a tsawon ranekun zaman.

A ranar 9/10/2016, ’yan sanda a Kaduna, sun rika kama ’yan’uwa a hanyoyi daban-daban. Kamar akwai wasu da suka baro Hayin Danmani za su je Markaz, Malam Ahmad Rigasa da iyalansa kananan yara, ’yan sanda suka kama su. Haka ma cikin masu tahowa daga yankin Nasarawa/Barnawa, su Injiniya Mansur Karofi, ’yan sanda sun kama su, bayan sun harba masu Tiyagas a kan hanyar tasu ta zuwa wajen zaman Ashura, sannan suka kai su kotu. Daga nan aka yi gidan kurkuku da su.

Kananan yaran kuwa, sai daga baya aka ba da belin su. A yayin da wata Sista mai suna Malama Salamatu Abdullahi, sai da ta yi kusan wata uku cur a tsare a kurkukun Kaduna kafin kotu ta yarda ta ba da belinta. Sauran mazan kuwa, yanzu haka fiye da shekaru biyu ana tsare da su. Laifinsu kawai shi ne an kama su a kan hanya za su je zaman juyayin Imam Husaini (AS) a lokacin Ashura. An shiga kotu ya kai kusan sau 30 har yau ana dage-dagen shari’ar.

Wasu daga kananan yaran da yan Sandan suka kama 

Wani zaluncin sarari dangane da wadannan bayin Allah din shi ne farkon kai su kotu a ranar 10/10/2016, kwana 1 bayan kama su, kotun ta nemi ’yan sanda su gabatar da shaida a kan wadanda suke zargin, amma Sifeton na ’yan sanda mai suna Dogara, wanda kuma shi ne ‘Prosecutor’ din, ya ce suna rokon kotu ta ba su nan da makonni biyu don gabatar da shaidun. Nan kuwa Alkali ya sa aka kai ’yan uwan kurkuku zuwa lokacin da za a koma Shari’ar. Tun daga ran nan suka fara ganin zalunci har yau!

WAKI’AR ASHURA 2016

A ranar Laraba, 12/10/2016 (Ranar Ashura) aka yi waki'o'in Ashura a garuruwan Funtuwa, Kano, Sakkwato, Kaduna da Jos.

A duk garuruwan da aka yi waki’ar, garin Jos ne kawai Allah ya takaita ba a samu Shahidi ba, amma an yi zaluncin da ya kai matuka, wanda ya yi sanadiyyar rushe Markaz din ’yan’uwa na garin da jikkata gomomin ’yan’uwa da kama ’yan’uwa maza da mata, yara da manya kusan mutum 45, aka tsare su a kurkuku na tsawon watanni biyu kafin kotu ta ba da belin su.

A garin Funtuwa ta Jihar Katsina, an samu Shahidai 10 nan take. A yayin da jami’an tsaron suka kama ’yan’uwa kusan 37 aka tsare su tsawon watanni.

Wani Dattijo, daya daga cikin Shahidan Ashura a Funtua

A Kano ma ’yan sandan da kansu suka debo ’yan iskan gari a cikin motocinsu, suka rika kokarin auka wa Muzaharar. Allah bai nufi za a yi waki’a mai tsanani a ran nan ba. Amma daga baya jami’an tsaron sun kashe wani Haris mai lura da zirga-zirgan ababen hawa (Traffic), Shahid Ja’afar Ali.

A garin Sakkwato ma ’yan iskan gari sun kashe wani dan uwa, Shahid Alhaji Farouk Gwadangwaji a wannan ranar ta Ashura, wanda suka kashe shi bayan kammala Muzaharar.

A garin Kaduna ma, sai da aka tashi Muzaharar lafiya, sannan da yamma jami’an tsaron tare da hadin gwiwar ’yan iskan gari suka auka wa ’yan’uwa a Markaz, inda a nan ma aka samu Shahidai 3, sannan kuma suka kona Markaz din. Bayan sun sace kayan cikin ta suka rushe ta, suka kuma je makarantar Fudiyya da ke Layin Kosai suka lalata ta.

Kwanaki uku bayan waki’ar Ashura a garin Kaduna, a ranar 15/10/2016 wasu ’yan’uwa suka je don su share Markaz din da aka rusa, nan take ’yan sanda suka zo da ’yan iskan gari, suka dira a kan ’yan uwan, suka kashe mutum daya nan take, suka jikkata da dama.

Daga nan jami’an tsaron suka kuma raka ’yan iskan gari zuwa unguwar Mu’azu, inda nan ma suka rushe makarantar Fudiyyar unguwar. Suka kuma shiga gidan wani dan’uwa, Sharif Awwal a Kinkanau suka samu karamar yarinya a ciki, suka hau ta da duka, suka ji mata rauni a ka, sannan suka je gidan wani dan’uwa Alhaji Usman shi ma suka lalata shi, suka kwashe kayayyakin da ke ciki.

WAKI’AR TATTAKI 2016

Waki’ar Tattakin Arba’in din Imam Husain (AS) a yankin Kano, ta auku ne a ranar Litinin 14/11/2016, inda ’yan sanda suka tare kan titi a daidai lokacin da masu Tattakin suka zo wani gari da ake kira karfi a Jihar Kano, suka bude wuta. Nan take suka kashe mutanen da har yanzu ba a tabbatar da adadinsu ba, sai dai akalla ana da tabbacin ba su gaza mutum 25 ba.

Jami’an tsaron sun sace gawawwakin wadanda suka kashe sun je sun bizne su a kabarin bai-daya, in ban da mutum 8 da suka ba da gawawwakinsu. Cikin wanda suka kashe har da jaririya ’yar kimanin watanni 8 da haihuwa mai suna Zainabul Kubra.

Jaririya Zainab, daya daga wadanda aka kashe a yayin Tattakin 

A wannan waki’ar, ’yan sandan sun kama mutane kusan 90 a farko, suka ba da belin kananan yara daga baya, a yayin da kusan mutum 50 suka shafe tsawon watanni bakwai a kurkukun Kano, kafin kotu ta ba da belin su.

Yayin da yan sanda suke ruwan wuta a kan masu Tattakin Arba'een din

A ranar 5/3/2017 ne Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya furta da bakinsa cewa shi ya ba ’yan sanda umurnin bude wannan wutar da aka yi a kan masu Tattakin da ta jawo rasuwar mutane 25 a lokacin da yake ganawa da wasu Malamai da suka ziyarce shi a gidan gwamnati.

YUNKURIN AUKA WA ’YAN’UWA A SAKKWATO

Ranar Laraba 27/9/2017, Ashurar shekarar 1439 ta rage saura kwanaki kamar hudu, gwamnatin Jihar Sakkwato ta sanar da cewa ta haramta duk wani motsi ko muzahara da ’yan’uwa Musulmi almajiran Shaikh Zakzaky za su gudanar a duk fadin Jihar.

Washegari, Alhamis sai ga ’yan sanda dauke da muggan makamai a karkashin Kwamishinan ’yan sandan Jihar, Muhammad Abdulkadir sun zo Markaz, wadda ke kusa da gidan Shaikh Kasimu Umar. Lokacin da Shehin Malamin ya nufo Markaz din, sun tare shi sun yi magana da shi, ya tabbatar masu da cewa ba wani abu za a yi ba face abin da aka saba gudanarwa na zaman Ashura, sai suka tafi.

Yayin da Shaikh Qaseem ke magana da jami'an tsaron. 

Ranar Juma’a sai suka kuma dawowa, suka daidaici lokacin fitowar Shaikh Kasim zuwa Markaz, sai suka bi ta hanyar, inda suka yi kokarin nuna an tare masu hanya ne, nan suka kama wasu ’yan’uwa guda 6, suka kai su State CID, sannan kuma suka girke jami’an tsaro a kowane lungun unguwar har zuwa wayewar gari.

Allah ya takaita lamarin, a yayin da ’yan’uwa suka samu sabati, kuma aka dauki matakan kaucewa duk wani mugun nufinsu, har ya zama ranar 1/10/2017, wanda ta yi daidai da 10/1/1439H, an gudanar da Muzaharar Ashura da asubahin ranar a Sakkwato, kuma an tashi lafiya. Sai dai an kama mutane 4 a garin Bodinga bayan kammala Muzaharar Ashura a garin, ciki har da Na’ibin Wakilin ’yan’uwa na garin, Malam Abubakar Modi. Sai da suka yi watanni hudu da kwana 10 aka sake su.

A ranar Lahadi, 22/10/2017 ’yan sandan sun kuma yunkurin auka wa ’yan’uwa a Sakkwato, inda suka je wajen da aka rufe Muzaharar Free Zakzaky. Da suka tarar an tashi sai suka harba Tiyagas. Daga nan suka nufi Markaz, inda suka tarar ba kowa, sai suka tafi.

A daidai wannan ranar, ’yan sanda sun bude wuta a kan masu Muzahara a Kaduna, inda suka jikkata ’yan uwa da dama, suka kuma kama mutane hudu.

WAKI’AR TATTAKI 2017

Shekara guda bayan wancan aukawar da ’yan sanda suka yi a kan masu Tattakin Arba’in din Imam Husaini (AS) daga yankin Kano, a ranar 5/11/2017 aka fara Tattakin wannan shekarar ta 1439H daga yankin Kano. An taso da misalin karfe 10:00ns daga Kofar Mazugal, aka yi Sallar Zuhuraini a kofar Nasarawa, sannan aka ci gaba da tafiya har inda aka rufe Tattakin a Dangi ‘Roundabout’ gab da wajen da ake ce wa Gadar Lado da nufin washegari za a tashi daga wannan wajen.

Kwatsam! Sai ga ’yan sanda nan sun taho cikin mota 10 a guje, suna zuwa kafin wasu su sauka a motocinsu ma suka fara bude wuta a kan ’yan’uwan da suke wajen ba su gama watsewa ba. Nan suka harbi ’yan uwa masu yawa, aka samu Shahidai guda uku; A’isha Muhammad Azare, Husaina Dauda Nalado Kano da kuma Shahid Umar Ahmad Gano, wanda shi sun tafi da gawarsa ne sai bayan kwanaki 28 suka ba da ita aka yi mata jana’iza.

Da yake an tsara bayan an kammala Tattakin kowane yanki, za a hadu ne a Abuja a yi taron Arba’in a ranar 20 ga Safar din shekarar. A wannan ranar wacce ta dace da 10/11/2017, jami’an tsaro sun kuma bude wuta a kan ’yan uwa masu taron Arba’in din, inda suka jikkata da dama da barkonun tsohuwa.

Za mu ci gaba insha Allah.

January 07, 2019

Manzon Allah (S) Ramzi Ne, Abin Koyi - Inji Shaikh Zakzaky (H)

A wajen Mauludin Manzon Allah (S) na shekarar 2014.

Shaikh Zakzaky ya yi bayani a kan cewa Manzon Allah ne cikakken mutum, kuma abin koyi ga dukkan talikai. Ya Kuma jaddada alkawarin Allah ne dawo da addinin Musulunci ya yi iko da doron Duniya.

