March 02, 2019
Shekaru 3 Da Kisan-kiyashin Zariya (10)
Daga Saifullahi M. Kabir
KAWO WA SHAIKH ZAKZAKY SAMMACIN KOTU
Bayan hakan da ’yan kwanaki, a ranar 2/5/18 sai ga wani ‘Registerer’ din kotu daga Kaduna ya zo inda ake tsare da Shaikh Zakzaky, wai ya kawo sammacin kotu.
Kamar yadda wannan din ma Shaikh Zakzaky ya sanar da Sayyid Muhammad ta waya labarin abin da ya faru, Shaikh din ya bayyana cewa bai karbi takardar ba, kuma bai sanya hannu ba, har ma ya ce a mayar da ita, a ce ba zai karba ba, kuma ba zai sa hannu ba, kuma ba zai je kotun ba, sai dai in za a kai shi da bakin bindiga!
Shaikh Zakzaky ya fada wa Sayyid Muhammad cewa; “To, a nan sai na fa]a wa (mai kawo sammacin) cewa, ka gane wannan al’amari fa, mu aka kawo wa hari, aka bude mana wuta, aka harbe mu da bindiga, aka kashe mutane sama da 1,000, ciki har da ’ya’yanmu. Ni da matata an harbe mu, ni an ja ni a kan gawar ’ya’yana ne. Sannan kuma aka kawo mu nan aka kulle duk cikar mu da harsasai a jikinmu. Yanzu haka muna fama da ciwo duk jikinmu da harsasai.”
Ya ci gaba da cewa; “To, sannan mu muka kai kara kotu, muka ce don me ake tsare da mu? Suka tura Lauyan gwamnati, ya ce suna tsare da mu ne domin su kare mu. Kotu bayan ta gama jin kowane bangare ta fitar da hukunci, cewa, lallai ba wata doka a Nijeriya ko wacce Nijeriya ta saka ma hannu (ta kasar waje), wadda ta ba da dama gwamnati ta tsare wani mutum da sunan tana kare shi. Saboda haka (kotu) ta hukunta cewa a sake mu ba tare da gindaya shara]i ba. Yau an kwashe kusan shekara da watanni shiru, ba su bi umurnin wannan kotun ba. Sannan kuma yanzu ka zo ka ce wai ka kawo za a kai ni kara? Wannan bai da ma’ana ai.”
A nan sai shi mai kawo sammacin ya nemi ya yi jayayya da Shaikh Zakzaky a kan sai fa Shaikh din ya saka hannu a wannan takardar, don haka Shaikh ya yi masa magana mai zafi. Cikin abin da Shaikh Zakzaky ya fada masa; “To in kai ma bangaren ‘problem’ din ne (zaluncin da ake mana), don ka sani, kun yi kadan! Tunda da bindiga kuka harbe mu kuka zo da mu nan, to yanzu ku zo da bindigar ma ku sake harbin, ko ku yi abin da kuka so.”
Shaikh Zakzaky ya ce; “Sai ya nemi ya fita ya bar takardun. Sai muka ce masa, ba ka isa ba sai ka dauki abinka. Daya daga cikin ma’aikatansu na DSS sai ya Dauka, sai muka ce a’a, sai an ba shi. Lallai sai an ba shi takardun. Sannan dole ya karbi takardun. Kuma muka raka shi ya tsaya a waje, duk sai suka taru (su ’yan security) suka hadu, shi kadai ne fa (dan sakon), muka tsaya a kofar wajen muka ce lallai sai an fita da shi. To, a nan ne ma nake ce wa shi wanda ya zo da shi, fita da wannan ]an iskan daga nan, na ga shi ‘is part of’ abin. Ka fita da shi da wuri. Ya kwashe takardunsa aka sa shi ya shiga mota aka yi waje da shi. Sai da muka tabbatar motar ta tafi, ta bace da gani, sannan muka dawo.”
Shaikh ya ci gaba da cewa; “To, ni abin da ban gane ba shi ne, shi wannan mutumin ya ba ni mamaki. Shi ya zo a matsayin Dan sako ne, amma wai sai an sa hannu. To, kuma ka ga kamar yadda nake ce maka, ka ga su mutanen nan, su suna nan a kan bin umurnin abin da aka ba su ne. Dama tuntuni su Saudi-Arabiyya da suka biya su suna ta ba su umurnin cewa, lallai a kashe ni. Lallai a kashe ni kawai. Kuma tuntuni suke masu wannan. To, kuma ga dukkan alamu tunda abin da suke nufi shi ne tunda su sukan kai mutum kotu ne a Saudi-Arabiyya, su yanke masa hukunci su ce sun kashe shi, to shi ma abin da suka ba su umurnin yanzu su yi ke nan.”
Ya kara da cewa; “To, lokacin da suka bude mana wuta ai ba kotu suka kai mu suka yanke mana hukunci ba, sun zo sun bude wuta ne. Yanzu ma mene nasu na zuwa su kai kotu sannan su yanke mana hukuncin kisa? Yanzu su zo da bindigar mana su harbe, me ya rage kuma?”
Ya ce; “Kuma alhali ba yadda za a yi bayan kotu ta ce, tsare mun da ake yi ba bisa ka’ida ba ne, a sake mu, sannan wani ya zo don rashin kunya ya ce wai kuma yana karar mu a kotu. Wace kotu kuma bayan ta yanke hukunci? Ana wani hukuncin ne a kan wani hukuncin? Hukuncin da ba ku bi ba, an riga an ba ku umurni ba ku bi ba, sannan kuma ku ce ku kuna wata kara? In dai ba bindigar nan za ku sa (ba)! Sai dai in bindiga za su saka kamar yadda suka saka mana da farko. Amma Wallahi sun yi ladan, su ce wai mu mu tashi wai mu je, wai akwai wata tsiya wai ita kotu, wai tana mana hukunci, Wallahi sun yi kadan. In dai bindiga ce tana nan a hannunsu, kuma mu ma jininmu yana nan a tare da mu, saboda haka ku zo ku gama shekarwa. Zance ya kare.”
KAI SHAIKH ZAKZAKY KOTU A KADUNA DAGA ABUJA
To, bayan wannan kawo sammacin da ya faru a ranar 2/5/2018, kwatsam da subahin ranar Talata, 15/5/2018, sai kuwa jami’an tsaro suka zo don tafiya da Shaikh Zakzaky kotu da bakin bindiga.
A wannan ranar gamayyar jami’an tsaro sun zo inda ake tsare da Shaikh Zakzaky da misalin karfi 5:00 da mintoci, na safe, a daidai lokacin Shaikh ya sallame Sallar Asubah yana addu’o’in bayan Sallar (Ta’akibat), sai kawai suka ji ana buge-bugen kofofi, tare da kabbarori. Ashe suna yunkurin balla kofar dakin da yaran Shaikh Zakzaky suke ne, a yayin da yaran suke kabbara.
Majiya mai tushe ta tabbatar mana cewa, bayan sun haura inda Shaikh Zakzaky yake, sun bugi kofar dakin da yake ne suka balle, suka shiga suka rika haukataku, har wasunsu na cewa yana jiran mene? A yayin da Shaikh Zakzaky ke kokarin saka rawani, suna rirrike shi suna kokarin fita da shi da karfi. Da kyar Shaikh ya samu ya saka takalminsa a yayin da suke jan sa, ba su bari ya saka abayarsa ba sai bayan da suka fito da shi.
Haka suka fito da Shaikh Zakzaky suna rirrike da shi, ba su dubi tsufansa a matsayinsa na Dattijo mai shekara 67 ba, ba su yi la’akari da raunukan da ke jikinsa na harbin da sojoji suka masa a kafa, hannu da ido ba, suka rika musguna masa, har suka sanya shi a tsakiyar mota a baya, gefe da gefensa a cikin motar akwai jami’an tsaro kowanne rike da bindiga har da bindigar da suke saka wa mutum ta yi masa shokin.
A yayin da ita ma Malama Zeenah, suka shiga suka fito da ita suka saka ta a wata mota ta daban. Haka ma sauran ’yan’uwan da suke tare da su, su uku, suka saka wa biyu ankwa a hannayensu, dayar kuwa bayan ankwar hannu har da mari a kafa. Suka shigar da kowaccensu mota aka tafi da su Kaduna.
A haka suka kai Shaikh Zakzaky kotu da karfin tsiya, da bakin bindiga a wannan ranar Talata din. Ranar ta dace da karshen watan Sha’aban din shekarar 1439 ne, inda daga nan aka fara yi wa su Shaikh Zakzaky haramtacciyar Shari’a.
HARAMTACCIYAR SHARI’A A KADUNA
A wannan ranar da aka dauko su Shaikh daga Abuja, kai tsaye an taho da su wata babbar kotu ne a Kaduna, a yayin da shi kansa Shaikh Zakzaky din sai da aka isa aka bude motar ya sauka sai ya gane ashe duk wannan haukar da ake masu za a kawo su kotu ne.
Bayan shiga kotu aka fara Shari’a, a yayin da ya kasance tunda ana da labarin yiwuwar kawo Shaikh sin kotu a wannan ranar, tuni wasu daga Lauyoyin Shaikh Zakzaky da suka hada da Barista Maxwell sun hallara a kotun. Haka su ma Lauyoyin gwamnatin Kaduna, karkashin Barista Bayaro Dari sun kasance a kotun.
A nan Alkali ya nemi ganin ragowar mutum biyu da ake karar da su, sai Lauyan Gwamnati, Bayero ya nemi Alkalin ya ba shi dama kafin zama na gaba don ya isar da takardar sammaci ga ragowar mutum biyun a Kano da Katsina.
Lauyoyin Shaikh Zakzaky sun nemi kotun ta ba da belinsa da matarsa a wannan ranar, amma sai Alkalin ya ce sai dai su rubuto takardar neman belin su kawo wa kotu a rubuce. Sannan Jojin ya yi tambayar a ina ake tsare da su Shaikh Zakzaky da matarsa a yanzu? Aka sanar da shi cewa suna hannun DSS ne. Sai ya yi umurni a ci gaba da tsare su a hannun DSS din, maimakon mai da su gidan yari.
Daga nan ne kotun ta fara tattauna batun daga Shari’ar da sanya sabuwar ranar da za a dawo kotu don ci gaba da Shari’ar. Alkalin ya saka cewa za a dawo bayan mako biyu ne, amma sai Shaikh Zakzaky ya kira Lauyansa ya tambaye shi, bayan mako biyu din za mu zo kotu? Ya ce masa eh za ku zo. Sai Shaikh ya ce masa a bari sai bayan Ramadan! Sai aka ce yaushe ne Ramadan din? Shaikh Zakzaky ya ce tana iya yiwuwa ya zama jibi 17/5/18 ne, kuma za a kwana kamar 30 ana Ramadan, bayan Sallah sai a dawo. Nan Alkalin ya ce ya yi yawa. Lauyan ya ce masa haka wanda muke karewa yake bukata. Don haka sai Alkalin ya ce za a daga zuwa 21/6/2018. Aka ce ya yi.
Ranar Laraba 20/6/18 ana gobe komawa kotu, ’yan’uwa suka fita gagarumar Muzahara a Kaduna, wadda ’yan sanda suka bude wuta, har suka raunata mutane uku. Haka ma washegari Alhamis, 21/6/18, ’yan’uwa sun sake fitowa Muzaharar, nan ma ’yan sanda suka sake bude wuta har suka shahadantar da mutane uku, kamar yadda muka yi bayani a babin waki’o’i.
A wannan ranar Alhamis din, sai ba a kawo su Shaikh Zakaky kotun ba, aka ce wai me Keke-Napep ya kade Alkalin, don haka yana jinya ba zai samu damar zuwa kotun ranar ba. Nan take ba a saka ranar da za a dawo ba, sai daga baya babban Lauyan Shaikh Zakzaky Femi Falana SAN ya je kotun aka saka sabuwar ranar da za a koma.
Ranar Alhamis, 2/8/2019 ne aka koma kotu don ci gaba da haramtacciyar Shari’ar da ake wa su Shaikh Zakzaky. A wannan ranar Mai Shari’ar Gidiom Kurada ya halarci kotun. Sai dai har a sannan ba a iya zuwa da sauran mutum biyu da ake karar tare da su Shaikh Zakzaky ba, don haka sai ya ba da umurnin a kamo su kafin a ci gaba da zaman, inda ya sake daga zaman zuwa ranar 4/10/2018. Sai dai a wannan ranar ne ya karanto wa Shaikh Zakzaky laifuffukan da ake tuhumarsa da aikatawa, inda Shaikh Zakzaky ya musanta su baki daya, ya kuma bayyana su a matsayin raini da zagi ga ‘shaksiyyarsa’.