Takaicin Shaikh Zakzaky A Kan Kashe Jami'an Tsaron Nigeria

Kalli wani yankin Video din Mauludin Manzon Allah (S) a shekarar 2014 a garin Zariya.

A ciki, Jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya, Shaikh Ibraheem Zakzaky ya nuna takaicinsa dangane da yadda ake tura jami'an tsaron Sojoji da Yan Sandan Nijeriya ana kashe su da sunan fada da Boko Haram.

January 06, 2019

Shekaru 3 Da Kisan Kiyashin Zariya (4)

Daga Saifullahi M. Kabir

BAYAN HUKUNCIN KOTU

Bayan hukuncin babbar kotun Tarayya da ke Abuja na umurnin sakin Shaikh Zakzaky da maidakinsa Malama Zeenah, da biyan su diyya da sauran sharudda kamar yadda suka gabata, an rika samun kungiyoyi da daidaikun mutane suna jaddada kira ga gwamnatin Nijeriya karkashin Shugaban kasa Muhammadu Buhari kan ta mutunta umurnin na kotun kasa.

Bayan wannan hukuncin, wani tsohon Shugaban kungiyar Lauyoyin na kasa (NBA), Dakta Olisa Agbakoba, ya yi kira ga gwamnatin Buhari kan ta bi umurnin kotu wajen sakin Shaikh Zakzaky da maidakinsa.

Ya ce; “A matsayinsa na dan kasar nan, El-Zakzaky ya cancanci ’yanci. In kuwa akwai wani dalili na tsare shi, me ya sa ba za a bi umurnin kotu a sake shi ba, alabashi daga baya a kai shi kotu bisa wannan dalilin na daban?”

Shi ma tsohon Shugaban kungiyar Lauyoyin na Lagos, Mista Monday Ubani, ya jaddada cewa; “Wajibi ne gwamnatin Tarayya ta bi umurnin kotun Tarayya a cikin umurnin nata.”

A yayin da shi ma Festus Keyamo, wani fitaccen Lauya a garin Lagos din ya nanata cewa; “In har kotun kasa ta ba da matsaya a kan wani abu, to, wajibi ne gwamnati da al’ummar kasa su bi wannan matsayar.”

A ranar 10/12/2016, kimanin mako guda bayan hukuncin na kotun, kungiyar Lauyoyin ta kasa (NBA) a wajen wani taro da ta gudanar a garin Lagos, ta jaddada kira ga mutunta dokar ta kotu ga gwamnatin Shugaba Buhari.

Shugaban kungiyar, Abubakar Mahmod (SAN), ya bayyana matukar damuwarsu a kan rashin bin umurnin na kotun kasa, inda ya ce; “Ya sabawa duk wata doka a ce gwamnatin kasa ta ki bin umurnin kotu.”

Ya kuma jaddada kira a kan a gaggauta sakin Shaikh Zakzaky da matarsa kamar yadda kotun ta yi umurni. Tare kuma da kira ga mabiya Harkar Musulunci kan su rika mutunta dokoki da hakkokin sauran jama’a.

Wasu daga Lauyoyin Shaikh Ibraheem Zakzaky suna ganawa da manema labarai 

An kuma rika samun sakonnin taya murna ga Harkar Musulunci bisa nasarar da ta samu a yayin da ta kafawa masu zaluntar ta hujja da abin da suka yi imani da shi, kuma ta yi galaba a kansu. Kamar yadda wata kungiya mai suna ‘Mahdi Muslim Community’ da ke Nairobi a kasar Kenya ta fitar da takardar taya murna ga Harkar Musulunci a kan wannan nasarar, ta kuma jaddada kira ga gwamnatin Nijeriya kan ta gaggauta bin umurmin na kotun kasar, a ranar 7/12/2016.

Ganin yadda ake ta kiraye-kiraye ta ko’ina a kan gwamnati ta bi umurnin kotu, kwatsam sai ga wata kungiya da ake kira MURIC, wanda a farkon waki’ar Zariya sune farkon wadanda suka yi Allah-wadai da ta’addancin sojojin a kan ’yan kasa Musulmi, a wannan karon kuma bayan nasarar ’yan’uwa a kotu, sai kungiyar ta fito ta bakin Daraktanta, Farfesa Ishaka Akintola, wai ta bayyana Harkar Musulunci a matsayin kungiyar ’yan tashin hankali.

Sun bayyana hakan ne a ranar 5/12/2016, kwanaki uku bayan hukucin kotun Tarayyar ta Abuja, sai ga gwamnatin Kaduna ta fitar da abin da ta kira ‘White-Paper’, wadda take nuna matsayar gwamnatin Kaduna dangane da sakamakon rahoton JCI da ta kafa don binciken dalilin kisan kiyashin Zariya.

A cikin abin da ta kira ‘White-Paper’ din, gwamnatin Kadunan karkashin Gwamnan Jihar, Nasiru El-Rufa’i, ta bayyana matsayarta kan cewa za su bukaci gwamnatin Tarayya ta damka masu Shaikh Ibraheem Zakzaky don su gurfanar da shi a gaban kotu don su caje shi da laifuka daban-daban da ya aikata wa Jihar Kaduna a tsawon shekaru fiye da 30 na gudanar da Harkar Musulunci.

A nan, sai El-Rufa’i ya yi kunnen-uwar-shegu da kiran da kwamitin binciken na JCI ya yi a cikin rahoton da ya mika masa a ranar 15/7/2016, inda ya bukaci a hukunta Shugaban rundunar sojoji ta 1, ‘GOC 1-Division Army’ da ke Kaduna, Janar Oyebade, wanda shi ne ya jagoranci kashe mutum fiye da 347 da duk abin da ya faru a Zariya ranar 12-14/12/2015.

Kwatsam, ranar 1 ga Janairun 2017, sai ga Shugaban kasa Muhammadu Buhari a yayin da yake jawabin sabuwar shekara, ya kira ’yan’uwa Musulmi almajiran Shaikh Zakzaky da sunan ’yan’uwansa. Buhari ya ambaci cewa: “’Yan’uwanmu maza da mata na al’ummar Shi’a”, ya yi kira gare su a kan su kasance masu bin dokokin kasa.

Wannan furucin ya sa al’ummar Nijeriya sun yi caa a kansa ta hanyar mai da masa da martanin cewa shi ya fi kamata ya bi dokar kotun kasa, tunda har yau ba a samu wani laifi kwara daya da wadanda ya kira ’yan Shi’a ko Jagoransu ya aikata, wanda ya sabawa dokar kasar ba, sabanin shi da ya ki bin umurnin kotun kasa tsawon lokaci.

Wannan ya tilasta Kakakinsa, Malam Garba Shehu yin magana a ranar 2/1/2017, a yayin da yake hira da BBC, ya bayyana cewa, al’amarin tsare Shaikh Zakzaky sha’anin Jihar Kaduna ne, ba abin da ya shafi Shugaban kasa da shi. Ya kuma kara da bayyana cewa, wasu mutane sun daukaka kara bisa hukuncin kotun da ta ce a saki Shaikh Zakzaky. Sai dai bai fadi ko su waye mutanen da suka daukaka karar ba.

Ranar 16/1/2017 ne wa’adin da kotun Tarayya ta ba gwamnati kan ta saki Shaikh Zakzaky da matarsa ya cika, a yayin da har zuwa wannan lokacin ba su bi umurnin kotun ba. Sai a ranar 21/1/2-17 jaridar DAILY TRUST ta kawo wani labari daga fadar Shugaban kasa, inda suka bayyana cewa, suna ci gaba da tsare Shaikh Zakzaky ne saboda matsalar tsaro da bukatar jama’a. Suka kuma ce ita matarsa Malama Zeenah ba suna tsare da ita ba ne, tana kula da mai gidan nata ne a inda ake tsare da shi.

Idan ba ku manta ba, a baya mun kawo cewa, a ranar 13/6/2016, Lauyan DSS, Bar. Tijjani ya bayyana a gaban kotu cewa, ba ana tsare da Shaikh Zakzaky ba ne bisa tilasci. Ya ce ana ba shi kariya ne a inda aka aje shi bisa yardarsa. Har ma ya ce DSS sun yi masa maganin raunin da sojoji suka masa na Naira Miliyan 5 da rabi.

A ranar Alhamis, 20/4/2017 kuma, sai ga mataimakin Shugaban kasa, Farfesa Yemi Osibanjo ya rubuta a shafinsa na Twitter cewa, suna ci gaba da tsare Shaikh Zakzaky ne saboda matsalar tsaro. Ya kuma ce sun daukaka kara na hukuncin babban kotun Tarayyar da ta ce a saki Shaikh Zakzaky din.

In mai karatu yana lura, zai ga yadda maganganu suke sassabawa a tsakanin kwanaki daga jami’an gwamnatin, ta yadda suka kasa bayyana takamaiman dalili daya da ya sa suke tsare da Shaikh Zakzaky. Don haka a karshe suka ga ba mafita face kawai su mika Shaikh Zakzaky din zuwa ga gwamnatin Jihar Kaduna, don ta caje shi da kirkirarrun laifuffukan da ta ga dama.

WASU MATAKAN

Cikin matakan da Harkar Musulunci ta bi wajen bayyana zaluncin da aka mata da kuma kokarin samar da adalci daga dokoki da ka’ida na hukunta masu laifin yin wannan kisan kiyashin, kwamitin da ke fafutukar ganin an saki Shaikh Zakzaky da ke karkashin Harkar Musuluci, har ila yau, sun aika da koke zuwa ga Hukumar kare hakkin bil’adama ta Majalisar Dinkin Duniya (United Nations Human Rights Counsil) da ke Geneva, dangane da kisan kiyashin da aka yi a Zariya.

Bayan aikawa da wannan koken, UNHRC da ke Geneva din sun bai wa ‘FreeZakzaky Champaign Committee’ gayyata har sau uku a karo daban-daban, amma sai ofishin jakadancin Switzerland ta hana ‘Visa’ don amsa wannan gayyatar na zuwa ba da bayanai. Daga baya ma ofishin ya sanya takunkumi na tsawon shekaru uku ga Wakilan Kwamitin fafutukar ganin an saki Shaikh Zakzaky din.

Har ila yau, Harkar Musulunci ta shigar da karar duk masu hannu a kisan kiyashin Zariya a kotun hukunta manyan laifuka ta duniya, wato ‘International Criminal Court’ (ICC), wanda izuwa hada wannan rahoton Kotun na ICC ta kammala bincikenta a matakin farko dangane da kisan kiyashin, kuma har ma binciken nasu ya tabbatar da cewa sojojin Nijeriya sun aiwatar da wannan kisan kiyashin a Zariya. Ya zuwa yanzu ana jiran mataki na gaba ne, wanda shi ne kotun ICC din ta ayyana wadanda alhakin wannan kisan kiyashin na Zariya 2015 ya rataya a wuyansu. Daga nan sai matakin tuhumar su da ba da ‘waranti’ na a kama su a gurfanar da su a gabanta a mazauninta da ke Hague a Netherlands.

Harkar Musulunci ta kuma rika shirya Muzaharori a Abuja da sauran garuruwa da kuma gabatar da tarurrukan wayar da kan al’umma da fadakarwa, tare da bayyana zaluncin da aka yi a Zariya, musamman ga ’yan boko da masu rajin kare hakkin bil’adam, inda aka samu da dama suka rika fitowa suna Allah wadai, musamman a kan ci gaban gwamnatin Buhari na yunkurin kawar da Harkar, da auka wa ’yan uwa Musulmi a duk lokacin da suka fito don yin Muzahara ko wani taro da ya shafi addini da fahimtarsu.

Ita kuwa gwamnati a kowane lokaci ba ta da aikin da ya wuce ci gaba da fada da Harkar Musuluncin a matakin Jiha da matakin Tarayya. Tun bayan waki’ar ta Zariya, jami’an tsaro sun ci gaba da auka wa ’yan’uwa a garuruwa daban-daban a lokuta daban-daban, kamar yadda za mu kawo su daki-daki a ci gaban rubutunmu in Allah ya nufa.

Shekaru 3 Da Kisan Kiyashin Zariya (3)

Daga Saifullahi M. Kabir

HARKA DA MATAKAN SHARI’A

A kokarinta na neman a yi mata adalci daga mummunan ta’addancin da sojojin Nijeriya suka yi na auka wa Jagoranta, rushe duk wani muhalli mallakinsa, kashe kimanin mutane 1,000 daga mabiyansa, da kuma kama shi a tsare ba tare da kwakkwaran dalili ba, Harkar Musulunci ta samar da Lauyoyi a karkashin jagorancin wani babban Lauya, Mr. Femi Falana (SAN), daya daga cikin lauyoyin da suka rika yin kira a kan a yi adalci ta hanyar hukunta masu hannu a rikicin Zariya tun a farkon Waki’ar.

Mr. Femi Falana SAN, na jawabi a wajen wani Muzaharar kira a saki Shaikh Zakzaky a Abuja 

Bayan shafe tsawon lokaci da aka yi Lauyoyin na Harkar Musulunci suna neman damar ganin Shaikh Zakzaky, sai a ranar Juma’a 1/4/2016, kimanin watanni biyar da tsare Shaikh din, sannan hukumomi suka bari Lauyoyin a karkashin Mr. Falana suka gana da shi a karon farko a inda ake tsare da shi a Abuja. Wannan ne ma ya ba Falana damar rubuta takarda a ranar 5/4/2016 ga Daraktan DSS na lokacin, Lawal Daura, a kan neman a bar iyalai da Likitocin wanda suke karewa su rika ganawa da shi.

Daya daga cikin lauyoyin Shaikh Ibraheem Zakzaky, Festus Okoye ya sanar da manema labarai a ranar 13/4/2016 cewa, sun shigar da kara a manyan kotuna guda biyu a Abuja da Kaduna a madadin Shaikh Ibraheem Zakzaky da matarsa, Malama Zeenah Ibrahim, bisa caji daban-daban.

Karan na kotun Babbar kotun Abuja (Federal High Court -6, Abuja), Shaikh Zakzaky da matarsa Malama Zeenah suna karar Antoni-Janar na kasa (AGF), Abubakar Malami, da Daraktan hukumar jami’an tsaron farin kaya (DG, DSS), Lawal Daura, da kuma shugaban hukumar ’yan sanda na kasa (IG).

Masu karan guda biyu, suna neman kotu ta tabbatar musu da hakkokinsu da suka hada da, hakkin rayuwa, hakkin walwala da zirga-zirga, hakkin kare daraja da mutunci, da kuma hakkin rayuwa cikin aminci tare da iyali.

Bisa take wadannan hakkokin da wadanda ake zargin suka yi ga Shaikh Zakzaky da Matarsa, ta hanyar tsare su na tsawon watanni biyar ba tare da likitocinsu, lauyoyinsu ko iyalinsu sun ziyarce su ba, sun bukaci kotun ta sa wadanda suke tsare da sun su biya su diyyar Naira biliyan biyu (2 Billion Naira).

Shi kuwa karar da aka shigar a Kaduna, Shaikh Zakzaky da matarsa Malama Zeenat ne suke karar Antoni-Janar na kasa (AGF), da Sojojin Nijeriya (NA), da Shugaban sojojin Nijeriya, Tukur Buratai, da Hukumar tsaron farin kaya (DSS), da kuma Antoni Janar kuma Kwamishinan shari’a na jihar Kaduna, bisa zargin kai hari a gidansu a ranar 12-14/12/2015, kashe musu ’ya’yansu da almajiransa a gabansu, rusa musu muhallansu da barnata dukiyarsu da kuma kama su a tsare, wanda ya tauye ’yancinsu a matsayinsu na ’yan kasa.

SHARI’AR KOTUN ABUJA

An fara shiga shari’ar da ke kotun Abuja ne a ranar 23/5/2016, a gaban mai shari’a Gabriel Kolawale, inda aka dage zuwa ranar 13/6/2016 sakamakon rashin zuwan wasu daga lauyoyin wadanda ake zargi. A ranar Talatar, 13/6/2016 aka ci gaba da shari’ar, inda lauyan DSS, Barr. Tijjani Gazali ya bayyana wa kotu cewa ba bisa tilasci ake tsare da Shaikh Zakzaky ba, yana tsare ne bisa zabin kansa, kuma su suna tsare shi ne bisa yardarsa don su ba shi kariya.

Gazali ya kuma bayyana wa kotun cewa, a tsawon watannin da ake tsare da Shaikh Zakzaky da Mai dakinsa a wajen DSS, an kashe masa abin da bai gaza Naira miliyan 5.1M ba na magani. A nan ne sai Lauyoyin Shaikh Zakzaky suka bukaci kotun ta ba su lokaci don mai da martani ga ikirarin na lauyan DSS, inda Alkalin ya daga ranar ci gaba da sauraron shari’ar zuwa ranar 13/7/2016.

Bayan dawowa kotun a ranar 13/7/2016, Lauyoyin Harka sun gabatar da amsa ga ikirarin na Lauyan DSS. Abin da ya tabbata shi ne hatta man injin da ke haska wajen da ake tsare da Shaikh Zakzaky a Abuja, Shaikh din ne ke saya da kudinsa tun sad da aka tsare su. Mai shari’a Kolawaye, ya sake dage ci gaba da shari’ar zuwa ranar 20/9/2016. Ya bayyana zuwan Alkalai hutu a wannan tsakanin a matsayin dalilin dagewa da nisa.

Kodayake Lauyan Shaikh Zakzaky, Mr. Falana ya nemi kotun ta ci gaba da zaman a cikin hutun, amma Alkalin ya yi watsi da bukatar tasa. Sai dai a ranar 30/8/2016, Falana ya aika wa kotun da wasika, yana mai neman ta ba da dama a kai Shaikh Zakzaky asibiti a kasar waje, sakamakon rashin lafiyar idanunsa da yake kara tsananta.

Bukatar Falana ba ta amsu ba, a yayin da aka dawo kotu a ranar 20/9/2016, nan kuma zaman kotun bai yiwu ba, sakamakon taron da Alkalan manyan kotuna suke yi a wannan ranar a Abuja. Sai aka kuma saka ranar 5/10/2016 a matsayin ranar da za a dawo don ci gaban shari’ar.

A ranar 5/10/2016, Mai Shari’a Gabriel Kolawale, bayan sauraron abubuwan da suka rage, ya bayyana takaicinsa matuka a kan shari’ar, inda ya ce irin wannan take hakkin na dan kasa abin kunya ne ga Nijeriya. Ya nemi da a je a sulhunta tsakanin masu karar da wadanda ake kara kafin ranar 25/11/2016, inda ya ce zai yanke hukunci a wannan ranar ko da ba a sulhunta ba. Ko da ranar 25/11/2016 ta zagayo, ba a yi zaman kotun ba, nan ma Alkalin ya sake kara mako guda, inda ya saka ranar 2/12/2016 a matsayin ranar yanke hukunci.

Ranar 2/12/2016 ne kotun ta yi zamanta na karshe, inda mai shari’a Gabriel Kolawale ya karanta hukunci. Ya bayyana tsare Shaikh Zakzaky da mai dakinsa da ake yi a matsayin haramtacce, wanda ya saba doka. Ya kuma saba wa kundin tsarin mulkin Nijeriya. A madadin kotun, Kolawale ya ba da umurni ga gwamnatin Nijeriya ta gaggauta sakin Shaikh Zakzaky da mai dakinsa, Malama Zeenat a cikin kasa da kwanaki 45 daga ranar wannan hukuncin.

Har ila yau, kotun ta ba da umurnin gwamnatin Nijeriya ta gina wa Shaikh Ibraheem Zakzaky gida a duk jihar da yake bukatar zama a fadin jihohin arewacin Nijeriya, tare kuma da biyan kowannen su, (Shaikh din da Malama Zeenat) diyyar Naira miliyan 25 na haramtaccen tsarewar da aka yi musu, wanda ya kama Naira miliyan 50. Sannan kuma a yayin sakin, Hukumar DSS su mika Shaikh din da Matarsa ga wani babban Dan sanda, su kuma su raka shi zuwa gidan da aka tanadar masa a cikin kasa da awa 24.

SHARI’AR KOTUN KADUNA

Ita kuwa shari’ar Kaduna, wanda aka shigar a High Court, karkashin mai shari’a S.M Shu’aibu, bisa neman hakkokin barnar da aka yi a Zariya, an fara gudanar da zaman kotun ne a ranar 18/5/2016, inda aka dage ta zuwa ranar 7/6/2016 don ci gaba da sauraron karar.

A ranar Alhamis, 7/6/2016, aka koma don ci gaba da shari’ar, inda bayan kammala karanta kara, sai lauyan gwamnati, wato Antoni Janar na Tarayya ya nemi kotun da ta ba su lokaci don nazari da mai da martani ga Karan. Nan aka dage ci gaban sauraron karar zuwa ranar 15/6/2016.

A ranar Alhamis, 15/6/2016 an dawo kotun don ci gaba da shari’ar. Sai dai Babban Lauyan da ke wakiltan Shugaban sojojin Nijeriya bai zo ba, ya turo wani Lauya mai suna Husain Oyebani a matsayin wanda zai wakilce shi. Husaini ya bayyana wa kotu cewa ba zai iya kare shari’ar ba saboda bai yi nazarin ta ba. Sai ya nemi a ba su lokaci don yin nazarin shari’ar. Kotun ta karbi uzurinsa, kuma Alkalin ya dage ci gaba da sauraron shari’ar zuwa ranar 30/6/2017, inda ya gargade su da shiryawa kare karar zuwa wannan ranar.

Ranar 30/6/2017, Lauyan na sojoji kuma mai tsayawa a madadin Tukur Buratai, wato, Mr. Biola Oyebanji ya bayyana a gaban kotun, inda ya bukaci kotun ta kori shari’ar, bisa hujjar cewa shari’ar na kotun Kaduna ta yi kama da ta Abuja da Alkali Kolawale ya yanke hukunci a ranar 2/12/2016.