Alhamis 4/10/18 aka sake komawa kotun don duba yiwuwar ta ba da belinsu kamar yadda Lauyoyinsa suka nema a zaman farko aka ce sai sun rubuto. Sai dai kuma a wannan ranar ba a kawo Shaikh Zakzaky da maidakinsa kotun ba, bisa hujjar da Lauyan gwamnati ya bayyana a cikin kotu na cewa a wannan ranar Shugaban kasa zai zo Kaduna, kuma babu isassun jami’an tsaron da za su ba shi tsaro a lokaci guda su bai wa Shaikh Zakzaky.
Wannan ta sa ba a yi Shari’ar ba, balle a yi batun ba da beli. Aka kuma dage ci gaba da sauraron karar zuwa 7/11/2018. Sai dai bayan da Lauyan gwamnati ya fito daga kotun, ’yan jarida sun tambaye shi dalilin dagewan, sai ya ce masu mataimakin Shugaban kasa ne zai zo Kaduna a ranar, ba Shugabankasar da kansa ba.
Ranar 7/11/2018 aka koma kotu da su Shaikh Zakzaky don yin batu a kan yiwuwar ba da beli. Sai dai a ranar Alkalin ya hana belin, bisa hujjar cewa bai gamsu da cewa su Shaikh Zakzaky ba su da lafiya ba, saboda ba a kawo gamsasshiyyar takarda daga Asibitin gwamnati ko wacce Hukumar lafiya ta amincewa a kan rashin lafiyar su Shaikh Zakzaky din ba.
Ya kuma amince da abin da Lauyan gwamnati ya gabatar, na cewa in har aka ba da belin Shaikh Zakzaky ba lallai ne in yana waje ya kawo kansa kotun ba. Don haka sai Mai Shari’a Kurada ya kori batun belin. Ko da aka zo batun ranar da za a dawo kotu, sai Shaikh Zakzaky ya ce masu in sun so su kai ta watan Maris, 2019, wato bayan an gama zaben Shugaban kasa da na Gwamnoni.
Sai dai Alkalin ya sanya 22/1/2019 a matsayin ranar da za a dawo kotu. A wannan ranar ne kuma Falana SAN da kansa ya samu halartar kotun, inda ya yi ma kotu cikakken bayani a kan rashin lafiyar da Shaikh Zakzaky ke fama da shi, ya kuma tabbatarwa da kotun cewa gwamnati ba ta da niyyar bai wa Shaikh Zakzaky kulawa, ya kuma nemi kotun ta ba da izini a fitar da Shaikh Zakzaky kasar waje don ya nemi lafiyarsa da kansa.
A nan sai Lauyan gwamnatin Kaduna, Bayero Dari ya musanta ikirarin Falana SAN, inda ya ce tuntuni har kasar waje gwamnati ta fitar da su Shaikh Zakzaky don nema masu lafiya, don haka ya nemi kotu ta yi watsi da maganar Falana.
A nan Shaikh Zakzaky ya lauyan na gwamnati wa’azi da cewa ya ji tsoron Allah ya guji yin karya, musamman ma a gaban kotu. Tabbas ba inda aka fitar da Shaikh Zakzaky tun da aka kama shi.
Sannan sai Alkalin ya bukaci Shaikh Zakzaky ya zo da Likitocinsa don su duba shi, kuma a yayin zuwan su su ma DSS su zo da nasu, kuma su jami’an tsaron DSS su kyale Likitocin na Shaikh Zakzaky wanda za su zo daga kasar waje ko daga nan gida Nijeriya su duba shi. Ya kuma dage ci gaba da Shari’ar zuwa ranar 25/3/2019.
Shekaru 3 Da Kisan-kiyashin Zariya (9)
Daga Saifullahi M. Kabir
KAFIN DAWO DA SHAIKH ZAKZAKY KADUNA
Tun bayan da kotu ta yi umurnin a saki Shaikh Zakzaky a ranar 2 ga Disambar 2016, inda kotun ta ba da umurnin a saki Shaikh din da mai]akinsa, a cikin kasa da kwanaki 45, kuma a biya su diyyar Naira miliyan 50, tare da gina masu gida a duk Jihar da suka zaba a cikin Jihohin Arewacin Nijeriya, mako guda bayan wannan hukuncin na Kotu, a ranar Juma’a 9/12/2016, kwatsam sai DSS suka je gidan da suke tsare da Shaikh Zakzaky a cikin garin Abuja suna kokarin canza masa wajen da za su ci gaba da tsare shi.
A yayin wayarsa da wasu daga iyalansa a lokacin, Shaikh Zakzaky ya ba da labarin yadda wasu jami’an tsaron suka zo suna kokarin sai sun tashe su a gidan, kan cewa za su komar da su wani gida daban. Sai dai a yayin da suka zo, sam ba su nuna cewa za su canza wajen tsarewa ba ne, sun ce ne ana so ai ma wannan gidan kwaskwarima.
Shaikh Zakzaky ya ce masu; “Ku da kotu ta ce ku sake mu, me zai sa ku zo ku ce za ku canza mana wajen tsarewa? Kuma in ma da gaske za a yi gyara ne, ko fenti a nan gidan, ai ana iya yi muna cikin gidan, illa iyaka ai ma wani bangare, in ya bushe sai mu koma can a sake wa wani bangaren.” Amma dai sai suka dage a kan lallai suna so sai an kwashe kayan su Shaikh din, tare da su an mai da su wani waje saboda nan za a yi gyara.
A ranar Juma’a kwashe kaya da dauke Shaikh Zakzaky bai yiwu ba, sai a ranar Asabar suka kuma dawowa da Yamma a kan cewa lallai DSS DG Lawal Daura ne ya ce, a kwashe kayan a komar da su Malam Zakzaky wani wajen daban, don ci gaba da tsarewa.
Bayan Isha, a wannan daren Asabar 10/12/16 din kuwa, sai suka sake dawowa dauke da bindigogi suka kewaye gidan, sun zo da katuwar mota don kwashe kaya, suka rika hauka, har suka kwashi wasu karikitai suka yi gaba da su.
Dama a wannan lokacin akan ba Shaikh Zakzaky waya duk ranar Asabar da Talata da daddare don su yi waya da danginsu. Amma a wannan ranar, sai suka hana su waya din, sai daga baya aka ba da, inda su Malam suka labarta wa iyalansu, kuma ta sanadin hakan ne ma ’yan’uwa suka san halin da ake ciki, wanda aka rika Muzaharori tun a wannan daren, ba kawai a Nijeriya ba, har a birnin London.
Ranar Lahadi 11/12/16, sai DSS suka aminta Jagora ya tura ’ya’yansa da suke tare da shi su gyara wajen da za a mai da su din. Don haka suka je suka ga wajen suka tsaftace shi, sannan a ranar 12/12/16, shekara daya cif da waki’ar Zariya aka dauke su Shaikh Zakzaky daga inda ake tsare da su a cikin garin Abuja, aka komar da su unguwar jami’an tsaro don ci gaba da tsarewa.
Shaikh Zakzaky da mai]akinsa, Malama Zeenat sun ci gaba da zama a wannan sabon wajen tsarewar har tsawon watanni 17, wato tun daga 12/12/2016 har zuwa ranar 15/5/2018, inda aka dauke su daga Abuja, aka kai su kotu a Kaduna da bakin bindiga.
SHIRYE-SHIRYEN MAIDO DA SHAIKH ZAKZAKY KADUNA
Wani abu tabbatacce shi ne, duk lokacin da ’yan’uwa almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky suka yi wani gagarumin motsi (Muzahara), musamman a birnin Tarayya Abuja na kiran a saki Shaikh din daga haramtacciyar tsarewar da ake masa, jami’an tsaro sun auka musu, ko ba su auka ba, za ka ga wata natija ya biyo bayan hakan.
Wannan a fili yake, mun gani a can baya, yadda suka fito suka nuna Shaikh Zakzaky a TV, yana magana da ’yan jarida, bayan da ’yan’uwa suka kwashe mako guda suna Muzaharori, ana bu]e masu wuta, amma ba su takaita ba a farkon shekarar 2018.
Wasu muhimman abubuwa sun auku a watan Afrilun 2018, wanda ya fara da gagarumar Muzahara da ta gudana a ranar Laraba 11/4/16, inda aka yini a gaban kofar Majalisar Tarayyar Nijeriya, washegari Alhamis kuma aka gudanar da taron tunawa da Shahidan Gwagwarmayar Musulunci, wanda shi ne mafi girman taro da ya gudana a Abuja a lokacin, bayan kammala shi aka yi Muzahara wacce aka rufe ta a gaban ofishin Shari’a na Nijeriya.
Tun daga wannan ranar ne jami’an tsaro, da suka ha]a da ’yan sanda da kuma sojojin da ke tsaron fadar Shugaban kasa (Guards Brigade), suka mamaye filin ‘Unity Fountain’ dauke da muggan makamai, suka dakatar da zaman dirshan din da aka faro tsawon kusan watanni uku, tare da hana duk wani taro a wannan muhallin.
Makon da ya biyo baya, ranar Litinin 16/4/2018, ’yan’uwa suka sake cincirindo suka gudanar da Muzaharar kira a saki Shaikh Zakzaky, inda suka je ofishin Hukumar kare hakkin dan’adam da ke Abuja, sai dai a gaban Hukumar ’yan sanda suka bude wa ’yan’uwa wuta, suka raunata da dama, suka kama fiye da mutum 100, har aka samu Shahidi guda daya; Ahmad Rufa’i Bauchi.
Mutane da kungiyoyi sun ta Allah-wadai da wannan abin, don haka ga alama ita gwamnatin ba ta ji dadin hujumin da duniya ta yi mata na tofin-Allah-tsinen ba, sai kawai kwana biyu bayan nan, a ranar Laraba 18/4/18 gwamnatin Kaduna ta gaggauta shigar da kara a wata babbar kotu a Kaduna, inda take zargin Shaikh Zakzaky, Malama Zeenah da wasu mutum biyu; Malam Yakubu Yahya da Malam Sunusi Abdulkadir da laifuka guda takwas.
Sai dai kuma gwamnatin ba ta bayyana shigar da karar ba a wannan lokacin sai daga baya. A ranar 27/4/2018, Shaikh Zakzaky ya yi waya da babban dansa; Sayyid Muhammad, inda ya ba da labarin yadda Shugaban DSS na lokacin, Lawal Daura ya gana da shi, da kuma abubuwan da suka tattauna.
TATTAUNAWAR SHAIKH ZAKZAKY DA LAWAL DAURA
Shaikh Zakzaky ya labarta cewa a ranar Laraba 25/4/2018 an sanar da shi cewa washegari za su gana da Lawal Daura, don haka ranar Alhamis 26/4/18 tun da sassafe aka dauke su aka kai su muhallin da za su yi ganawar, amma shiru, har zuwa Magriban wannan yinin Lawal Daura bai zo ba. Sai bayan hakan ya zo, ya rika nuna masu isa. Daga karshe ya ce ba zai yiwu a yi ganin a wannan ranar ba, sai dai gobe a komo. Aka mai da su Shaikh inda suke tsare.
Washegari Juma’a aka dawo da su Malam, nan ma Lawal Daura ya kara bata lokaci, sai can da yamma ya zo. A nan ma ya so ya kara dage zaman, amma sai su Malam (H) suka ce ba za su sake zuwa wajen ba in har bai yi maganar da zai yi a lokacin ba. Don haka sai ya yi maganganunsa masu cike da izgili, nuna isa da rainin wayo.
Idan mai karatu ya nemi ‘audio’ din wayar da Shaikh Zakzaky ya yi da Sayyid Muhammad a lokacin, ko kuma ya nemi littafin da Cibiyar wallafa da yada ayyukan Shaikh Zakzaky ta wallafa mai suna ‘Yunkurin kashe Shaikh Zakzaky a tsawon shekaru 10’, zai ga cikakken labarin abin da ya gudana tsakanin Lawal Daura da Shaikh Zakzaky.
Dama kwana biyu kafin zuwan Lawal Daura, Yariman Saudiyya, MBS, ya yi magana, inda ya yi ikirarin da hannunsu a yi wa Shaikh Zakzaky abin da aka masa na yunkurin kawo karshensa da da’awarsa. Don haka a lokacin Shaikh Zakzaky ya fada wa Lawal Daura cewa: “Ka je ka gaya wa wanda ya ba ka ajiyarmu, ya kammala ladansa, in ya dauka kashe mu lada ne, tunda ya kashe mutum sama da dubu, to ya ha]a da mu. Ka ce masa ni da matata a shirye muke, mun shirya mutuwa, saboda haka Bismillah!”
Lawal Daura ya tambayi Shaikh Zakzaky, yanzu idan aka sake shi me zai yi? Ya ce wa Shaikh din. “Saboda akwai wasu masu wani ‘interest’ daban, in ya so sai a fasa wannan.” Sai dai bai fa]i mene ne wannan din da za a fasa din ba, kuma Shaikh Zakzaky bai tambaye shi ko mene ne ba.
Shaikh Zakzaky ya ce masa, zai ci gaba da abin da yake yi ne. “Da can me nake yi? Makamaina tun a da sune ilimi, da hankali da hikima. Kuna so na fita na sa jahilci ne da wauta da hauka? Me kake so na yi? Da can me nake yi wanda yanzu in na fita zan canza? Sai dai in kuna so in na fita zan yi hauka ke nan. Ko kuma ya zama ba ilimi zan sa ba, ko zan dauki makami. Na ce makami na shi ne ilimi da hankali. To sai dai in zan dauki kuma wani makamin ne daban,” in ji Malam Zakzaky.
A nan ne Lawal Daura ya ce wa Shaikh Zakzaky; “Malam na fa san ka tun kana yaro!” Malam ya ce masa; “Tun ina yaro? Ko tun muna yara? Ina ce a 1953 aka haife ka?” Lawal Daura ya ce; “Eh, a watan Agustan 1953.” Sai Malam Zakzaky ya ce masa; “Ni kuma an haife ni a watan Mayun 1953.” Nan Lawal Daura ya ce wa Shaikh Zakzaky; “Eh ka girme ni da watanni uku. To, shi ke nan tun muna yara.”
Nan Shaikh Zakzaky ya ce masa; “To, abin da ka san ni tuntuni dai ina yi, shi nake kai har yanzu. Shekarana 40 ina yi, shi ne kuma nake yi, a kansa kuma nake. Don haka in na fita abin da nake yi tun shekaru 40, shi zan ci gaba da yi.”
A nan Lawal Daura ya samu amsar daga alama ba ita ya so samu daga Shaikh Zakzaky ba. Ya ga cewa tunda Shaikh Zakzaky ya tabbatar masa da cewa zai ci gaba da abin da ya saba ne, bai da alamar fasawa, don haka yanzu ba za a fasa wannan din da yace in ya so sai a fasa shi ba. Wannan din kuwa shi ne kai Shaikh Zakzaky kotu, wanda suka riga suka shigar da kara tun kafin zuwan nasu.
Za mu cigaba.
February 26, 2019
Shekaru 3 Da Kisan-kiyashin Zariya (8)
Daga Saifullahi M. Kabir
RAHOTON AL’ARABIYYA TV A YAYIN ZUWAN BUHARI QATAR
Kwatsam sai ga tashar talabijin ta AL-ARABIYYA ta yi wani rahoto a kan ziyarar da Shugaban kasar Nijeriya Muhammadu Buhari ya kai Qatar, wanda suka dora ‘video’ din rahoton a shafin gidan talabijin din a ranar Talata 1/03/16. Suka yi masa take da “Sabon gargadi daga Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, game da masu yada busharar Shi’anci a Afrika.”
Suka ce: “Buhari ya hangi wani hatsari da ke tunkarowa na yaduwar wata akida mai hatsari, wacce manufarta ita ce, tayar da fitina, raba kan al’umma da kawo hatsaniya.”
Rahoton ya ci gaba da cewa: “Nijeriya wacce take Cibiyar Afrika; ta fi kowace kasa a Nahiyar ta Afirka yawan mutane, wacce ake kiyasta Musulmin cikin ta sun kai miliyan 85. Daga cikin su akwai kasa da miliyan 10 ’yan Shi'a, sauran kuma Musulmi ne mabiya Sunnah.”
Su ci gaba da cewa: “Shi’a ta yadu daga baya (a Nijeriya) ta hannun Ibraheem El-Zakzaky, wanda Iran ta nasabta shi a matsayin Wakilin Hizbullah a Nijeriya. Jami’an tsaro sun kama shi ne a watan Disambar shekarar da ta gabata; bayan sun tuhume shi da yunkurin kashe Shugaban Hafsan Sojojin Nigeria, a lokacin da yake kan hanyarsa ta wucewa Zariya; wacce ake ganin ta a matsayin wuri mafi muhimmanci ga mabiya Shi'a da suke zaune a Arewacin Nijeriya, kuma nan ne mazaunin Shugabanta da ke samun goyon bayan Iran.”
A nan sai suka sanya bidiyon Buhari yana cewa: “Arangamar (ta Zariya) faru ne a lokacin da ya yi kokarin dakatar da tawagar Hafsan-Hafsoshin sojojin Nijeriya. Daga baya Shi’a ta yi karfi. Kuma muna da masaniyar cewa tana samun karfafa da abin da ya yi kama da haka daga Iran”.
Sannan suka ci gaba da sharhi da cewa: “Shugabannin siyasa da sojojin Nijeriya ra’ayinsu ya zo daya a kan cewa Shi’a a Nijeriya - wacce take da goyon bayan Iran – ra’ayinsu daya da kungiyar Boko Haram, wacce ta yi wa Da’esh bai’a.”
Suka ce: “Dalilai da dama ne suka sabbaba yaduwar Shi’a a Nijeriya. Daga cikin su akwai talauci, jahilci, ba da tallafin karatu, (da Shi'a suke badawa) da kuma yaudarar mutane ta hanyar taken ’yanto Masallacin Al-Aqsa. Wadannan dalilan ne ke sa mutane tudadar shiga wannan Mazhabar da Iran ke karfafawa.”
Mai karatu, ka lura da yadda bayanan mutanen nan ke zuwa a tare; yaduwar Shi’anci, tasirin Iran, goyon bayan Iran, da batun TAQIYYA, ko taimakon raunana. Wadannan sune duk abin da suke kokarin su nuna cewa Harkar Musulunci na samu don habakar ta. Kuma shi ne abin da suke kokarin a dakile.
Kuma har ila yau, kalaman Buhari ya nuna maka kai tsaye mai suka yi a Zariya, sun auka wa Shaikh Zakzaky ne da almajiransa, don su dakile yaduwar tasirin Iran a Afirka, musamman a Nijeriya. Amma ba wani abu wai tare hanya ne ya sabbaba kashe mutum 1,000, da kama Shaikh Zakzaky a daure tsawon shekaru da rauni a jikinsa ba, kamar yadda za mu ji daga bakin Yariman Saudiyya a gaba.
Muhammadu Buhari da Malaman Wahabiyawa na Saudiyya da na Nijeriya
RAHOTON DW NA BAYANIN BIN SALMAN KAN DAKILE TASIRIN IRAN A AFIRKA
Sai aka zo, a ranar 24 ga watan Afrilun 2018, sashen Hausa na gidan rediyon DW da ke Jamus ya fitar da rahoton murya, inda Yariman Saudiyya, Muhammad Bin Salman ya furta a sarari cewa su ke da alhakin harin da aka kai wa Shaikh Zakzaky a kokarinsu na dakile karfi da tasirin Iran a Afirka!
Rahoton na DW, ya bayyana cewa: “A wata hira da jaridar TIMES ta Amurka ta yi da Yarima mai jiran gado na Saudiyya, Muhammad Bin Salman ya ce kasarsa ta kai gouro-ta-kai-mari a Afirka don ganin ta rage tasirin Iran a nahiyar, yadda ya zuwa yanzu ta yi nasarar karya karfin kasar ta Iran a Afirka da kimanin kaso 95 cikin 100.”
A shafinsu na sakar sama, DW, sun rubuta a karkashin wani hoto da suka saka, cewa: “Muhammad Bin Salman ya ce kasarsa (Saudi-Arebiya) ce ta dakushe karfin Ibraheem al-Zakzaky a Nijeriya”
Sannan rahoton nasu ya ci gaba da cewa: “Dakta Zayeed Al-Amri, mamba a Cibiyar tsara dabarun mulki da tunkarar matsaloli na kasar ta Saudiyya, ya yi karin bayani kan manufar Yariman, inda yake cewa ‘abin da Yarima ke nufi a nan shi ne tun bayan da ya ayyana shirinsa na tunkarar makiya, Saudiya ta yi nasarar karya tanadin Iran a Yemen da Somaliya da Djibouti da Sudan, kamar yadda ta lalata yunkurinta na kafa makamanciyar kungiyar Hizbollah a Nijeriya da hana Ibraheem Zakzaky yin juyin mulki a kasar.”
Kafar ta DW, ta kuma ruwaito Dakta Amani al-Taweel ta Cibiyar bincike na Al-Ahram a Masar, inda take cewa: “A gaskiya Saudiyya ba abin da ya fi damunta tamkar yada akidar Wahabiyyanci a Afirka fiye da kulla huldar kasuwanci da alakar diflomasiyya ta ban gishiri, in ba ka manda.”
A wannan rahoton, Muhammad Bin Salman da sauran masu sharhi sun bayyana karara dalilin kisan kiyashin Zariya, cewa kwangila ce ta gidan Sarautar Saudiyya zuwa ga Shugaban Nijeriya da jami’an tsaronta a kan su dakile mata Shaikh Zakzaky da abin da suke kira Shi’anci, a kokarinsu na dakile tasirin Iran a Afirka da kuma karfafar yaduwar akidarsu ta Wahabiyyanci.
GUDUMMAWAR MALAMAN WAHABIYAWA A KAN WAKI’AR
Ya gabata tun a kashi na biyu na wannan jerin rubutun, na kawo yadda Malaman Wahabiyyawa suka rika zame-zame da gwamnati da kuma yin wasu kalamai na nuna farin cikinsu kafin da kuma musamman ma bayan abin da ya faru na kashe wadanda suke kira ’yan Shi’a fiye da 1,000 a Zariya.
Mun kawo yadda a ranar Asabar, 19/12/2015 wasu daga cikin Gwamnonin Arewa, karkashin Kashim Shettima, suka gabatar da zama a Kaduna, inda suka tattauna yadda za su bullowa taka wa Harkar Musulunci burki a Jihohinsu.
Da kuma zaman kungiyar Limamai da Malamai na Jihar Kaduna a ranar 28/12/2015 da suka gana da Nasiru El-Rufa’i, inda suka bayyana goyon bayansu a kan fadan da yake da ’yan Shi’a a Jihar tasa. Suka kuma bayyana masa cewa hakan da yake yi wani aiki ne da addinin Musulunci ke maraba da shi.
Mun kuwa kawo yadda a 14 ga Junairun 2016, shi ma GOC I Division, Manjo-Janar Adeniyi Oyebade, ya gana da wasu Malaman Wahabiyawa da Limamansu, ya yi masu bayani a kan shirin jami’an tsaro a kan Shi’a da kuma gudummawar da ake bu}ata daga Malaman, har ya ba su kyautar Naira dubu 500 su raba.
Mun kawo kuma inda a ranar 21/12/2015, Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi; daya daga cikin masu ra’ayin Wahabiyanci ya yi jawabi, inda yake yaba wa sojoji a kan abin da suka yi, da sunan hakan taimakon Sunnah ne da magance masu zagin Sahabbai.
Kungiyar Izala, musamman ta bakin shugabanninta, Shaikh Sani Yahaya Jingre, Shaikh Abdullahi Bala Lau da Shaikh Kabiru Gombe sun yi ta wa’azozi suna masu murna da abin da aka yi a Zariya.
Wani abu da ban kawo ba a baya shi ne bayanin daya daga cikin Malaman Izala, Shaikh Gero Argungun ya yi a fadar Sarkin Yawuri, Dakta Muhammad Zayyanu Abdullahi, kwanaki kadan bayan kisan kiyashin na Zariya, inda bayan ya gama yin karairayi ga Shi’a da Shi’anci a karshe ya shiga bayyana alakar su da Shugaban kasa, Muhammadu Buhari wajen kokarin magance Shi’anci a Nijeriya.
A cikin ‘audio’ din jawabin nasa, Shaikh Gero ya bayyana cewa: “Iran komai suna iya yi, shi ya sa da suka gayyaci Shugaban kasar Nijeriya, Muhammadu Buhari, muka yi ‘meeting’ tare da shi, muka fada masa ya yi hattara da wadannan mutane. Muka fada masa ka ji, ka ji ka ji (dangane da Shi’a). Ya ce to zai lura. Muka ce to in kuma ka je Iran kar ka sa bakaken kaya, don yana cikin hanyar yaudararsu, za su yi maka hoto su yada wa duniya cewa ai kai mamba ne daga cikin su.”