Mai Shari’an, Sale Musa Shu’aibu, ya bayyana cewa kararrakin guda biyu da aka shigar a Kaduna da wanda aka shigar a Abuja abu ne mabambanta. Ya ce ya nazarci hukuncin da dan’uwansa Alkali Kolawale na babban kotun tarayya ya gabatar a kan neman hakkin tsarewa ba bisa ka’ida ba, da kuma neman ’yancin rayuwa. Kuma ya ga akwai bambanci da wanda yake gabansa. Don haka ya sanya ranar Alhamis, 6/7/2017 a matsayin ranar da zai yanke hukunci.

A ranar 6/7/2017, kwatsam sai Alkali S.M Shu’aibu ya bayyana da sabon al’amari. Inda ya karbi bukatar Lauyan sojoji, ya koma kan ra’ayin cewa kararrakin da aka shigar a kotun Abuja da wanda aka shigar a wannan kotun nasa abu guda ne. Don haka kai tsaye ya yanke hukuncin korar shari’ar gaba daya.

Da yake mai da martani a kan hukuncin na kotun, Shugaban kwamitin fafutukar ganin an saki Shaikh Zakzaky, Malam Abdurrahman Abubakar Yola, a wata takardar manema labarai da ya saka wa hannu a ranar 6/7/2017, ya bayyana bambancin da ke tsakanin karar da aka shigar a kotun Abuja da wanda aka shigar a Kaduna.

Ya ce, a Abuja an yi karar Antoni Janar na kasa, Shugaban DSS, da kuma Shugaban rundunar ’yan sanda na kasa a kan laifin da suka aikata a Abuja na tsare Shaikh Zakzaky da matarsa ba bisa ka’ida ba, da hana su ’yancin walwala. A Kaduna kuwa, an shigar da kara ne na Antoni Janar na kasa (AGF), da Sojojin Nijeriya (NA), da Shugaban sojojin Nijeriya, Tukur Buratai, da Hukumar tsaron farin kaya (DSS), da kuma Antoni Janar kuma Kwamishinan shari’a na jihar Kaduna, su kuma bisa laifin da suka aikata a jihar Kaduna na kai hari ga Shaikh Zakzaky da kama shi ba bisa ka’ida ba, kashe masa ’ya’ya da ’yan uwa da almajirai da kuma rusa masa muhallansa. “Don haka bambancin a bayyane yake,” in ji shi.

Malam Yola ya ce: “Wannan hukuncin ba zai taba karya mana kwarin guiwarmu na ci gaba da neman adalci ta hanyar bin matakan shari’a ba.”

Ya zuwa hada wannan rahoton, mun samu labarin cewa, Lauyoyin na Shaikh Zakzaky sun daukaka karar shari’o’in guda biyu zuwa kotun daukaka kara wato ‘Appeal court’; bisa rashin bin umurnin sakin Shaikh Zakzaky da kotun Abuja ta ba da, da kuma korar karar da kotun Kaduna ta yi bisa hujjar kamanceceniyar shari’un biyu. Sai dai alamu na nuna rashin jin dadin hakan daga hukumar Nijeriya, a yayin da ta kowane hali suke ta kokarin kawo cikas ga fara zaman na kotun daukaka kara a boye.

Ku biyo mu don jin abubuwan da suka biyo bayan yanke hukuncin kotun Tarayya da ke Abuja.

Shekaru 3 Da Kisan Kiyashin Zariya (2)

Daga Saifullahi M. Kabir

BAYAN KISAN KIYASHIN ZARIYA:

Da yammacin ranar Litinin, 14 ga Disambar 2015 ne Shugaban rudunar soja ta 1 ke Kaduna, Manjo-Janar Adeniyi Oyebade ya kira taron manema labarai, inda ya bayyana cewa shi ne ya ba da umurnin a mamaye Husainiyyah Bakiyyatullah, gidan Shaikh Zakzaky da ke Gyallesu da Darur-Rahma. Ya kuma tabbatar da cewa, sun kama Shaikh Zakzaky, tare da matarsa da kuma wasu, kuma Shaikh din yana nan a raye cikin koshin lafiya. Ya yi wa ’yan jaridar alkawarin washegari su zo su gana da shi. Sai dai hakan bai yiwu ba.

’Yan’uwa Musulmi sun fito kan tituna a birane da kauyuka a washegarin wannan ranar don yin Muzaharar Allah-wadai da ta’addancin sojojin, tare da kira a kan su saki Shaikh Zakzaky. ’Yan sanda sun bu]e wa masu wannan Muzaharar wuta a garin Kaduna a ranar Talatar 15/12/2015, inda suka kashe ’yan uwa 13. Bakwai nan take, yayin da mutane shida sun kama su ne suka tafi da su da ransu, suka azabtar da su, sai a ranar Juma’a suka ba da gawawwakinsu aka yi musu jana’iza.

An samu Shahidi na 14, mai suna Shahid Idris Mando, wanda Allah ya karbi rayuwarsa a ranar 17/4/2016 bayan jinya da ya yi na tsawon watanni uku cur na harbin da jami’an ’yan sandan suka masa a yayin wannan Muzaharar ta ranar Talatar bayan waki’ar Zariya.

Ranar Alhamis, 17/12/2015 kafar watsa labarai ta ‘Fars News Agency’, ta ruwaito cewa Sarkin Saudiyyah, Salman Bin Abdul’azin ya kira Shugaban kasar Nijeriya, Muhammadu Buhari don ya yi masa jinjina, tare da bayyana harin kare-dangin da sojojin Nijeriya suka kaddamar a kan ’yan uwa Musulmi mabiya mazhabar Ahlul Baiti (AS) a matsayin daya daga hanyoyin yaki da ta’addanci.

Tsawon kwanaki biyu sojoji suka yi suna aikin kwasar gawawwakin da suka kashe a Gyallesu, inda suka kai wasu dakin ajiye gawa na asibitin Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, suka kuma tafi da wasu Depot dinsu da ke Zariya.

A tsakar daren wannan Alhamis din, 17/12/2015 ne sojoji suka kwashe duk gawawwakin na ’yan’uwa Musulmi suka je suka binne su a ramukan bai-]aya a kauyen Mando da ke bayan garin Kaduna da kuma wasu guraren da ba a iya tantance ina ne ba har yanzu.

Sakataren Gwamnatin jihar Kaduna, Alhaji Lawal Balarabe Abbas, ya bayyana a gaban kwamitin binciken abin da ya faru a Zariya (JCI) da Gwamna Nasiru El-Rufa’i ya kafa ranar Litinin 11/4/2016 cewa, shi da wasu daga jami’an gwamnatin Jihar Kaduna, da suka hada da shi Gwamnan kansa, wasu Sanatoci da kuma Babban Daraktan ofishin kula da harkokin addini na Kaduna, Injiniya Namadi Musa, sun yi zama, inda suka samo izini daga kotu, kuma suka je suka jagoranci Sojoji wajen bizne gawawwakin ’yan’uwa Musulmi da aka kashe a Zariya a ramin bai-daya a kauyen Mando da ke bayan garin Kaduna.

Alhaji Lawal Balarabe ya kuma bayyana a gaban JCI cewa, shi da kansa, tare da Manjo Odundare sun kirga gawawwakin ’yan’uwa Musulmi guda 156 a asibitin ABUTH da ke Zariya, sun kuma kirga wasu gawawwaki guda 191 a Depot din Soji na Zariya, inda suka kwaso su zuwa kauyen Mando, suka bizne su a ramukan bai-daya da aka haka bisa taimakon sojoji guda 40. Aikin wanda ya ce sun fara shi da tsakar dare ya dauke su tsawon awanni kafin su kammala. Nan suka bizne maza da mata, yara da manya a rami guda, ba tare da rarrabewa ba.

Kodayake ba a iya samun cikakken bayani a kan inda sojojin suka bizne gawawwakin da suka yi wa kisan-kiyashin ba, sai a ranar 6 ga Junairun 2016, wasu ’yan’uwa masu bincike suka gano. Jawabin Alhaji Lawal Balarabe a gaban kwamitin ta JCI ya kara tabbatar da gaskiyar abin da ake tsammani a baya.

Da yake kisan-kiyashin na Zariya an yi shi ne bisa kwangilar nufin shafe Harkar Musulunci a Nijeriya da Jagoranta, don haka bayan abin da sojoji suka yi na kashe mutane fiye da 1,000 a ranakun 12-14 ga Disambar, tare da rushe gine-ginen Husainiyyah, Gidan Shaikh Zakzaky da sakawa makabartar Darur-Rahma wuta, sai gwamnatin Jihar Kaduna ta shiga rushe duk wani gini da yake da alaka da Shaikh Zakzaky, ko kuma Harkar Musulunci baki daya a garin Zariya.

A ranar 17 ga Disambar 2015, Gwamnan Kaduna, Nasiru El-Rufa’i ya bayyana a kafafen ya]a labaran Jihar Kaduna, inda ya yi wasu kalamai da suke nuna goyon bayan abin da sojoji suka yi, da kuma tabbatar da cewa hakan an yi shi ne da masaniyar su, da kuma kokarin bata Harkar Musulunci.

Nasiru El-Rufa’i ya yi ikirarin cewa Harkar Musulunci tana takura wa al’umma a Jihar Kaduna a tsawon shekaru 30 ta hanyar rufe manyan hanyoyi a yayin tarukansu, amfani da makarantun gwamnati a yayin Tattakin Imam Husaini (AS), da kuma barazanar kwace wa wadanda suke makwabtaka da su filaye da gidaje. A nan ne ya bayyana cewa Husainiyyah Ba}iyyatullah ma ba bisa izini aka gina ta ba.

Sai dai Harkar Musulunci ta warware dukkan zarge-zargen nasa, a wani rubutu da Shugaban bangaren yada labarai na Harkar ya saka wa hannu. Ya nuna cewa ba su taba kashe hanya, ko hana wasu wucewa ba a yayin tarukansu, har ma suna da jami’an kula da ba da hannu a yayin taruka. Kuma duk inda ake amfani da shi a yayin Tattakin Arba’in, wanda aka fara yin sa a nan kasar shekaru uku da suka gabaci waki’ar, ana neman izinin jami’an kula da wajen. Sannan kuma ya bayyana cewa, Harkar Musulunci ba ta bata kwace wani waje, fili, gida, ko masallaci daga wani, ko wasu ba, kamar yadda ba ta taba yin gini a wani waje ba face ta cika sharuddan Hukumar tsara gine-gine.

Sai dai kamar El-Rufa’i ya yi wannan bayanan ne don ya samu damar ci gaba da rushe gine-ginen da ke da alaka da Shaikh Zakzaky, don haka a tsakanin ranar Lahadi zuwa Talata 20-22/12/2015, ya tura ma’aikatan KASUPDA bisa rakiyar jami’an tsaro suka je suka karasa rushe duk gine-ginen da ke Husainiyyah Bakiyyatullah, da ginin NTC, wanda ya shafe fiye da shekaru 50 (ba a dade da sayensa a hannun masu shi ba wannan abin ya auku). Tare da rushe shagunan da ake ginawa a tsallaken Husainiyyah, wanda su ma Shaikh Zakzaky ya sayi filin ne daga hannun masu shi ba jimawa.