Gero ya ce: “Duk alkawuran da ya yi mana, da ya je Iran ya cika su, kun gan shi a ‘setilayit’ cikin fararen kaya.” Ya ci gaba da cewa: “Da (Buhari) ya dawo ya kira wasu daga cikin mu da muka yi ‘meeting’ da shi (kan ya tafi), ni ban samu zuwa ba. Ya ce duk abin da kuka fada mana kun rage, ni na je Iran na gani da idona, Wallahi babu Musulunci.”
Mai karatu, ba za mu tambayi kanmu cewa mene ne damuwar Shugaban kasar Nijeriya, kasar da ba ruwanta da Allah da addini, ba ruwanta da me kake bautawa a ka’idarta, da akidar Shi’anci ko Mazhabar Ahlul Baiti (AS)?
Kuma hatta taron da Buhari ya je Iran taro ne na wasu kasashe guda 8 masu arzikin man fetur a duniya ne. Ko da yake ya gana da Shugaban addini na kasar Iran, Sayyid Khamene’i, amma sam ganawarsu ba ta da alaka da Musulunci ko Shi’anci, face ya ba shi shawarwari ne a kan muhimmancin dogaro-da-kai da nisantar kasashe masu yin mulkin-mallaka.
KARKAREWA
Daga abin da ya bayyana ga mai karatu, zai fahimci cewa tabbas waki’ar Zariya da aka dira a kan Shaikh Zakzaky da almajiransa, wani yunkuri ne na kokarin kawar da Harkar Musulunci da abin da suka kira Shi’anci, ko tasirin Iran a Afirka. Ya fi karfin wani wasan kwaikwayo na cewa, wai an tare hanya ne kawai sai hakan ya auku, kuma har yau bai kawo karshe ba!
Don haka ne ma duk abin da suka yi na kokarin ganin bayan Harkar ta Musulunci abu ya ci tura, har yanzu ba su hakura ba. Suna ci gaba da tsare daruruwan almajiran Shaikh Zakzaky, da shi kansa Shaikh din da maidakinsa, duk da cewa babbar Kotun Tarayya a Abuja ta ba da umurnin a sake shi.
Amma sun take dokar, yanzu ma sun komar da shi Kaduna ne sun gurfanar da shi a gaban wata kotu suna masa haramtacciyar shari’a, wacce insha Allah a rubutu na gaba za mu tashi da bayanin yadda aka dawo da Shaikh Zakzaky Kaduna daga Abuja, zuwa yadda ake gudanar da haramtacciyar shari’arsa a wata babbar kotu da ke garin Kaduna din.
February 25, 2019
Shekaru 3 Da Kisan-kiyashin Zariya (7)
Daga Saifullahi M. Kabir
HANNUN WAHABIYAWA A KISAN-KIYASHIN ZARIYA
Waki’ar Zariya ta auku ne da nufin kawar da Shaikh Ibraheem Zakzaky da Da’awarsa baki-daya. Don haka ma tun kafin aukuwarta da kuma abubuwan da suka biyo baya, sun nuna balo-balo cewa akwai cikakkiyar gudummawar wadanda ake kira Wahabiyawa, wato akwai hannun tushen Wahabiyanci, gidan Sarautar Saudi-Arebiya a cikin duk abin da ya faru.
A nan, zan so mu dogara ga wasu abubuwa guda biyar da suka auku kafin, da kuma bayan kisan-kiyashin na Zariya, kamar haka:
1- Rahoton WISAL TV a kan yaduwar Shi’a a Nijeriya.
2- Kashedin Shekau ga Shaikh Zakzaky, da kuma kai mana hari da sunan Boko Haram.
3- Waki’ar Zariya da yabawar Sarkin Saudiyyah.
4- Rahoton AL’ARABIYYA a yayin zuwan Buhari Katar.
5- Rahoton DW na bayanin MBS a kan dakile tasirin Iran a Afirka.
6- Gudummawar Malaman Wahabiyawa/Izala a kan waki’ar.
RAHOTON TASHAR WISAL TV
Watanni kamar uku kafin aukuwar waki’ar Zariya, a cikin watan Satumbar 2015, wani gidan TV mai suna Wisal, mallakin kasar Saudi-Arebiya, sun yi wani ‘documentary’ inda a cikin sa suka nuna hadarin da ke fuskantar Nijeriya na yaduwar Shi’anci da tasirin Iran a tsakanin matasa, ta hannun Shaikh Ibraheem Zakzaky. Inda a marshe suka nuna takaici ga yadda aka kyale hakan na faruwa a masar da tafi ko’ina girma da tattalin arziki a nahiyar Afirka.
Rahoton ya bayyana cewa: “A duk duniya, a yanzu babu wata masa mafi ha]ari kamar Nijeriya, saboda yadda wata sabuwar fahimta ke ya]uwa har ta mamaye Jihohi hudu, wadda a cikin su akwai masu wannan a}idar kimanin mutane miliyan 25.”
Suka ce: “Wannan cutar da ta bulla a Nijeriya ita ce Shi’a, wacce take yaduwa a tsakanin matasa, wadanda suke makarantun boko suna karantar ilimin likitanci, Kanikanci da wasu fannonin na ilimin boko, wanda kuma ana daukar nauyinsu su je su kware a fannoni daban-daban. Wannan ya sa da yawan matasan ba su san ilimin addini ba. Don haka cutar Shi’anci ke yaduwa da gaggawa a tsakanin matasan Nijeriya.”
Suka ci gaba da cewa: “Wani matashi mai suna Ibraheem Yaqoub Zakzaky ne ya buya a bayan wasu abubuwa, kamar kokarin ’yanto Masallacin Qudus daga hannun Yahudawa da goyon bayan raunanan al’ummar da ake zalunta, yana yaudarar mutanen Nijeriya zuwa ga shiga wannan akidar ta Shi’anci.”
Suka ce: “Malamin, wanda aka san shi a matsayin dan tawaye, ana gayyatar sa ya je Iran don a kara masa ilimi a kan akidar Shi’a. Tsayuwarsa wajen yi wa Shi’anci aiki ya sa shi da mabiyansa sun kai ga suna shirya wasu Muzaharori kamar na Qudus da Ashura. Ya samu nasarar yada wannan cutar ne ta hanyar yin abin da ake kira TAQIYYA, wanda hakan ne ya sa jahilai suke bin sa. Da’awarsa ta fara shahara ne a shekarun tamaninoni (1980s), ta kuma ci gaba da yaduwa a 1990s. Abin da ya fi bata rai shi ne yadda Malamai suka kyale, suka yi shiru a yayin da wannan akidar mai hadari take ci gaba da yaduwa.”
Rahoton na Wisal ya ce: “Zakzaky din, ya yi fice a harkokin diflomasiyya, ta kai ga yana tura dalibai zuwa Jami’ar Tehran a Iran su yi karatu su mware a fannoni, har ma sun fara dawowa Nijeriya suna yada Shi’anci a tsakanin mutane.”
Suka ce: “Suna da wata Jarida da ake kira ALMIZAN, wacce ake buga ta da Hausa, wacce take yaduwa a cikin mutane sosai. Tana taimakawa wajen kara yaduwar Shi’anci. Kuma suna da Website na Hausa da Turanci, wanda suke yada manufofinsu. Kuma suna sayen lokaci a gidajen rediyo da talabijin da jaridu, don su yada manufofinsu ga al’umma. Wannan ne ya ba su damar samun alaka da kyakkyawar fahimta da masu bin Darikun Sufaye, suke haduwa don su fuskanci Ahlus Sunnah.”
Bayan kare rahoton, sai suka saka hira da wani mutum mai suna Dakta Muhammad al-Mubarak, inda yake sharhi a kan abin da aka fa]a. A ciki yake cewa: “A shekarar 1979, shekarar da Khumaini ya yi juyin-juya-hali, babu Shi’a ko daya a Afrika. Sam ba su san Shi’a ba kwata-kwata. Afirka nahiyar Musulmi ne. Eh, akwai wasu kasashe da mafiya yawan mutanen cikin su Musulmi ne, akwai kuma wasu da ka]an ne Musulmi din, amma Shi’a, sam ba a san Shi’a ba a nahiyar baki daya. Haka nan abin yake a da yawa daga kasashen Musulmi, kamar Indinosia.”
Al-Mubarak ya ce: “Amma bayan juyin Khumaini a 1979, sai aka fara aikin yada akidar Shi’anci zuwa kasashe daban-daban. Za mu iya gani yanzu, abin mamaki, Shi’a ta mamaye mafi girman kasashen Afirka a yawan mutane da tattalin arziki. Yanzu muna jin hauhawar farashin mabiya Shi’a a Nijeriya.”
Wannan rahoton, wanda muke da ‘video clip’ dinsa, in mutum ya nazarce shi, zai ga cewa Saudiyya tana jin takaicin yaduwar da’awar Shaikh Ibraheem Zakzaky na Harkar Musulunci da yake yi a tsakanin matasan Nijeriya, wanda kuma suna wa Da’awar kallon Shi’anci ne, saboda ganin cewa Jagoran Harkar da mafiya yawan mabiyansa suna bin tafarkin Ahlul Baiti (AS) ne.
Don haka sun nuna a cikin rahoton cewa, akwai bukatar taka wa yaduwar Shi’ancin birki ta kowane hali, a yayin da suke kokarin nuna cewa Harkar Musulunci din, ko abin da suke kira Shi’anci, na daga cikin tasirin juyin-juya-halin Musulunci ta Iran, wacce Amurka, Isra’ila da ita Saudi-Arebiya din suke tsananin gaba da shi.
KASHEDIN SHEKAU DA KAWO HARIN BOM A KAN ’YAN’UWA
Ba a jima da yin wannan rahoton na Saudiyya a kan takaicinsu na ya]uwar Shi’anci a Nijeriya ba, kamar wata guda bayan hakan, a karshen watan Oktoban 2015, sai ga Shugaban wata kungiyar Wahabiyawa da suke kai hare-haren ta’addanci a Arewacin Nijeriya da aka saka wa suna Boko Haram, mai suna Abubakar Shekau yana kashedi ga Shaikh Zakzaky da almajiransa a kan su gaggauta tuba daga Shi’anci.
A cikin garejeren bidiyon na Shekau, ya furta cewa: “’Yan Kaduna! Kai Zakzaky! ’Yan Shi’a, masu TAQIYYA! Ku tuba!”
Ku lura da wasu abubuwa a cikin wannan garejeriyar maganar ta Shekau, ta yadda yake kiran sunan Shaikh Zakzaky gatsai yana cewa ya tuba, alhali a baya Shekau bai taba kama sunan wani Malamin addini a kasar nan ya yi masa kashedi ba.
Kuma ku lura da yadda ya ambaci kalmar TAQIYYA, wannan kalmar da rahoton Wisal TV ya jaddada, cewa wai Shaikh Zakzaky yana yaudarar matasa ne ta hanyar yin TAQIYYA. Bai zama abin la’akari ba, a yayin da kalmomin Shekau suka dace da na Saudiyya?
To, bayan wannan kashedin kuma da wata guda, har ila yau, a karshen watan Nuwambar 2015, sai aka kawo wa ’yan’uwa Musulmi almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky harin bom a yayin da suke kan hanyarsu na Tattakin juyayin Arba’in din Imam Husaini (AS), daga Kano sun nufo Zariya.
Harin bom ]in da ya ci rayukan almajiran Shaikh Zakzaky kusan mutum 25, an yi nasarar dakile tashin na mutum daya, a yayin da na guda daya ne ya tashi ya kashe wannan adadin. Kwatam sai aka ji a kafafen yada labarai, wai kungiyar Boko Haram ta dauki alhakin kawo wannan harin.
Sai ya zama kamar wannan ne ma’anar kashedin Shekau ga Shaikh Zakzaky da ’yan Shi’a, a yayin da yake cewa su tuba. Da ba su tuba ba, suka ci gaba da Shi’anci, ga shi ya kawo masu harin kunar bakin wake ma.
Sai dai Jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya, Shaikh Ibraheem Zakzaky, a yayin da yake jawabi a wajen rufe taron Arba’in, kwana uku bayan aukuwar harin, ya bayyana cewa ba kowa ke da alhakin kawo harin ba face jami’an tsaron Nijeriya, wa]anda dama suke da alhakin duk abubuwan da ke faruwa a kasar nan da sunan rashin tsaro.
Bayan Shaikh Zakzaky ya dora alhakin harin a kan jami’an tsaron, bisa dalilan da ya bayyana a cikin jawabinsa na ranar Arba’in din, wanda aka gudanar a ranar Alhamis, 3 ga watan Disambar 2015, ba a samu wata murya daga bangaren gwamnati ko jami’an tsaro da ta musanta zargin da Shaikh Zakzaky ya yi a wannan lokacin ba. Sai kawai martanin da sojoji suka bayar kwanaki tara bayan wannan jawabin, wanda shi ne ‘Kisan-Kiyashin Zariya’.
WAKI’AR ZARIYA DA YABAWAR SARKIN SAUDIYYA
Mun riga mun yi bayani a kan waki’ar Zariya tun a babin farko na wannan rubutun, kuma mun kawo yadda wata kafar ya]a labarai ta ‘Pars News Agency’ ta ruwaito a ranar 16/12/2015, kwanaki biyu bayan gama waki’ar ta Zariya, cewa Sarkin Saudiyya, Salman Bin Abdul’azeez ya kira Shugaban kasar Nijeriya, Buhari ya taya shi murna a kan aikin da ya yi na murkushe Harkar Musulunci da sunan wai fada da ta’addanci.
Sarki Salman, ya bayyana kisan-kiyashin Zariya a matsayin yaki da ta’addanci da murkushe ’yan ta’adda. Wanda a rahoton Wisal TV da ya gabata za mu iya gane suna nufin tasirin Iran a Afirka da yaduwar Shi’anci ne suke nufi da Ta’addancin, kamar yadda kuma za mu gani a gaba.
Za mu cigaba insha Allah.
February 19, 2019
An Yi Walimar Cika Shekaru 40 Da Shelanta Harkar Musulunci
Daga Wakilinmu
A wani sabon salon amfani da kafafen sadarwa ta hanyar gudanar da ayyukan alkairi, ’yan’uwa Musulmi almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky, sun gudanar da walimar cika shekaru 40 da shelanta Harkar Musulunci a zauren Khairul Amal da ke shafin WhatsApps.
Walimar, wacce ta gudana a tsawon kwanaki uku a jere, an fara ta ne daga ranar Juma’a, 19 zuwa Lahadi 21 ga Jimadal Ulan a shekarar 1440BH, inda aka gudanar da abubuwa kala-kala da suka hada da kacici-kacici a kan Tarihin Harkar Musulunci, wanda ya gudana a ranar farko.
A rana ta biyu aka gabatar da jawabi a kan tarihin Harkar Musulunci a tsawon shekaru 40 a takaice. Sannan a ranar karshe aka saurari labarurruka daga dukkanin ’yan uwan da ke zauren a kan yadda suka fahimci Harka har suka tsinci kansu ana tafiyar tare da su.
Yayin jawabinsa dangane da maudu’in ‘Harkar Musulunci A Shekaru 40’, wanda ya gudanar a salon rubutu, Jagoran zauren na Khairul Amal, Saifullahi M. Kabir, ya bayyana tarihin Harkar Musulunci tun daga tushenta, inda ya faro da bayani a kan tarihin Jagoran Harkar, wato Shaikh Ibraheem Zakzaky.
Malam Saifullahi M. Kabir, ya yi bayani a kan tarihin haihuwar Shaikh Zakzaky, wanda ya faru a garin Zariya a shekarar 1953, wanda ya yi daidai da shekarar 1372 Hijiriyya. Da kuma yadda Shaikh din ya taso a gidan Malaman Alkur’ani, don haka ya zama tun yana karami ya shagaltu da karatun Alkur’ani ne da zuwa gona don taya Mahaifinsa aiki, har zuwa lokacin da ya sauke Alkur’ani yana da shekaru 14 da haihuwa. Inda daga nan ya fara karatun littattafai a gaban Malamai har ya karanta duk littattafan da ake karantawa a zaurukan ilimi a wancan lokacin.
Ya ci gaba da cewa, bayan da Shaikh Zakzaky ya karanta fannoni daban-daban na ilimin addini da Luggar Larabci, a shekarar 1969 (lokacin yana da shekaru 16) ne aka saka shi a makaranta Nizamiyya, inda ya fara da wata makaranta ta koyon Larabci a Zariya, wacce ake kira Zaria Provincial School. Bayan shekaru biyu, wato 1969 zuwa 1971, ya kammala ta.
Ya bayyana yadda Shaikh Zakzaky ya ci gaba da yin wata makaranta da ake kira Madarasatul Ulumul Arabiyya (School for Arabic Studies) a Kano, inda ya fara ta daga shekarar 1971 zuwa 1975. Ya ce, a wannan makarantar ne Shaikh din ya rika ware lokaci yana zuwa wasu azuzuwa na daban (Advance Level) yana karantar wasu fannoni na Boko da suka ha]a da English, Literature, Economics, Government, Hausa, Arabiyya da kuma Islamic Studies.
Ya ce, wannan ne ya sa Shaikh Zakzaky a yayin gama makarantar ya rubuta jarabawa kashi biyu; ta Grade II din da yake karatu a kansa da kuma na Advance Level ]in da ya karawa kansa. Kuma duk ya ci su. Don haka fitowar sakamakon a shekarar 1976 ya ba shi damar fara karatun Jami’a kai tsaye ba tare da share fage ba. Ya fara karanta Economic, Government da Sociology. Daga baya sai ya fi kwarewa a Economics, don haka sai ya dauke shi a matsayin ‘course’ dinsa. Ya yi Digiri a bangarensa, inda ya kammala a shekarar 1979.
Da ya shiga bayani a kan farkon Da’awar Harkar Musulunci kuwa, Malam Saifullahi M. Kabir, ya bayyana yadda Shaikh Zakzaky ya samu Jami’a a lokacinsa, akwai mutane wasu masu tunani dangane da makomar kasa kashi biyu; kashin farko sune kungiyar dalibai Kiristoci (FCS), wadanda suke da tunanin cewa tsarin da ke iko da kasar ya yi, don haka da bukatar a inganta shi ne kawai ba tare da sauyi ba.
Kashi na biyu kuma sune masu ra’ayin Kwaminisanci, wadanda suke sukar addini gaba daya, suke kuma sukar addinin Musulunci, musamman kan cewa addini kawai an samar da shi ne ma don a samu damar mulkar mutane.
Ya ce; “Kwaminisawa sun rika sukar addinin Musulunci ta hanyar ba da misali da mulkin wasu Sarakuna da Daulolin Gargajiya ko na Musulunci, irin su Mulkin Banu Umayya da Banul Abbas da irin ta’addancin da Sarakunansu suka yi. Haka ma irin mulkin Sarakunan Gargajiya a nan kasar. Sai suke nuna cewa wannan zaluncin da Sarakuna suka ri}a yi shi ne ma koyarwar addinin Musulunci. Don haka suna ganin ba zai taba yiwuwa addini ya zama tsarin adalci ga rayuwar mutane ba. Har ma suna cewa addinin Musulunci ya kafu, ya yi iko ne a duniya saboda lokacin duniya ba ta waye ba.”
Ya ce, da Shaikh Zakzaky ya riski wa]annan ra’ayoyin, sai ya samar da murya ta uku a karkashin inuwar Kungiyar Dalibai Musulmi (MSS), wanda yake a lokacin shi ne Sakataren kungiyar a Jami’ar Ahmadu Bello, kuma mataimakin Shugabanta na kasa kan harkokin kasashen waje. “Don haka sai ya fara kokarin mai da martani ga Kwaminisawa, ta hanyar wanke addinin Musulunci kan cewa, a kawo inda aka ga zalunci a gwamnatin da Manzon Allah (S) ya kafa. Ya kuma rika tabbatar wa da mutanen Jami’a cewa, komawa ga addinin Musulunci shi ne kadai mafita wajen samun adalci da wadatuwar arziki da samun aminci.
“Shaikh Zakzaky ya tsaya kyam a Jami’a wajen fa]akar da ]alibai da Malamai cewa, Musulunci kammalallen nizamin rayuwa ne ga mutum, addini ne, hanyar rayuwa ne, kuma ‘ideology’ ne a lokaci guda. Kuma a kan asasin adalci da ilimi da hujja aka kafa Musulunci. A yayin da shi Kirista yake ganin cewa Addini daban, rayuwa daban, Musulunci na ganin duk abu guda ne. Kwaminisanci na ganin ana danniya a kawo adalci. To, Shaikh Zakzaky ya tabbatar masu da cewa, ba inda za a samu adalci in ba a Musulunci ba.”
Malam Saifullah ya ce; “Da irin haka ne Shaikh Zakzaky ya fara kira ga komawa ga addinin Musulunci da yunkurin tabbatar da shi ya yi iko a doron kasa ma.”
Ya ce, tun daga wannan lokacin na Jami’a ne Hukuma ta fara daukar matakai a kan Shaikh Zakzaky da kiran da yake yi, wanda hakan ya yi sanadin kama shi a daure tun yana Jami’a a lokacin mulkin soja na Obasanjo, da hana shi takardar shaidar kammala Digirinsa.
Da yake magana a kan yadda Shaikh Zakzaky ya sha gwagwarmaya tun daga farkon al’amari, Saifullahi ya bayyana cewa tun da Shaikh Zakzaky ya shelanta da’awar kira a komawa Musulunci a ranar Asabar 5/4/1980 daidai da 20 ga Jimadal Ula, 1400H, daga nan Hukuma ta fara daukan matakan kama shi ta daure a kurkuku na tsawon shekaru.
Ya kawo jerin kame-kamen da aka wa Shaikh Zakzaky da adadin lokacin da ya yi, tun daga kamun gwamnatin Shagari, wanda aka kama Malam Zakzaky a garin Sakkwato a watan Mayun 1981 zuwa May 1984, sannan aka sake shi.
Ya ce; “Shaikh Zakzaky na kurkukun Shagari ne Buhari ya yi juyin mulki ya hambare Shagari. Don haka Shaikh ]in ya fito ne a lokacin Buhari na mulkin Soja. Wata shida bayan fitowarsa kuma, sai Buhari a lokacin yana yayin kame-kamen mutane ya daure, ya sake kama Shaikh Zakzaky ya daure shi tun a watan Disambar 1984, a lokacin Shaikh din bai jima da aure ba. Don haka ma har aka haifa wa Shaikh Zakzaky yaronsa na farko da aka saka wa suna Muhammad, Shaikh din na tsare a kurkukun Buhari soja. Sai a watan Agustan 1985, bayan an hambare Buhari daga mulki, Shaikh Zakzaky ya fito, bayan ya shafe watanni tara a tsare a kurkuku.”
Ya ci gaba da cewa; “Babangida kuwa ya kama Shaikh Zakzaky ne ya tsare tun a watan Maris din 1987 bayan shekaru biyu, a shekarar 1989, sannan aka sake shi. Daga nan ne kuma ba a sake kama Malam Zakzaky ba sai a lokacin Mulkin Janaral Sani Abacha, wanda ya kama shi a shekarar 1996. Bayan mutuwar Abacha, a shekarar 1999 Shaikh din ya fito a lokacin rikon kwaryar Abdussalami Abubakar.
Ya ce; “A yanzu haka Shaikh Zakzaky ya kasance a tsare tun kimanin shekaru uku da suka gabata, bayan da sojoji suka yi dirar mikiya a kansa, suka kashe iyalai, dangi da almajiransa fiye da 1,000 a Zariya bisa umurnin Shugaban kasa, Muhammadu Buhari.”
Ya bayyana babban darasin da ke cikin bitar tarihi, inda ya ce shi ne don a koyi abubuwan kirki. Ya ce; “Tabbas daga waiwayen tarihin Harkar Musulunci da Jagoranta ’yan’uwa za su koyi dakewa, kamar yadda Shaikh Zakzaky ya iya fuskantar wannan baranaza da jarabawowin a tsawon wa]annan shekarun, amma har yau bai sauya hadafi, ko manufarsa ba.”
A yayin taron, an raba kyaututtukan katin waya, ga wadanda suka lashe gasar kacici-kacici a kan Tarihin Harkar Musulunci, wanda Malam Adamun Adamawa ya jagoranta.
Daga jaridar ALMIZAN ta 26/5/1440
Shekaru 3 da Kisan-kiyashin Zariya (6)
Daga Saifullahi M. Kabir
WAKI’AR FREE ZAKZAKY A KADUNA DA ABUJA
A ranar 6/1/2018 labari ya iske ’yan’uwa daga dangi da makusantan Shaikh Zakzaky, cewa jikinsa ya tashi sosai har ma yana fuskantar barazanar shanyewar barin jiki! Wannan ya sa hankalin ’yan’uwa ya tashi. A cikin wannan daren na ranar 6/1/2018 aka rika gudanar da Muzaharori a wasu garuruwa, musamman a Bauchi da Kano.