KASUPDA bisa rakiyar jami’an tsaron sun kuma je unguwar dan Magaji da ke Zariya, inda suka rushe ginin Fudiyyah Islamic Center, wanda tsohon waje ne da Harkar Musulunci ta saye shi fiye da shekaru 20 da suka gabata a ginensa, kuma ba a yi komai a wajen ba a yayin harin sojojin. Suka je garzaya unguwar Jushi duk a cikin garin Zariya din, suka rushe wani gida da a cikinsa aka bizne Mahaifiyar Shaikh Ibraheem Zakzaky. Tare da rushe Darur-Rahma a kauyen Dembo, muhallin da ke dauke da makabartar Shahidai, masallaci, dakin taro da kuma gine-ginen tarihi don yin fima-fiman addini.


MUZAHARORIN ALLAH-WADAI

Al’ummar duniya ta kadu sosai da wannan harin ta’addancin da gwamnatin Nijeriya ta tura sojojinta suka yi a kan Shaikh Zakzaky da Harkar Musulunci, don haka aka ri}a samun zanga-zangar lumana (Muzaharori) tare da gangamin Allah-wadai a kusan dukkan manya biranen kasashen duniya.

Tun a daren Asabar, a yayin da sojoji suke gabatar da harin a gidan Shaikh Zakzaky, ’yan’uwa Musulmi a duk manya da kananan garuruwan kasar nan sun rika fitowa Muzaharar Allah-wadai da harin. Haka ma a kasar Birtaniya, yayin da wasu suka bayyana a ofishin jakadancin Nijeriya da ke birnin London, suna kira ga a dakatar da harin ta’addancin da sojojin Nijeriya suke gabatarwa a kan ’yan’uwa Musulmi a Nijeriya.

A ranar Juma’a, 18 ga Disamabar 2015, an gabatar da Muzaharori da gangamin Allah-wadai da aikin sojojin Nijeriya a kan ’yan kasa marasa makami a garuruwa kusan 50 a kasar Pakistan kawai, musamman a manyan biranensu da suka hada da Lahore, Karaci, Islamabad da sauransu.

Haka ma a Indiya, Muzaharorin Allah-wadai da kuma kiran a saki Shaikh Zakzaky ya gudana garuruwa fiye da 20. Haka kuma a Iran, Irak, Newyork, Istanbul, Canada da wasu kasashen Afirka da suka hada da Nijar da Kamaru.

Muzaharori da gangamin kira a saki Shaikh Zakzaky sun rika gudana a tsawon wadannan shekaru ukun, musamman a garuruwan Nijeriya, wanda a farkon wannan shekarar aka fara gabatar da Muzaharar kullum a babban birnin Tarayyar Nijeriya, Abuja.

'Yan uwa a wajen Muzaharar #FreeZakzaky a Abuja 

A yayin da tarukan addu’a da fatan Allah ya dauki fansa ba su dakata ba, ana ci gaba da gudanar da su a ko’ina, ciki har da birnin Makkah da Madina, Haramin Imam Ali da ke Najaf, da na Imam Husaini a Karbala da kuma Haramin Imam Ridha (AS) da na Sayyida Ma’asuma a biranen kasar Iran.


ALLAH-WADAI DAGA KUNGIYOYI DA MUTANE

Kasashe daban-daban, ciki har da kasar Amurka da Iran, da kuma wasu cibiyoyi da manyan kungiyoyi a Nijeriya da suka hada da Majalisar koli ta Harkokin Addinin Musulunci a Nijeriya (NSCIA), kungiyar Kiristoci ta kasa (CAN), Majalisar Dattijan Nijeriya, kungiyar kwadago ta kasa (NLC), kungiyar fafutukan kafa kasar Biafra (IPOB) da wasunsu, sun yi Allah-wadai da faruwar lamarin, tare da kira a gaggauta bincike a kuma hukunta wadanda suke da laifi a abin da ya faru a Zariya.

Wata kungiya mai suna ‘Socialist Party of Nijeriya’ a ranar 24/12/2015 ta yi kira ga Shugaban sojojin Nijeriya, Janaral Tukur Buratai da ya sauka daga mukaminsa har sai an kammala bincike a kan barnar da sojojin suka yi a karkashin ikonsa. Ta kuma yi Allah-wadai da takurawar da ake wa mabiya Harkar Musulunci, inda ta bayyana haramta zanga-zangar kiran a saki Shaikh Zakzaky da El-Rufa’i ya yi bayan abin da ya faru a matsayin goyon baya ga kisan-kiyashin da sojojin suka yi.

Haka ma kungiyar da ake kira a Turance, ‘Non-profit Making organisation’, sun bayyana takaicinsu a kan rayukan da sojojin suka kashe a Zariya ta hanyar cewa; “Ta kowane yanayi abin da sojojin suka yi ya saba wa ka’idar dokar kasa, ya kuma saba wa kundin tsarin mulkin Nijeriya.”

A yayin da kungiyar Inyamurai ta ‘Igbo Mandate Congress’ ya yi kira ga Shugaban kasa Buhari a kan ya samar da wani Kwamiti da zai ba Shaikh Zakzaky hakuri a kan abin da ya faru a madadin gwamnatinsa.

Daidaikun mutane ma sun rika tir da kisan-kiyashin Zariya, a yayin da tsohon Ministan sufurin jiragen sama na kasa, Femi Fani Kayode, ya bayyana abin da ya faru a Zariya a matsayin shiryayye kuma tsararren abu. Kuma ya yi Allah-wadai da kashe rayukan ’yan kasa marasa makami da kona gidaje da sojoji suka yi a Zariya, tare da tabbatarwa da Buhari da Buratai cewa za su bayyana a gaban kotun hukunta manyan laifuka na Duniya (ICC) ba da jimawa ba.

A wata hirarsa da tashar Talabijin din Channels TV a ranar 22/12/2015, mai rajin kare hamkin bil’adama, kuma Babban Lauya, Mista Femi Falana (SAN), ya nuna matukar takaicinsa a kan yadda jami’an sojoji suka take doka da kafafunsu, suka bude wuta a kan ’yan kasa marasa makami ba bisa ka’ida ba. Inda ya bayyana dole ne gwamnatin Nijeriya ta kama duk wanda ke da hannu a wannan harin ta hukunta shi, ta kuma biya diyyar duk barnar da aka yi na rayuka da dukiya. Sannan ta sanya darussan koyar da sanin hakki da ’yancin dan’adam a cikin kwasa-kwasan da ake koyarwa a makarantun sojoji.

Haka ma Babban Malamin adinin Musulunci, kuma Shehin Darikar Tijjaniya, Shaikh Dahiru Usman Bauchi, ya bayyana zubar da jinin da aka yi a Zariya a matsayin abin da zai jawo wa kasa fushin Allah. Ya kuma yi Allah-wadai da ayyukan sojoji, musamman da yake a daidai lokacin sun kama wasu daga Mahadattan Alkur’ani a Jihar Yobe, sun gana masu azaba, tare da yunwatar da su na tsawon kwanaki.


CI GABAN YUNKURIN GWAMNATI NA SHAFE HARKAR MUSULUNCI

Ganin irin tausayawar da ake ta samu daga kungiyoyi da mutane, tare da Allah-wadai da ake yi da wannan ta’addancin na Sojojin Nijeriya a kan ’yan’uwa Musulmi, sai gwamnatin Buhari ta fara fito da wasu shirye-shirye da tsare-tsare da zai bayyana abin da aka yi a matsayin abin da ya dace, tare da samar da muryoyin da za su nuna goyon baya da cire tausayin al’umma ga iyalai da dangin wadanda aka kashe a Zariya.

A ranar Asabar, 19/12/2015 wasu daga cikin Gwamnonin Arewa, karkashin Shugaban mungiyar Gwamnonin, Kasim Shettima, suka gabatar da zama a Kaduna, inda suka tattauna yadda za su bullowa su taka wa Harkar Musulunci burki a Jihohinsu.

Makonni biyu bayan wannan zaman, a ranar 28/12/2015 kungiyar Limamai da Malamai na Jihar Kaduna a karkashin jagorancin Marigayi Shaikh Usman Abubakar Babantine suka gana da Gwamnan Kaduna, Nasiru El-Rufa’i, inda suka bayyana goyon bayansu a kan fada da yake da wadanda suka kira su da ’yan Shi’a a Jihar Kaduna, suka kuma bayyana masa cewa hakan da yake wani aiki ne ma addinin Musulunci.

Kwanaki kadan bayan wannan zaman, a ranar 14 ga Junairun 2016, shi ma GOC I Division, Manjo-Janar Adeniyi, wanda shi ne ya jagoranci duk hare-haren da sojoji suka yi a Zariya, ya gana da wasu Malaman Wahabiyawa da Limamansu, inda ya yi musu bayani a kan dalilin da ya sa suka yi fada da Harka Islamiyya, da kuma sanar da su abin da sojoji suke bu}atar su sanar da almajirai da mabiyansu. A karshe ya ba su kyautar Naira dubu 500 suka raba a tsakanin su.

Wannan sai ya ba wasu daga Malaman kungiyar Izala, wadanda dama ba su iya boye gabarsu ga Shi’anci ba, damar ganin sun ri}a halatta ta’asar da sojoji, tare da gwamnati suka yi a kan ’yan’uwa Musulmi da bayyana kashe rayuka da barnata dukiyoyin da su Janaral Oyebade suka yi a Zariya a matsayin aikin da addinin Musulunci ke bukata.

A ranar 21/12/2015, Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi ya yi jawabi, inda yake yabawa da kashe rayukan da sojojin suka yi a Zariya, inda ya bayyana shi a matsayin fada da masu zagin Sahabbai. Sarki Sanusi ya ambata cewa, Nijeriya kasa ce da aka gina ta a kan koyarwar Sunnah, don haka ba za su zura ido wasu su rika zagin Sahabbai da matan Manzon Allah (S) suna kallo ba.

Kungiyar Izala, musamman ta bakin shugabanninta, Shaikh Sani Yahaya Jingir, Shaikh Abdullahi Bala Lau da Shaikh Kabiru Gombe sun yi ta wa’azozi suna masu murna da abin da aka yi a Zariya. A rayawarsu, gwamnati ta yi hakan ne don ta murkushe wadanda suka tare masu gaba, ta maishe su manyan Malamai.

Tun bayan kama Shaikh Ibraheem Zakzaky da sojoji suka yi a ranar Litinin 14/12/2015, a ranar Alhamis 17/12/2015 Shugaban rundunar sojojin Nijeriya, Janar Tukur Y. Buratai ya bayyana wa manema labarai cewa sun mika Shaikh din inda ya dace don a hukunta shi. Ba a sake samun labarin halin da Shaikh Zakzaky da matarsa, Malama Zeenah ke ciki ba, sai a ranar 13 ga Junairun 2016, kimanin wata guda cur, a yayin da wani Kwamiti a karkashin Majalisar koli ta Harkokin addinin Musulunci a Nijeriya (NSCIA), wacce ta hada da Farfesa Dahiru Yahya, suka gana da Shaikh din a inda ake tsare da shi a Abuja.

Baya ga matakin Muzahara da addu’a, wadanne matakai ne almajiran Shaikh Zakzaky suka rika bi a tsawon shekaru ukun nan don ganin an tabbatar masu da adalci an saki Jagoransu? Ku biyo mu don jin bitar su.

Shekaru 3 Da Kisan Kiyashin Zariya (1)

Daga Saifullahi M. Kabir

WAIWAYE

Kimanin shekaru tara da suka gabata, gwamnatin Nijeriya bisa umurnin tsohon Shugaban kasa, Marigayi Umaru Musa ’Yara’aduwa, ta yi shiri na musamman don murkushe Harkar Musulunci a Nijeriya ta hanyar kashe Jagoranta Shaikh Ibraheem Zakzaky da tarwatsa dukkan dandazon mabiyansa.

Gidan Shaikh Ibraheem Zakzaky da sojoji suka rusa. 

A wancan lokacin, sun tsara cewa, za su saka bam ne a gidan Shaikh Zakzaky, sai ya zama cikin sauki shi da dukkan iyalansa sun rasu. A yayin da mabiya suka fito da nufin yin Allah wadai da wannan mummunan aikin, sai su bude wuta a kan su, kamar dai yadda suka yi ga wasu mutane da aka kira su da suna ’yan kungiyar Boko Haram a Jihohin Arewa-maso-gabashin Nijeriya a shekarar 2009.

Wannan yunkurin na gwamnatin ’Yar’aduwa ya bi ruwa ne bayan da Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya samu cikakken rahoton zaman sirrin da suka tsara aiwatar da wannan danyen aikin, tare da kwafin takardar sirri (blueprint) din gwamnati kan yadda ta tsara za ta aiwatar da kisan-kiyashin.

Shaikh Zakzaky bai yi jinkiri ba wajen sanarwa da duniya halin da ake ciki, a wajen Tafsirin Alkur’ani na watan Ramadanan 1430 a FIC, Zariya.

Duk da fallasa cewa, jami’an tsaro na shirin yin kisan-kiyashi a kan ’yan’uwa Musulmi da Shaikh Zakzaky ya yi a wannan lokacin, bai hana jami’an tsaron bude wa masu Muzaharar nuna goyon bayan Palasdinawa wuta a Zariya ba a ranar Juma’ar karshen Ramadan din wannan shekarar, wacce ta dace da 18/9/2009, inda suka kashe mutum biyu, tare da jikkata gomomi a daidai kofar Doka, Zariya.

Bayan rasuwar Marigayi Umaru Musa ’Yar’aduwa a ranar 5/5/2010, da yake kamar yadda Shaikh Zakzaky ya sha fada karara cewa, wasu ayyanannun kasashe ne suke da nufin a kashe masu shi, a kuma kawo karshen Harkar Musulunci a Nijeriya, kasancewar suna kallon ta a matsayin barazana gare su daga nufinsu na sake mamaye kasar nan da dibar arzikin cikinta. Don haka sai kwangilar kashe shi ta komo hannun Shugaban kasa Goodluck Jonathan.

Da farko kasashen da ke nufin ganin bayan Shaikh Zakzaky da da’awarsa, wanda suka hada da Amurka da Isra’ila, sun ba da kwangilar hakan ne ga wani Baturen Birtaniya, mazaunin kasar Amurka, mai suna Patrick William, wanda aka ce yana da kamfani na musamman don yin kisan mummuke ga duk wanda ake bukatar kashewa a duniya.

Patrick ya samu cikakken iko na amfani da wasu jami’an tsaron kasar nan a duk sad da yake bukata, inda suka rika shirin su harbe Shaikh Zakzaky, musamman a kan hanyarsa ta zuwa Husainiyyah Bakiyyatullah, inda yake bayar da karatu. Sai dai, hakan ya ci masu tura, a yayin da a ranar Mauludin Manzon Allah (S) na shekarar 1433 (19/2/2012), Shaikh Ibraheem Zakzaky ya fallasa wannan shirin, ya kuma yi wa Patrick da wadanda suka ba shi aikin albishir da rashin cikar burinsu.

Shaikh Zakzaky yake cewa; “Duk ranar da Allah ya kaddara min ajali, ya kuma zama shahada ya kaddara min, kuma ya zama kai Patrick kai ne makashina, zan yi wa kaina kyakkyawan albishir, in ce Alhamdulillah! Na gode wa Allah da ya zama kafiri tantiri irin ka ne aka ba shi kwangilar kashe ni. Albishirinka! Kai kuma ba za ka rayu bayana ba, ko shekara ma ba za ka yi ba. Wannan ma idan ka ga an kashe ni ajalina ne ya yi, kuma ko a kashe ni ko in mutu, wani abu guda shi ne, addinin yana nan, ruhin addinin kuma yana nan. Shi wannan ba ku isa ku kashe ba!”

Daga baya, kwangilar kashe Shaikh Zakzaky da murkushe Harkar Musulunci ta koma kai tsaye hannun Jonathan, tare da mataimakinsa Namadi Sambo. Kamar yadda a wani jawabinsa a shekarar 2013 Shaikh Zakzaky yake bayyanawa: “To, kuma yanzu sun sanar da shi Shugaban kasa da mataimakinsa, duk an sanar da su, kuma sun yarda sun saka hannu a kan sun amince za a kawar da al-Zakzaky.”

Don haka ya zama dare da rana, kowane lokaci, musamman a karshen mulkin Jonathan, Shaikh Zakzaky na faman tsallake yunkurin kisa ne daga jami’an tsaro. Har ma a ranar bikin Nisfu Sha’aban din shekarar 1435 (2014) yake cewa: “Kullum cikin tsallake hari muke daga wadannan miyagun mutanen. Yunkurinsu kullum shi ne ya za a yi su ga sun kashe mu… To, amma ranmu ba shi a hannunsu, yana hannun Allah ne. Allah (T) ne mai rayawa. Da a ce ranmu na hannunsu ne, ai da tuni sun zare. Tun da tuntuni suna ta faman bakin ciki, ga abu ba su so, ga shi yana ta habaka.”

A ranar Juma’ar karshen watan Ramadan, a kokarinsu na murkushe Harkar Musulunci, sojojin Nijeriya sun dira a kan almajiran Shaikh Zakzaky a daidai PZ da ke Zariya, a yayin da suke gudanar da Muzaharar nuna goyon bayan Palasdinawa, inda suka kashe mutane 34, cikin su har da ’ya’yan Shaikh Zakzaky su uku, wadanda sun kama su ne da ransu da lafiyarsu suka tafi da su barikin Basawa, suka kashe su ta hanyar azabtarwa.

Sojoji tun a wannan lokacin sun yi niyyar su samu dama ne da za su ci gaba da kashe-kashe, har su kai ga Shaikh Zakzaky. Shi ya sa ma bayan sun yi wannan kisan-kiyashin, sun ta zura ido su ga ko mabiya Shaikh Zakzaky za su fito Muzahara don yin Allah-wadai da harin, sai su yi amfani da wannan damar wajen ci gaba da kashe su, tare da bi gida-gida suna kisa da sunan suna neman ’yan’uwa Musulmin. A wannan lokacin, sai Shaikh Zakzaky ya hana ’yan’uwa fita don yin komai.

Duk da haka, sai sojojin suka rika yada farfaganda da labaran karya, cewa ’yan’uwa Musulmi suna shirin za su mai da martani ga sojoji a barikinsu. Karyar da ba ta samu wajen zama ba a kwakwalen wadanda suka san Harkar Musulunci a tsawon shekaru fiye da 30 a matsayin tafiyar addini marar tashin hankali ko neman fada da kowa.

A ranar 22 ga Muharram 1436 (14/11/2014), bayan kammala zaman juyayin Ashura, Shaikh Zakzaky ya ba da labari cewa: “Dazun abin da aka ce mana; an tara Sojoji a sansaninsu, an ce masu; Al-Zakzaky zai yi bore, saboda haka su zama cikin shiri komai na iya faruwa. To, me ya kawo sunan Al-Zakzaky kai da kake ‘training?’ Kuma in ya yi bore, ina ruwanka da boren? Na dauka idan ma wani abu ne, ba aikin ’yan sanda ba ne? Sai dai in Dan sanda ya gayyace ka, ka taimaka masa, amma Soja da bindiga an ce masa Al-Zakzaky zai yi bore ya zama cikin shiri, komai na iya faruwa.

“Wannan abin da aka gaya masu dazun ke nan. Kuma aka ce su rike bindigoginsu, yanzu haka bindigogin na hannunsu, kuma suna nan yanzu cikin shiri. Kuma sun shigo (Zariya) motoci ne ba kadan ba. Tun kwanaki suna ta shigowa, har da inda aka ga mota 10 da Turawa zalla, sun shigo sun je barikin Basawa shekaranjiya wancan. Kuma yanzu mota 10, mota 20 duk suna shiga. To, kuma duk ba za mu damu ba. Amma me ya kawo sunan Al-Zakzaky? Da yake shi soja ana masa tarbiyya ne da cewa; su mutanen gari sune abokanan gabansa. Za shi ya yi kisan kai ne kawai.”

Shaikh Zakzaky ya ci gaba da cewa: “To, wala Allah su zama cikin shirin, kila sun shirya suna da wani ‘unit’ wanda zai sa bakin kaya, ya je ya yi ta’addanci, su ce; ‘to, ka gani? Dama mun gaya muku.’ Daga nan kuma sai su shigo gari, su shiga kisan kai.”

Tun daga wannan lokacin, sojoji a karkashin mulkin Jonathan suka rika kai farmaki a kan Shaikh Zakzaky, a kowane lokaci suna da nufin su bude masa wuta, ko dai a kan hanyarsa ko kuma a gidansa. Haka ne ma ya sa wani lokacin sukan shigo cikin unguwar Gyallesu da tsakar dare, amma idan suka ga komai dare unguwar ba ta rabuwa da ’yan’uwa da suke ba da kariya, sai su juya a guje.

Shaikh Zakzaky ya tsallake yunkurin kisa daga gwamnatin Jonathan fiye da sau 30 a lokuta daban-daban. Ta kai ga yakan canza hanya idan aka gano sun yi kwanton-bauna a hanyar da aka saba bi zuwa wajen karatu. Haka aka rika fama har zuwa lokacin da aka samu canjin gwamnati. Ya zama Shugaba kasa Muhammadu Buhari ke mulki a karkashin jam’iyyar APC, a shekarar 2015.

A farko, kamar komai zai tafi lafiya kalau, bayan ’yan watanni da hawansa, musamman bayan da wata tashar ‘satilayit’ mallakar kasar Saudiyya, mai suna WISAL TV, ta fitar da wani rahoto, wanda a cikinsa ta gargadi hukumomin Nijeriya a kan bari da suka yi Shi’a na ya]uwa a kasar, ta kuma yi kira gare su da su dakile yaduwar Shi’ancin, kawai sai aka fara ganin hare-hare a kan ’yan’uwa Musulmi, harin kusa da kisan-kiyashin Zariya shi ne harin bom, da aka turo wasu yara cikin masu Tattakin Arba’in din Imam Husain (AS) daga yankin Kano, wanda ya yi sanadiyyar kashe mutum 23 da jikkata gomomi.