An ci gaba da Muzaharar kira ga gwamnati ta saki Shaikh Zakzaky domin ya je ya nema ma kansa lafiya a safiyar Lahadi, 7/8/2018 a kusan dukkan birane da kauyukan kasar nan.
A wannan ranar ta Lahadi ’yan sanda sun bude wuta a kan masu Muzaharar a Kaduna, inda suka jikkata mutane biyar, har biyu daga cikin su suka samu Shahada; Shahid Muhammad Auwal Kakuri da Shahid Abdulmalik Sani. Shaikh Zango ya jagoranci yi masu janaza washe-gari Litinin a Kaduna.
Litinin 8/1/2018 ne ’yan’uwa suka fara cincirindon shiga Abuja don fara gudanar da Muzaharorin kira a saki Shaikh Zakzaky na sai baba-ta-gani. A wannan ranar ’yan sanda sun bude wa masu muzaharar wuta, inda suka kama wasu, kuma suka jikkata da dama, amma ba a samu Shahidi ba.
Ranar Talata 9/1/2018 ’yan’uwa almajiran Shaikh Zakzaky sun sake fitowa Muzaharar kira a sake shi a tsakiyar garin Abuja. A ran nan ma ’yan sandan sun kuma bude wuta a kan ’yan’uwa, inda suka jikkata da dama, suka kama ’yan’uwa masu yawa. A wannan ranar ne ’yan sanda suka harbi Shaikh Kasim Umar Sakkwato a cinyarsa, wanda bayan jinya da ya sha na tsawon kimanin kusan wata guda, ya yi shahada a ranar 5/2/2017.
Shaikh Saleh Lazare na jagorantar janazar Shaheed Qaseem Umar
Washegari Laraba 10/1/2018 ’yan’uwa suka sake fitowa don Muzaharar Free Zakzaky a Abuja din. Ran nan ma jami’an tsaron sun bude wuta a kan masu Muzaharar, inda suka datse gaba da bayan Muzaharar, suka rika amfani da wasu mashina suna ratsa cikin ’yan’uwa suna watsa musu Tiyagas, bayan sun galabaitar da su, sai suka fara harbi da harsasai masu rai, inda nan take suka kashe mutum biyu; Shahid Aminu Ibrahim Gashua da kuma Shahid Usman Dunari, wanda shi sai bayan kwanaki 9 da shahadarsa sannan ’yan sanda suka ba da gawarsa aka yi mata janaza. Sun kuma jikkata gomomi a yayin da suka kama ’yan’uwa masu yawa.
Alhamis 11/1/2018 aka ci gaba da Muzaharar, sai dai an tashi lafiya a wannan ranar. Amma a ranar Juma’a 12/1/2018 an yi Muzaharar ne daga Babban masallacin Kasa na Abuja, inda ’yan sanda suka harba Tiyagas a kan masu Muzaharar.
A ci gaba da Muzaharar kullum a garin Abuja don fafutukar ganin an saki Jagoran Harkar Musulunci daga haramtaccen tsarewar da gwamnatin Buhari ke masa, yanzu haka Muzaharar ta kullum, wadda ake kira Fafutukar Abuja ko ‘Abuja Struggle’ a Turance, ta cika shekara guda cur ba tare da fashi ba.
Sai dai kuma, yana daga cikin natijojin wadannan waki’o’in na mako guda a jere, yadda ya zama ranar Asabar 13/1/2018 gwamnatin Nijeriya ta nuna Shaikh Ibraheem Zakzaky a Talabijin, inda ya yi bayani a kan yanayin halin da yake ciki, ya kuma yi godiya ga ’yan Nijeriya da ke yi masa addu’a.
Kodayake sun yayyanke video din (editing), amma dai ya faranta ran masoyansa, ko ba komai ran nan ne karon farko da aka gan shi a ‘Video’ aka ji maganarsa tun bayan kama shi da Sojoji suka yi a ranar 14/12/2015, kimanin shekaru biyu da wata daya tsakanin kamun nasa da nuna shi a farko.
WAKI’O’IN GABAN OFISHIN NHRC
A ranar Litinin 16/4/2018 ’yan sanda suka sake bude wa ’yan’uwa masu Muzaharar kira a saki Shaikh Ibraheem Zakzaky wuta a kusa da ofishin Hukumar Kare Hakkin Dan’adam (NHRC) da ke Abuja. Sun jikkata ’yan’uwa da dama a yayin harbi da Tiyagas, ruwan zafi da kuma harsashi mai rai.
Cikin wadanda suka raunata har da Ahmad Rufa’i Abubakar Dodo, wanda Allah ya kaddara shahadarsa bayan kwana biyu. A ranar 19/4/2018 ya yi Shahada a wani asibiti a garin Kano. A wannan ranar ’yan sanda sun kama ’yan’uwa kusan 100.
An sanya ranar 23/4/2018 ne a matsayin ranar da za a yi jana’izar Shahid Ahmad Rufa’i, inda aka yi Muzahara zuwa Ofishin Hukumar Kare Hakkin na Dan’adam (NHRC) a Abujan, bayan an kai masu koke cewa wannan gawar ’yan sanda sun harbe ta ne a gaban ofishinsu a makon da ya gabata, sun dauki hoton gawar sun yi bayanai, har ma an gudanar da Sallah ga Shahidin. A gaban ofishin Hukumar ’yan sanda suka sake bude wa ’yan uwa wuta, inda suka kama fiye da 100, tare da jikkata gomomi.
WAKI’O’IN KAI SHAIKH ZAKZAKY KOTU
Bayan dawo da Shaikh Zakzaky da matarsa garin Kaduna da kuma gurfanar da su a gaban wata kotu don yi masu haramtacciyar Shari’ar da El-Rufa’i ya shigar da su a madadin gwamnatin Jihar Kaduna, a ranar Laraba 20 ga Yuni, 2018, jajiberin ranar komawa kotu da Shaikh din, ’yan’uwa a Kaduna sun gudanar da gagarumar Muzaharar kira a saki Shaikh Zakzaky din da kuma yin Allah wadai da kai shi wannan kotun, alhali wata kotun ta yi umurni a sake shi tun fiye da shekara guda gwamnati ba ta bi umurnin ba. Nan ’yan sanda suka bude wuta a kan masu Muzaharar, inda suka raunata mutane uku, amma ba a samu Shahidi a wannan ranar ba.
Ranar Alhamis 21/6/2018 aka ayyana don dawowa kotu da ci gaba da shari’ar Shaikh Zakzaky (H), kodayake ba a yi zaman kotun ba, amma ’yan’uwa sun sake fitowa Muzaharar kira a saki Shaikh Zakzaky a garin na Kaduna, inda ’yan sanda suka sake bude wuta, sun shahadantar da mutum 3 masu suna; Shahid Imrana Ringim, Shahid Idris Alhasan Kaduna da kuma Shahid Sagir Adamu (Baba Bauchi), sun kuma jikkata da dama.
’Yan sandan sun tafi da gawar Shahid Sagir suka hada ta da ta wani dan sanda da suka kashe a wannan ranar, suka kai su dakin ajiye gawa a wani asibiti. Har zuwa yanzu (kimanin watanni hudu ke nan) ba su ba da gawarsa an masa jana’iza ba.
WAKI’O’IN RANAR ASHURA 1440/2018
Ranar 20/9/2018 ta dace da ranar Ashura ta shekarar 1440H, ’yan’uwa sun gudanar da Muzaharorin Ashura a dukkan birane da kauyukan kasar nan ciki har da birnin Tarayya Abuja.
Sai dai a Zariya ’yan sanda sun harba Tiyagas a kan masu Muzaharar bayan an tashi, inda suka raunata ’yan’uwa guda hudu. Wasu zauna-gari-banza sun dira a kan masu Muzaharar ta Ashura a garin Suleja, inda suka jikkata wasu mata da kananan yara. Sannan kuma wasu zauna-gari-banzan bisa rakiyar jami’an tsaro sun je da nufin kona Fudiyyar Anchau da Pambeguwa da ke Jihar Kaduna, sun wargaza ta suka tafi.
A Abuja kuwa, jami’an tsaron sun yi mummunan shiri, don kuwa har jami’an da ke kula da tsaron Shugaban kasa (Guards Brigade) sun fito sun rika bin Muzaharar, amma Allah ya nufi an kammala lafiya.
Sai a garin Potiskum da ke Jihar Yobe ne sojoji suka bude wuta bayan an kammala Muzaharar, suka raunata mutane hudu, daya mutumin gari ne, wanda a nan take Allah ya yi masa cikawa, mutum na biyu kuma da suka kashe shi ne Shahid Ali Zakariyya, wanda ya yi shahada bayan jinyar kwanaki 10 da harbin nasa.
WAKI’AR TATTAKI 2018 A ABUJA
Ranar Asabar 27/10/2018 aka fara waki’ar Tattakin Arba’in a garin Abuja. Sojoji sun bude wuta a kan masu Tattakin a daidai gadar Zuba, inda suka kashe mutum 6 a wannan ranar, tare da jikkata da dama.
Litinin 29/10/2018 sojojin suka sake bude wuta a kan masu Tattakin Arba’in ta yankin Maraba, inda suka kashe mutum akalla 40, tare da jikkata fiye da mutum 100.
Wanda ya jagoranci wannan kisan-kiyashin shi ne Kwamandan jami’an tsaro masu kula da fadar Shugaban kasa (Guards Brigade), Birgediya-Janar Musa Yusuf.
Washegari Talata, 30/10/2018, daidai da ranar Arba’in din Imam Husain (AS), gamayyar soja da ’yan sanda suka kuma bude wuta a kan ’yan’uwa a Abuja, suka kashe mutum biyar da jikkata da dama.
A jerin kwanaki uku din nan, an samu Shahidai akalla 49, yayin da fiye da mutum 110 suka jikkata. Sun kuma kama fiye da ’yan’uwa 200 har zuwa yanzu wasu suna tsare.
KARKAREWA
A takaice, wadannan wasu ne daga waki’o’in da na iya taskacewa sun auku a tsawon shekaru uku, tun bayan waki’ar Zariya ta Disambar 2015. Duk wannan yana daga cikin yunkurin gwamnatin Nijeriya karasa kwangilar da ta karbo daga Amurka da Isra’ila da Saudiyya na kokarin ganin bayan Shaikh Zakzaky da kawo karshen Harkar Musulunci a Nijeriya.
Insha Allah a rubutu na gaba za mu duba hannun Saudiyya da gudummawar Malaman Wahabiyawa a cikin wannan Waki’ar ta Zariya da abubuwan da suka biyo bayanta.
January 11, 2019
Shekaru 3 Da Kisan Kiyashin Zariya (5)
Daga Saifullahi M. Kabir
WAKI’O’IN DA SUKA BIYO BAYAN TA ZARIYA
Bayan waki’ar Zariya, wacce ta auku a tsakanin 12-14 ga Disamba, 2015, Gwamnatin Nijeriya ta rika daukar matakai na karfi, baya ga matakan karairayi don kawo karshen Harkar Musulunci da hana ta kowane irin motsi ko da na numfashi.
Yana daga makaman da Harkar Musulunci ke amfani da shi, shi ne su fito kan tituna a garuruwa su yi Muzaharori don bayyana wa Duniya halin da ake ciki, tare da kiran a saki Jagoransu daga haramtacciyar tsarewar da ake masa.
Wannan kuwa shi ne babban abin da Hukumar Nijeriya ta rika fada da shi. Duk sad da aka fito don yin Muzaharar, sai ta turo jami’anta su yi kokarin dakatarwa, a wasu lokutan ma har su bude wuta, su kashe wasu daga almajiran Shaikh Zakzaky.
An yi waki’o’i da dama bayan waki’ar Zariya, wasu a lokutan Muzaharar kiran a saki Shaikh Zakzaky, wasu kuma a wasu munasabobi kamar na Ashura da Tattakin Arba’in din Imam Husaini (AS).
Har ila yau, a wasu waki’o’in jami’an tsaron kan jikkata ’yan uwa ne, a wasu lokuta kuma har ma da kisan rayuka. Zan so in dan kawo wasu daga manya-manyan waki’o’in da suka auku a tsawon wadannan shekaru ukun da suka gabata.