Duk da yake kungiyar Boko Haram ta dauki alhakin harin, har ma ta yi barazanar murkushe Shi’a, amma Shaikh Zakzaky ya dora alhakin harin ne kan jami’an tsaro, bisa dalilan da ya bayyana a cikin jawabinsa na ranar Arba’in, wanda aka gudanar a ranar Alhamis, 3 ga Disambar 2015.

Ba a samu wata murya daga bangaren gwamnati, ko jami’an tsaro da ta musanta zargin da Shaikh Zakzaky ya yi a wannan lokacin ba, sai kawai martanin da sojoji suka bayar kwanaki tara bayan wannan jawabin, wanda shi ne ‘Kisan-Kiyashin Zariya’.


KISAN-KIYASHIN ZARIYA

A ranar Alhamis, 28 ga Safar 1437, daidai da 10/12/2015, bayan kammala zaman juyayin ranar wafatin Manzon Allah (S), Shaikh Zakzaky ya bayar da sanarwar taron saka tutar Maulud, wanda za a gudanar a yammacin ranar Asabar 1 ga watan Rabi’ul Awwal, 1437 (12/2/2015).

A shekarun da suke gabanin nan, sojoji sun saba gabatar da bikin yaye sabbin kuratan sojojin a Zariya a duk karshen shekara, a ranar Juma’a da safe. Sai dai a wannan shekarar, sai suka mai da shi ranar Asabar 12 ga Disambar 2015, kuma da yammaci, maimako Juma’a da safe kamar yadda suka saba gabatarwa a tsawon shekaru. Wannan ya ba su damar ya zama rana da lokacin bikin nasu ya yi daidai da na taron sauya tutar Mauludi da Harkar Musulunci ta ayyana za ta gabatar a Husainiyyah Bakiyyatullah a wannan ranar.

Harkar Musulunci ba ta yi tunanin dage taronta a wannan ranar ba, ganin cewa wuraren da za a gudanar da taruka biyun ba kusa suke ba, don haka babu wani abu da zai hada masu gudanar da taron sauya tuta da masu yayen sabbin kurata. Kuma su wadannan sun saba yi ne da safe, bikin sanya tuta kuwa ana yi ne wajen karfe 5:00 na yamma.

Sai dai wani abu da ba a yi zato, ko tsammani ba, da misalin karfe 12:15 na ranar Asabar din, wata babban motar Sojoji ta zo ta sauke wasu dandazon kuratan sojoji dauke da makamai, tare da akwatun harsashi, a daidai gaban Husainiyyah Bakiyyatullah. Abin da ya yi matukar ba ’yan’uwan da ke wajen mamaki.

An yi kokarin tuntubar su dalilin kawo su gaban Husainiyyah a daidai wannan lokacin, amma sai suka fara harbi a sama. Daga baya sai suka fara kewaye wajen suna harbi, yayin da ’yan’uwa suka bu}ace su, su matsa daga gaban Husainiyya.

Bayan kamar awa guda da faruwar haka, misalin karfe 1:00nr, sai ga tawagar Janar Tukur Yusuf Buratai ta biyo ta wajen Husainiyyar da sunan wucewa. Kai ka ce tawagar ta Shugaban rundunar sojojin Nijeriya ba ta san abin da ya faru a wannan wajen kimamin awa guda da ta gabata ba, wanda a ka’idar tsaro zai tilasta masu barin bin hanyar da samun wata da babu kowane irin barazana.

Zuwan su, tare da masu daukar hotuna cikin kakin sojoji, sai suka shirya wani abu kamar wasan kwaikwayo. Suka yi fuska, tare da nuna rashin sanin faruwar wani abu da wasu kuratan sojoji suka gabatar a wajen kafin zuwan su. A yayin da wasu ’yan’uwa suka tunkare su don su ji ko da me suka sake dawowa wajen? Sai wasu jami’an tsaro a cikin rigar ’yan’uwa Musulmi (kamar yadda Shugaban DSS na Zariya ya bayyana a gaban JCI cewa akwai mutanensu a cikin ’yan’uwa a wannan ranar a Husainiyyar) suka rima ihu, tare da daddaga sanduna. Nan take sojojin suka bude wuta kan mai uwa-da-wabi.

Bayan bude wutar, tawagar ta Buratai ta wuce, sai wadancan kuratan sojojin da aka kawo da farko suka ci gaba da kewaye Husainiyyah, aka rika maro masu karfi. A yayin da suka bi suka kwashe gawawwakin wadanda suka harba, suna goge jini da harsasan da ke kan hanya.

A shirin rana na BBC a wannan ranar, sai ga hirar Kakakin rundunar soja na wancan lokacin, S.U Kukasheka, inda yake bayyana cewa, an yi kwanton-bauna ga Shugaban rundunar sojoji ne, har ma ya tsallake rijiya da baya. Zargin da nan take Shugaban Jagoran Harkar Musulunci Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky ya musanta.

Kamar yadda aka gani cikin cikakken bidiyon wannan harin da Harka Musulunci ta saki daga baya, Soja sun ci gaba da kewaye Husainiyyah, tare da harbin duk wanda suka samu a kewayenta, har zuwa marfe 5:00ny, lokacin da Gwamnan Kaduna, Nasiru Ahmad El-Rufa’i ya zo wajen.

Bayan magana da ya yi da Jagororin Sojin, sai ya yi gaba. Wucewarsa ke da wuya suka kara tsananta harbe-harbe a Husainiyyar, tare da yunkurin shiganta ta kowane hali.

Ana cikin wannan halin har shigar dare, da misalin karfe 10:30 na dare, sai ga wasu sojojin sun kawo hari gidan Shaikh Ibraheem Zakzaky da ke unguwar Gyallesu, kilomita kusan biyar daga Husainiyyah Bakiyyatullah.

Zuwan su ke da wuya suka yi burki a daidai Banadeen da ke kan kwanar layin da zai kai mutum gidan Shaikh Zakzaky. Suka bude wuta a wani shagon mai shayi da ’yan’uwa suka taru suna shan shayi. Suka jefa wani abin fashewa a wani shagon, bayan wuta ta kama, sai suka rima amfani da hasken wutar wajen saitawa da harbe duk wanda suka gani a kan wannan layin.

Sojoji sun kwana suna harbi a wannan ranar Asabar 12 ga Disambar 2015 din, har zuwa wayewar garin Lahadi, inda suka kashe duk wani mutum da ke gidan Shaikh Zakzaky da suka hada maza, mata da kananan yara, tare da jikkata saura. Suka kuma watsa fetur a kan gawawwakin ’yan’uwa da kuma masu rauni da ake ajiye su a gidan Harisawa da ke kusa da gidan Shaikh Zakzaky, suka banka masu wuta suka kone murmus. Sannan suka tattaro gawawwakin wadanda suka kashe a kan layi, suka tara su waje guda, suka ba mutanen unguwa damar su caje aljihunsu su debi abin da suke so a jikinsu.

A asubahin ranar Lahadin, aka tura wasu sojojin makabartar Darur-Rahma, wanda ke tare da gine-ginen tarihi da aka yi su don yin fim din tarihin rayuwar Shehu Usman Fodiye, da kuma masallacin da aka gina na miliyoyin kudi a wajen.

Akwai ’yan’uwa da suka fito daga yankin Bauchi da nufin zuwa Gyallesu, amma da yake dare ya yi masu, sai suka yada zango a wajen da nufin safe su mara. Sun kashe duka da wadanda ke kula da wajen. Daga bisani suka banka wa wajen wuta, suka rusa shi.

Sun tsare duk hanyoyin shiga da fita Zariya, suna kamawa da hukunta wadanda suke zargi da zama almajiran Shaikh Zakzaky. A irin haka ne suka tsare motoci biyu a Unguwar Dogarawa da ke dauke ’yan’uwa da suka fito daga Tudun Wadar dankadai, Kano, suka bude masu wuta, suka kashe su duka, suka kwashe su suka kai Asibitin koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Shika, Zariya.

A daidai lokacin suke wannan ta’addancin a Gyallesu da Darur-Rahma, sun rima harba gurneti a kan ginin Husainiyyah, har suka samu dama suka shiga ciki, suka kashe da dama, suka harbi wasu, sannan suka kama su suka wurga a motoci suka tafi da su. Daga nan suka hau rusa ginin Husainiyyar.

Duk da wuta da suka saka wa gidan Shaikh Zakzaky bai fito ya mima masu wuya ba, gidan ya kwana yana ci da wuta, a yayin da ba su samu ganin sa ba sai a ranar Litini 14/12/2015, bayan sun rika saka sifika suna yekuwar cewa yau sun gama da Shi’a, Soja na cewa; “Al-Zakzaky ka fito ka yi saranda, ko mu maka kisan wulamanci.”

Ganin yadda gidan ya mone kurumus, sun dauka duk wanda ke ciki ya kone, don haka sai suka shiga gidan suna balle kofofi, har suka kai ga dakin da Shaikh Zakzaky, iyalansa da wasu almajiransa ke ciki, suka yi masu ruwan wuta.

A nan suka kashe ’ya’yansa guda uku, suka harbe shi a hannayensa da kafarsa da kuma idanunsa guda biyu. Suka kama shi tare da matarsa da ke tare da shi, ita ma cikin raunin harbi, suka fita da su.

Shaikh Zakzaky ya bayyana a wata hirar da ya yi da babban dansa, ta wayar tarho daga inda ake tsare da shi cewa; “Mu aka kawo wa hari, aka bu]e mana wuta, aka harbe mu da bindiga, aka kashe mutane sama da 1,000, ciki har da ’ya’yanmu. Ni da matata an harbe mu, ni an ja ni a kan gawar ’ya’yana ne. Sannan kuma aka kawo mu nan aka kulle duk cikar mu da harsasai a jikinmu. Yanzu haka muna fama da ciwo, duk jikinmu da harsasai.”

Kwanaki biyu bayan hakan, sai Gwamnan Kaduna, Nasiru El-Rufa’i ya umurci Hukumar KASUPDA tare da rakiyar jami’an tsaron Soji da ’yan sanda, suka rika bin duk wani gini da ke da alaka da Shaikh Zakzaky suka rusa shi. Bayan Husainiyyah da suka rusa, sun rusa gine-ginen Darur-Rahma da ke kauyen Dambo, Gidan Shaikh Zakzaky a Gyallesu, Fudiyyah Islamic Center a Dan Magaji da gidan da aka birne Mahaifiyar Shaikh Zakzaky a cikin Zariya.

Kisan-kiyashin Zariya ya yi sanadiyyar kashe ’yan’uwa Musulmi almajiran Shaikh Zakzaky fiye da mutum 1,000, tare da jikkata daruruwa, ciki har da wadanda sojoji suka kona su da ransu, fatar jikinsu ya salbe, Allah bai nufi kwanansu ya kare a sannan ba da kuma wadanda aka binne da ransu. Ya shafe iyalai da dama da suka hada uwa, uba da ’ya’yansu. Ya kuma ci rayukan tsofaffi, kananan yara, mata da samari daliban manyan Jami’o’i.

Tun daga ranar Asabar 14 ga Disambar 2015, wato 1 ga watan Rabi’ul Awwal, 1437, har zuwa yau 1 ga watan Rabi’ul Awwal, 1440, tsawon shekaru uku ke nan gwamnatin Nijeriya na ci gaba da tsare Shaikh Zakzaky da daruruwan almajiransa.