WAKI’AR KADUNA
Waki'ar farko da aka yi a yayin Muzaharar kira a saki Shaikh Zakzaky (FreeZakzaky) a garin Kaduna ne, ranar Talata 15/12/2015, kwana guda bayan kama Malam Zakzaky (H). ’Yan sanda sun bude wuta suka kashe mutum bakwai nan take, suka kuma raunata wasu. Wasu ’yan’uwa shida kuwa, ’yan sanda sun kama, suka tafi da su da ransu ne, suka je suka kashe su. Ba su ba da gawarsu ba sai a ranar Litinin, bayan sun shafe kwanaki shida a hannunsu. Wannan ya sa Shahidan wannan waki’ar suka zama mutum 13. Akwai kuma mutane 10 da aka tsare su a wannan waki’ar, wadanda kotu ta wanke su daga tuhumar da ake yi masu bayan sun kwashe shekaru biyu a tsare.
An kuma samun Shahidi na 14, wato Shahid Idris Mando, wanda ya cika a ranar 17/4/2016, kimanin watanni 5 bayan waki'ar, bayan jinyar da ya sha na harbin da jami’an tsaron suka yi masa. An yi yi jana’izar Shahidai hudu a ranar Alhamis, Juma’a aka kuma yi ta mutum 3. Sauran mutum 6 din sai a ranar Litinin din da aka samu gawawwakinsu aka yi masu jana’iza.
Wannan ne farkon zaluncin da ya biyo bayan waki’ar Zariya. Duk da haka, bayan mako biyu da wannan ta’addancin, a ranar 2/1/2016 wasu matasa sun sake fitowa Muzaharar Free Zakzaky a Kaduna, inda suka faro daga Katsina Roundabout zuwa Leventis a cikin garin na Kaduna.
An ci gaba da gudanar da Muzaharori da tarukan da aka saba gudanarwa na Harkar Musulunci, duk da kuwa wasu ana yi lafiya, wasu kuma ana samun waki’o’i.
TUNAWA DA SHAHIDAN KUDUS, 2016
Abin da ya biyo bayan wannan waki'ar shi ne taron tunawa Shahidan Kudus da aka yi Darur Rahma ranar 25/7/2016, inda Mopol suka zo da dukkan shirinsu na auka wa, suka nemi hana gudanar da taron.
’Yan’uwa ba su fasa ba sai da suka yi addu’o’i da jawabai suka tashi. Bayan an watse suka harba Tiyagas da kokarin kama wasu ’yan’uwa, amma sai Allah (T) ya takaita lamarin.
A shekarar 2017 ma ’yan sandan sun kuma zuwa wajen taron a Darur-Rahma, inda suka harbi mutane hudu bayan an tashi a taron.
YUNKURIN DIRAR WA MASU TATTAKI ZUWA ABUJA
Sai kuma a ranar 6/8/2016, da wasu sojoji suka yi kokarin dira a kan wasu matasa da suka yi Tattaki daga Zariya suka nufi Abuja da nufin kiran a saki Shaikh Zakzaky. Sakamakon ido da aka saka masu a wannan lokacin da takardar manema labarai da Harka ta fitar dangane da mummunan nufin sojojin a kan matasan, sai Allah ya tunkude sharrinsu, sai bai zama waki'a ba, ba su harba ko kama kowa ba. Suka tilasta matasan su juya, amma duk da haka sai da matasan suka san yadda suka yi suka shiga garin Abuja a wannan lokacin a kokarinsu na bayyana wa duniya halin da Shaikh Zakzaky ke ciki.
MUZAHARAR FREE ZAKZAKY A ZARIYA
Alhamis, 11/8/2016 ’yan sanda suka bude wa masu Muzaharar Free Zakzaky wuta da harbi da Tiyagas a daidai Kofar Doka Zariya, suka kama mutum 1, amma ba su harbi kowa da harsashi mai rai ba.
WAKI’AR FARKO A MUZAHARAR ABUJA
Mako biyu bayan hakan, aka kira gagarumar Muzaharar ‘Free Zakzaky’ a Abuja a ranar Alhamis 22/9/2018. A wannan ranar ’yan sanda sun yi ruwan Tiyagas da ma harsashi, sun raunata ’yan’uwa da dama. Sannan suka kama wasu mutum 12. Daga baya suka ba da belin yara biyar a ranar. Mutum bakwai din, wadanda Sistoci guda 3 ne da Burazu 4, sun kai su kurkukun Keffi suka tsare.
Wannan ne karon farko da jami’an tsaro suka fara dira a kan masu Muzahara da harbi a Abuja. Amma Allah bai nufi an samu Shahidi ba.
SOME-SOMEN WAKI’AR ASHURA 2016
Bayan haka aka fara some-somen waki'ar Ashura ta shekarar 2016. Kafin zuwan ranar Ashura din a garin Jos, jami’an tsaron soji sun rika yin barazana ga duk mai tafiya da bakin kaya zuwa wajen zaman juyayin Ashura. Haka ma a Kaduna, jami’an ’yan sanda sun rika bi suna kokarin dakile masu Tattaki zuwa wajen zaman Ashura a tsawon ranekun zaman.
A ranar 9/10/2016, ’yan sanda a Kaduna, sun rika kama ’yan’uwa a hanyoyi daban-daban. Kamar akwai wasu da suka baro Hayin Danmani za su je Markaz, Malam Ahmad Rigasa da iyalansa kananan yara, ’yan sanda suka kama su. Haka ma cikin masu tahowa daga yankin Nasarawa/Barnawa, su Injiniya Mansur Karofi, ’yan sanda sun kama su, bayan sun harba masu Tiyagas a kan hanyar tasu ta zuwa wajen zaman Ashura, sannan suka kai su kotu. Daga nan aka yi gidan kurkuku da su.
Kananan yaran kuwa, sai daga baya aka ba da belin su. A yayin da wata Sista mai suna Malama Salamatu Abdullahi, sai da ta yi kusan wata uku cur a tsare a kurkukun Kaduna kafin kotu ta yarda ta ba da belinta. Sauran mazan kuwa, yanzu haka fiye da shekaru biyu ana tsare da su. Laifinsu kawai shi ne an kama su a kan hanya za su je zaman juyayin Imam Husaini (AS) a lokacin Ashura. An shiga kotu ya kai kusan sau 30 har yau ana dage-dagen shari’ar.
Wani zaluncin sarari dangane da wadannan bayin Allah din shi ne farkon kai su kotu a ranar 10/10/2016, kwana 1 bayan kama su, kotun ta nemi ’yan sanda su gabatar da shaida a kan wadanda suke zargin, amma Sifeton na ’yan sanda mai suna Dogara, wanda kuma shi ne ‘Prosecutor’ din, ya ce suna rokon kotu ta ba su nan da makonni biyu don gabatar da shaidun. Nan kuwa Alkali ya sa aka kai ’yan uwan kurkuku zuwa lokacin da za a koma Shari’ar. Tun daga ran nan suka fara ganin zalunci har yau!
WAKI’AR ASHURA 2016
A ranar Laraba, 12/10/2016 (Ranar Ashura) aka yi waki'o'in Ashura a garuruwan Funtuwa, Kano, Sakkwato, Kaduna da Jos.
A duk garuruwan da aka yi waki’ar, garin Jos ne kawai Allah ya takaita ba a samu Shahidi ba, amma an yi zaluncin da ya kai matuka, wanda ya yi sanadiyyar rushe Markaz din ’yan’uwa na garin da jikkata gomomin ’yan’uwa da kama ’yan’uwa maza da mata, yara da manya kusan mutum 45, aka tsare su a kurkuku na tsawon watanni biyu kafin kotu ta ba da belin su.
A garin Funtuwa ta Jihar Katsina, an samu Shahidai 10 nan take. A yayin da jami’an tsaron suka kama ’yan’uwa kusan 37 aka tsare su tsawon watanni.
A Kano ma ’yan sandan da kansu suka debo ’yan iskan gari a cikin motocinsu, suka rika kokarin auka wa Muzaharar. Allah bai nufi za a yi waki’a mai tsanani a ran nan ba. Amma daga baya jami’an tsaron sun kashe wani Haris mai lura da zirga-zirgan ababen hawa (Traffic), Shahid Ja’afar Ali.
A garin Sakkwato ma ’yan iskan gari sun kashe wani dan uwa, Shahid Alhaji Farouk Gwadangwaji a wannan ranar ta Ashura, wanda suka kashe shi bayan kammala Muzaharar.
A garin Kaduna ma, sai da aka tashi Muzaharar lafiya, sannan da yamma jami’an tsaron tare da hadin gwiwar ’yan iskan gari suka auka wa ’yan’uwa a Markaz, inda a nan ma aka samu Shahidai 3, sannan kuma suka kona Markaz din. Bayan sun sace kayan cikin ta suka rushe ta, suka kuma je makarantar Fudiyya da ke Layin Kosai suka lalata ta.
Kwanaki uku bayan waki’ar Ashura a garin Kaduna, a ranar 15/10/2016 wasu ’yan’uwa suka je don su share Markaz din da aka rusa, nan take ’yan sanda suka zo da ’yan iskan gari, suka dira a kan ’yan uwan, suka kashe mutum daya nan take, suka jikkata da dama.
Daga nan jami’an tsaron suka kuma raka ’yan iskan gari zuwa unguwar Mu’azu, inda nan ma suka rushe makarantar Fudiyyar unguwar. Suka kuma shiga gidan wani dan’uwa, Sharif Awwal a Kinkanau suka samu karamar yarinya a ciki, suka hau ta da duka, suka ji mata rauni a ka, sannan suka je gidan wani dan’uwa Alhaji Usman shi ma suka lalata shi, suka kwashe kayayyakin da ke ciki.
WAKI’AR TATTAKI 2016
Waki’ar Tattakin Arba’in din Imam Husain (AS) a yankin Kano, ta auku ne a ranar Litinin 14/11/2016, inda ’yan sanda suka tare kan titi a daidai lokacin da masu Tattakin suka zo wani gari da ake kira karfi a Jihar Kano, suka bude wuta. Nan take suka kashe mutanen da har yanzu ba a tabbatar da adadinsu ba, sai dai akalla ana da tabbacin ba su gaza mutum 25 ba.
Jami’an tsaron sun sace gawawwakin wadanda suka kashe sun je sun bizne su a kabarin bai-daya, in ban da mutum 8 da suka ba da gawawwakinsu. Cikin wanda suka kashe har da jaririya ’yar kimanin watanni 8 da haihuwa mai suna Zainabul Kubra.
A wannan waki’ar, ’yan sandan sun kama mutane kusan 90 a farko, suka ba da belin kananan yara daga baya, a yayin da kusan mutum 50 suka shafe tsawon watanni bakwai a kurkukun Kano, kafin kotu ta ba da belin su.
A ranar 5/3/2017 ne Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya furta da bakinsa cewa shi ya ba ’yan sanda umurnin bude wannan wutar da aka yi a kan masu Tattakin da ta jawo rasuwar mutane 25 a lokacin da yake ganawa da wasu Malamai da suka ziyarce shi a gidan gwamnati.
YUNKURIN AUKA WA ’YAN’UWA A SAKKWATO
Ranar Laraba 27/9/2017, Ashurar shekarar 1439 ta rage saura kwanaki kamar hudu, gwamnatin Jihar Sakkwato ta sanar da cewa ta haramta duk wani motsi ko muzahara da ’yan’uwa Musulmi almajiran Shaikh Zakzaky za su gudanar a duk fadin Jihar.
Washegari, Alhamis sai ga ’yan sanda dauke da muggan makamai a karkashin Kwamishinan ’yan sandan Jihar, Muhammad Abdulkadir sun zo Markaz, wadda ke kusa da gidan Shaikh Kasimu Umar. Lokacin da Shehin Malamin ya nufo Markaz din, sun tare shi sun yi magana da shi, ya tabbatar masu da cewa ba wani abu za a yi ba face abin da aka saba gudanarwa na zaman Ashura, sai suka tafi.
Ranar Juma’a sai suka kuma dawowa, suka daidaici lokacin fitowar Shaikh Kasim zuwa Markaz, sai suka bi ta hanyar, inda suka yi kokarin nuna an tare masu hanya ne, nan suka kama wasu ’yan’uwa guda 6, suka kai su State CID, sannan kuma suka girke jami’an tsaro a kowane lungun unguwar har zuwa wayewar gari.
Allah ya takaita lamarin, a yayin da ’yan’uwa suka samu sabati, kuma aka dauki matakan kaucewa duk wani mugun nufinsu, har ya zama ranar 1/10/2017, wanda ta yi daidai da 10/1/1439H, an gudanar da Muzaharar Ashura da asubahin ranar a Sakkwato, kuma an tashi lafiya. Sai dai an kama mutane 4 a garin Bodinga bayan kammala Muzaharar Ashura a garin, ciki har da Na’ibin Wakilin ’yan’uwa na garin, Malam Abubakar Modi. Sai da suka yi watanni hudu da kwana 10 aka sake su.