Ku biyo mu don karanta bitar abubuwan da suka biyo baya da abubuwan da suka faru daki-daki a tsawon wadannan shekaru ukun, tun bayan faruwar wannan harin.

January 03, 2019

Matakai Kafin Kisan Kai A Dokar Nijeriya



Daga Jawabin Jagora, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H). 

Daga Dalilan Jami'an Tsaro Na Ta Da Hargitsi A Kasar Nan

Saurari wani Jawabin Shaikh Zakzaky a kan yadda jami'an tsaro a Nijeriya ke amfani da rikici da ta da hargitsi don samun kudade.

WATAN DISAMBAR 2015 A KUNDIN ADANA NA

WATAN DISAMBAR 2015 A KUNDIN ADANA BAYANAI NA

Daga Saifullahi M. Kabir

Bayan na na kammala fitar da muhimman abubuwa guda 40 da suka faru a shekarar 2018 da suka shafi Harkar Musulunci da motsin fafutukar ganin an saki Jagora, Sayyid Zakzaky (H). Wasu ‘yan uwa sun bukaci a yi bitan sauran shekarun da suka gabata, musamman daga Disambar 2015, da shekarar 2016 da kuma 2017 ma a bisa jerin raneku.



1- Ranar 2 ga watan Disambar 2015 aka kammala Tattakin Arba’in din Imam Husaini (AS), wanda a cikinsa aka samu Shahidai 23 daga masu tasowa ta bangaren Kano zuwa Zariya, sakamakon Bom da jami’an tsaron gwamnatin Buhari suka dasa a jikin wasu yara guda biyu. Na farko ya tashi, na biyun aka kwance shi kafin ya tashi.

2- Ranar 12-14/12/2015 aka yi Waki’ar Zariya, wanda sojoji suka dira a kan ‘yan uwa Musulmi almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky (H), suka kashe fiye da mutum 1000 a cikin kwanaki 2, suka kona tare da rushe gidan Shaikh Zakzaky da wasu gine-gine akalla guda bakwai da suke da alaka da Shaikh din. Suka kashe ‘ya’yansa uku da ‘yan uwansa da yayarsa mace, suka harbe shi da matarsa suka kama su suka tafi da su cikin jinni, har yau shekaru uku kenan suna tsare da su bisa zalunci.

3- Ranar Litini 14/12/2015 Manjo-Janar Adeniyi Oyebade, shugaban rundunar soja ta 1 da ke Kaduna, wanda shi ya jagoranci duk ‘operations’ din da aka yi na kisan kiyashin Zariya, ya gana da manema labarai, inda ya bayyana musu cewa shi ya ba da umurnin a mamaye gidan Malam, Husainiyyah da kuma Darur Rahma a kawo masa Shaikh Zakzaky. Ya kuma ce Shaikh Zakzaky da matarsa Zeenah suna nan a raye, a ‘Protective Custody’.

4- Ranar Talata 15/12/2015 ‘yan uwa suka gudanar da gagarumar Muzaharar kira a saki Shaikh Zakzaky tare da yin Allah-wadai da kisan kiyashin Zariya a garin Kaduna. ‘yan sanda sun budewa ‘yan uwa wuta, inda suka kashe mutum 13. Mutum 7 daga cikin Shahidan an kashe su ne nan take, a yayin da mutum 6 ‘yan sanda sun tafi da su da ransu ne suka kashe su, sai bayan Waki’ar da kwana shida suka ba da gawarwakinsu akai musu Jana’iza.

5- Ranar Laraba 16/12/2015 kafar watsa labarai ta FARS NEWS AGENCY ta ruwaito cewa Sarkin Saudiyyah, Salman Bin Abdul’azeez ya kira Shugaban kasar Nijeriya, Muhammadu Buhari ya taya shi murna tare da bayyana kisan kiyashin Zariya a matsayin Yaqi da Ta’addanci.
 A wannan ranar ne sojoji suka kwashe duk gawarwakin da suka kashe daga asibitin Shika, da kuma wadanda suka aje su a Depo dinsu a Zariya, suka kai su wani kauye da ake kira Mando a bayan garin Kaduna suka bizne su cikin dare. Kamar yadda sakataren gwamnatin jihar Kaduna ya tabbatar a gaban kwamitin JCI.

6- Ranar Alhamis 17/12/2015 ne Gwamnan jihar Kaduna, Nasiru Elrufa’I ya fito a gidan Rediyon jihar Kaduna yana magana a kan matsayar gwamnatinsa a kan kisan kiyashin da sojoji suka yi a Zariya. Ya yi ikirarin cewa Harkar Musulunci tana mamaye gidajen mutane tai musu barazanar kwace su, kuma tana gina waje ba bisa izini ba, sannan ‘yan Harkar Musuluncin suna hawa su yi tafiya a kan Titin Gwamnati har su yi amfani da makarantun gwamnati (a yayin da suke Tattakin juyayin Shahadar jikan Manzon Allah (S), Imam Husaini (AS). Bayan ya jera zarge-zarge da kazafofinsa, sai yace zai kafa kwamitin bincike kana bin da ya faru a Zariya.
 A irin wannan ranar ne kuma shugaban sojojin Nijeriya, Tukur Yusuf Buratai ya bayyana cewa sun mika Shaikh Zakzaky ga inda ya dace don a hukunta shi.

7- Ranar Juma’a 18/12/2018 aka gudanar da Muzaharorin Allah-wadai da kisan kiyashin Zariya da sojojin Nijeriya suka aiwatar a kusan kowane bangare na kasashen Duniya. A Pakistan kawai an yi Muzahara a garuruwa kusan 50. Haka ma a Indiya da Iran, Iraq, NewYork, Istambul, Canada, da sauransu, bare kuma a Nijeriya, kauye da birni ‘yan uwa sun fita suna Allah-wadai, tare da kira a saki Jagora, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H).
 A wannan ranar wasu daidaikun mutane sun rika Allah-wadai da ta’addancin sojojin gwamnatin Nijeriya, kamar tsohon ministan harkokin jiragen sama na Nijeriya, Femi Fani Kayode, a wani rubutu da ya sake a kafar sadarwa, ya bayyana abin da ya faru a matsayin shiryayye kuma tsararren abu, inda ya kuma nuna takaicinsa kan yadda sojoji suka kona gidaje bayan sun kashe ‘yan kasa wadanda basu dauke da makami. Ya kuma jaddadawa Buhari da Buratai cewa kotun ICC tana jiransu. Shima Ministan Matasa da wasanni na kasa, Solomon Dalung ya yi Allah wadai da abin da ya faru, kamar yadda wata kafa ta thewistleng.com ta ruwaito.
 A wannan ranar Fadar Shugaban kasa ta sanar da cewa rikicin ba abu ne da ya shafe ta ba, ya shafi sojoji ne kawai, don haka ba za su ce uffan ba.

8- Ranar 19/12/2015, Gwamnonin Arewacin Nijeriya a karkashin shugabancin Kasim Shettima suka yi zama a Kaduna a kan yadda za su bullowa Harkar Musulunci da ‘yan Harkar a jihohinsu, musamman ma ta fuskacin hana su fita Muzaharori. A

9- A ranar Lahadi zuwa Talata 20-22/12/2015 ne gwamnatin jihar Kaduna ta tura hukumar KASUPDA tare da jami’an tsaro suka je suka karisa rusa Husainiyyah Bakiyyatullah, da ginin NTC da shagunan tsallaken Husainiyyah, da Darur Rahma da masallacin da ke cikinsa, suka je unguwar Jushi a cikin garin Zariya suka rushe gidan da aka bizne mahaifiyar Shaikh Zakzaky, suka kuma rushe Fudiyyah Islamic Center da ke unguwar Dan-Magaji a Zariya.

10- Ranar 21/12/2015 ne wani ‘audio’ ya bayyana na Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, inda yake yabawa da kisan kiyashin da aka yi ma ‘yan Shi’a a cewarsa. Ya bayyana ‘yan Shi’a a matsayin wadanda suke zagin Sahabbai, kuma yace Arewacin Nijeriya Ahlussunnah ne ya kafa shi, don haka ba za su cigaba da zura ido ‘Yan Shi’a suna zagin Sahabbai ba. Ya jingina duk kisan da su Janar Oyebade suka yi a matsayin sakamakon zagin sahabbai ne.

11- Ranar 22/12/2015 Kungiyar Biafara suka fitar da takardar Allah wadai da kisan da aka ma ‘yan kasa marasa dauke da makami a Zariya, ta hannun wani jigo a kungiyar mai suna Ndubuisi Anukwuem.
 Shima wani babban Lauya mai rajin kare hakkin dan Adam, Mista Femi Falana SAN ya yi tir da harin na Zariya a wani shiri ‘Breakfast show’ a gidan TV din Channels TV. Falana ya jaddada cewa dole ne gwamnatin Nijeriya ta biya diyyar wannan barnar da ta yi, ta kuma hukunta duk ofisoshin da suke da hannu wajen kisan-kiyashin na Zariya. Sannan kuma ya ba da shawarar a saka darussan da suka shafi ‘Yancin Dan Adam a makarantun hoton sojoji.

12- Ranar 24/12/2015 Kungiyar Iyamurai ta Igbo-Mandate Congress (IMC) ta yi Allah-wadai, tare da yin kira ga Buhari a kan ya ba Shaikh Zakzaky hakuri a kana bin da sojoji sukai masa. Sun yi kiran ne ta bakin babban daraktansu, Rev. Obinna Akukwe.
 Wata Kungiya mai suna ‘Social Party of Nigeria’ ta hannun kakakinta, Segun Sango, ita ma ta yi kira ga shugaban sojoji, Buratai ya sauka daga mukaminsa saboda abin kunyar da sojoji suka yi na kashe yan kasa marasa dauke da makami har daruruwa a cikin kwanaki biyu. Sun kuma yi Allah-wadai da hana Muzahara da afkawa masu yinsa da gwamnatin jihar Kaduna ke yi, inda suka ce ‘Hana mutane zanga-zangar lumana a kan hakkinsu goyawa zalunci baya ne.’
 Haka ma kungiyar ‘Non-Profit Making Organisation’ ta hannun Daraktanta, Josept Otteh, ta yi kira ga Buratai ya sauka daga mukaminsa don a bincike shi. Suka kuma bayyana harin a matsayin haramtacce wanda ya sabawa kundin tsarin mulkin kasa.

13- Ranar 28/12/2015 ne kungiyar Malamai da Limamai (na Wahabiyawa) na jihar Kaduna suka ziyarci gwamnan Kaduna, Elrufa’I a kan kudirinsu na mara masa baya a kan cigaba da fada da Shi’a (sunan da suka fi kiran Harkar Musulunci da shi).

Wadannan a takaice sune abubuwan da Kundi na ya iya taskacewa sun auku a jere a watan Disambar 2015 da suka shafi Harkar Musulunci ko Waki’ar Zariya. Saura na shekarar 2016 da 2017, in Allah ya bani iko insha Allah.