A ranar Lahadi, 22/10/2017 ’yan sandan sun kuma yunkurin auka wa ’yan’uwa a Sakkwato, inda suka je wajen da aka rufe Muzaharar Free Zakzaky. Da suka tarar an tashi sai suka harba Tiyagas. Daga nan suka nufi Markaz, inda suka tarar ba kowa, sai suka tafi.
A daidai wannan ranar, ’yan sanda sun bude wuta a kan masu Muzahara a Kaduna, inda suka jikkata ’yan uwa da dama, suka kuma kama mutane hudu.
WAKI’AR TATTAKI 2017
Shekara guda bayan wancan aukawar da ’yan sanda suka yi a kan masu Tattakin Arba’in din Imam Husaini (AS) daga yankin Kano, a ranar 5/11/2017 aka fara Tattakin wannan shekarar ta 1439H daga yankin Kano. An taso da misalin karfe 10:00ns daga Kofar Mazugal, aka yi Sallar Zuhuraini a kofar Nasarawa, sannan aka ci gaba da tafiya har inda aka rufe Tattakin a Dangi ‘Roundabout’ gab da wajen da ake ce wa Gadar Lado da nufin washegari za a tashi daga wannan wajen.
Kwatsam! Sai ga ’yan sanda nan sun taho cikin mota 10 a guje, suna zuwa kafin wasu su sauka a motocinsu ma suka fara bude wuta a kan ’yan’uwan da suke wajen ba su gama watsewa ba. Nan suka harbi ’yan uwa masu yawa, aka samu Shahidai guda uku; A’isha Muhammad Azare, Husaina Dauda Nalado Kano da kuma Shahid Umar Ahmad Gano, wanda shi sun tafi da gawarsa ne sai bayan kwanaki 28 suka ba da ita aka yi mata jana’iza.
Da yake an tsara bayan an kammala Tattakin kowane yanki, za a hadu ne a Abuja a yi taron Arba’in a ranar 20 ga Safar din shekarar. A wannan ranar wacce ta dace da 10/11/2017, jami’an tsaro sun kuma bude wuta a kan ’yan uwa masu taron Arba’in din, inda suka jikkata da dama da barkonun tsohuwa.
Za mu ci gaba insha Allah.
WAKI’O’IN DA SUKA BIYO BAYAN TA ZARIYA
Bayan waki’ar Zariya, wacce ta auku a tsakanin 12-14 ga Disamba, 2015, Gwamnatin Nijeriya ta rika daukar matakai na karfi, baya ga matakan karairayi don kawo karshen Harkar Musulunci da hana ta kowane irin motsi ko da na numfashi.
Yana daga makaman da Harkar Musulunci ke amfani da shi, shi ne su fito kan tituna a garuruwa su yi Muzaharori don bayyana wa Duniya halin da ake ciki, tare da kiran a saki Jagoransu daga haramtacciyar tsarewar da ake masa.
Wannan kuwa shi ne babban abin da Hukumar Nijeriya ta rika fada da shi. Duk sad da aka fito don yin Muzaharar, sai ta turo jami’anta su yi kokarin dakatarwa, a wasu lokutan ma har su bude wuta, su kashe wasu daga almajiran Shaikh Zakzaky.
An yi waki’o’i da dama bayan waki’ar Zariya, wasu a lokutan Muzaharar kiran a saki Shaikh Zakzaky, wasu kuma a wasu munasabobi kamar na Ashura da Tattakin Arba’in din Imam Husaini (AS).
Har ila yau, a wasu waki’o’in jami’an tsaron kan jikkata ’yan uwa ne, a wasu lokuta kuma har ma da kisan rayuka. Zan so in dan kawo wasu daga manya-manyan waki’o’in da suka auku a tsawon wadannan shekaru ukun da suka gabata.
WAKI’AR KADUNA
Waki'ar farko da aka yi a yayin Muzaharar kira a saki Shaikh Zakzaky (FreeZakzaky) a garin Kaduna ne, ranar Talata 15/12/2015, kwana guda bayan kama Malam Zakzaky (H). ’Yan sanda sun bude wuta suka kashe mutum bakwai nan take, suka kuma raunata wasu. Wasu ’yan’uwa shida kuwa, ’yan sanda sun kama, suka tafi da su da ransu ne, suka je suka kashe su. Ba su ba da gawarsu ba sai a ranar Litinin, bayan sun shafe kwanaki shida a hannunsu. Wannan ya sa Shahidan wannan waki’ar suka zama mutum 13. Akwai kuma mutane 10 da aka tsare su a wannan waki’ar, wadanda kotu ta wanke su daga tuhumar da ake yi masu bayan sun kwashe shekaru biyu a tsare.
An kuma samun Shahidi na 14, wato Shahid Idris Mando, wanda ya cika a ranar 17/4/2016, kimanin watanni 5 bayan waki'ar, bayan jinyar da ya sha na harbin da jami’an tsaron suka yi masa. An yi yi jana’izar Shahidai hudu a ranar Alhamis, Juma’a aka kuma yi ta mutum 3. Sauran mutum 6 din sai a ranar Litinin din da aka samu gawawwakinsu aka yi masu jana’iza.
Wannan ne farkon zaluncin da ya biyo bayan waki’ar Zariya. Duk da haka, bayan mako biyu da wannan ta’addancin, a ranar 2/1/2016 wasu matasa sun sake fitowa Muzaharar Free Zakzaky a Kaduna, inda suka faro daga Katsina Roundabout zuwa Leventis a cikin garin na Kaduna.
An ci gaba da gudanar da Muzaharori da tarukan da aka saba gudanarwa na Harkar Musulunci, duk da kuwa wasu ana yi lafiya, wasu kuma ana samun waki’o’i.
'Yan uwa a sahun Muzaharar #FreeZakzaky a Kaduna
TUNAWA DA SHAHIDAN KUDUS, 2016
Abin da ya biyo bayan wannan waki'ar shi ne taron tunawa Shahidan Kudus da aka yi Darur Rahma ranar 25/7/2016, inda Mopol suka zo da dukkan shirinsu na auka wa, suka nemi hana gudanar da taron.
’Yan’uwa ba su fasa ba sai da suka yi addu’o’i da jawabai suka tashi. Bayan an watse suka harba Tiyagas da kokarin kama wasu ’yan’uwa, amma sai Allah (T) ya takaita lamarin.
A shekarar 2017 ma ’yan sandan sun kuma zuwa wajen taron a Darur-Rahma, inda suka harbi mutane hudu bayan an tashi a taron.
Jami'an tsaro na fitowa daga Darur Rahma kafin su dirar ma Yan uwa
YUNKURIN DIRAR WA MASU TATTAKI ZUWA ABUJA
Sai kuma a ranar 6/8/2016, da wasu sojoji suka yi kokarin dira a kan wasu matasa da suka yi Tattaki daga Zariya suka nufi Abuja da nufin kiran a saki Shaikh Zakzaky. Sakamakon ido da aka saka masu a wannan lokacin da takardar manema labarai da Harka ta fitar dangane da mummunan nufin sojojin a kan matasan, sai Allah ya tunkude sharrinsu, sai bai zama waki'a ba, ba su harba ko kama kowa ba. Suka tilasta matasan su juya, amma duk da haka sai da matasan suka san yadda suka yi suka shiga garin Abuja a wannan lokacin a kokarinsu na bayyana wa duniya halin da Shaikh Zakzaky ke ciki.
'Yan uwa na tattaunawa da Sojojin a yayin Tattakin a hanyar Abuja
MUZAHARAR FREE ZAKZAKY A ZARIYA
Alhamis, 11/8/2016 ’yan sanda suka bude wa masu Muzaharar Free Zakzaky wuta da harbi da Tiyagas a daidai Kofar Doka Zariya, suka kama mutum 1, amma ba su harbi kowa da harsashi mai rai ba.
WAKI’AR FARKO A MUZAHARAR ABUJA
Mako biyu bayan hakan, aka kira gagarumar Muzaharar ‘Free Zakzaky’ a Abuja a ranar Alhamis 22/9/2018. A wannan ranar ’yan sanda sun yi ruwan Tiyagas da ma harsashi, sun raunata ’yan’uwa da dama. Sannan suka kama wasu mutum 12. Daga baya suka ba da belin yara biyar a ranar. Mutum bakwai din, wadanda Sistoci guda 3 ne da Burazu 4, sun kai su kurkukun Keffi suka tsare.
'Yan uwa mata da jami'an tsaron suka kama, bayan sun fito daga Kurkuku
Wannan ne karon farko da jami’an tsaro suka fara dira a kan masu Muzahara da harbi a Abuja. Amma Allah bai nufi an samu Shahidi ba.
SOME-SOMEN WAKI’AR ASHURA 2016
Bayan haka aka fara some-somen waki'ar Ashura ta shekarar 2016. Kafin zuwan ranar Ashura din a garin Jos, jami’an tsaron soji sun rika yin barazana ga duk mai tafiya da bakin kaya zuwa wajen zaman juyayin Ashura. Haka ma a Kaduna, jami’an ’yan sanda sun rika bi suna kokarin dakile masu Tattaki zuwa wajen zaman Ashura a tsawon ranekun zaman.
A ranar 9/10/2016, ’yan sanda a Kaduna, sun rika kama ’yan’uwa a hanyoyi daban-daban. Kamar akwai wasu da suka baro Hayin Danmani za su je Markaz, Malam Ahmad Rigasa da iyalansa kananan yara, ’yan sanda suka kama su. Haka ma cikin masu tahowa daga yankin Nasarawa/Barnawa, su Injiniya Mansur Karofi, ’yan sanda sun kama su, bayan sun harba masu Tiyagas a kan hanyar tasu ta zuwa wajen zaman Ashura, sannan suka kai su kotu. Daga nan aka yi gidan kurkuku da su.
Kananan yaran kuwa, sai daga baya aka ba da belin su. A yayin da wata Sista mai suna Malama Salamatu Abdullahi, sai da ta yi kusan wata uku cur a tsare a kurkukun Kaduna kafin kotu ta yarda ta ba da belinta. Sauran mazan kuwa, yanzu haka fiye da shekaru biyu ana tsare da su. Laifinsu kawai shi ne an kama su a kan hanya za su je zaman juyayin Imam Husaini (AS) a lokacin Ashura. An shiga kotu ya kai kusan sau 30 har yau ana dage-dagen shari’ar.
Wasu daga kananan yaran da yan Sandan suka kama
Wani zaluncin sarari dangane da wadannan bayin Allah din shi ne farkon kai su kotu a ranar 10/10/2016, kwana 1 bayan kama su, kotun ta nemi ’yan sanda su gabatar da shaida a kan wadanda suke zargin, amma Sifeton na ’yan sanda mai suna Dogara, wanda kuma shi ne ‘Prosecutor’ din, ya ce suna rokon kotu ta ba su nan da makonni biyu don gabatar da shaidun. Nan kuwa Alkali ya sa aka kai ’yan uwan kurkuku zuwa lokacin da za a koma Shari’ar. Tun daga ran nan suka fara ganin zalunci har yau!
WAKI’AR ASHURA 2016
A ranar Laraba, 12/10/2016 (Ranar Ashura) aka yi waki'o'in Ashura a garuruwan Funtuwa, Kano, Sakkwato, Kaduna da Jos.
A duk garuruwan da aka yi waki’ar, garin Jos ne kawai Allah ya takaita ba a samu Shahidi ba, amma an yi zaluncin da ya kai matuka, wanda ya yi sanadiyyar rushe Markaz din ’yan’uwa na garin da jikkata gomomin ’yan’uwa da kama ’yan’uwa maza da mata, yara da manya kusan mutum 45, aka tsare su a kurkuku na tsawon watanni biyu kafin kotu ta ba da belin su.
A garin Funtuwa ta Jihar Katsina, an samu Shahidai 10 nan take. A yayin da jami’an tsaron suka kama ’yan’uwa kusan 37 aka tsare su tsawon watanni.
Wani Dattijo, daya daga cikin Shahidan Ashura a Funtua
A Kano ma ’yan sandan da kansu suka debo ’yan iskan gari a cikin motocinsu, suka rika kokarin auka wa Muzaharar. Allah bai nufi za a yi waki’a mai tsanani a ran nan ba. Amma daga baya jami’an tsaron sun kashe wani Haris mai lura da zirga-zirgan ababen hawa (Traffic), Shahid Ja’afar Ali.
A garin Sakkwato ma ’yan iskan gari sun kashe wani dan uwa, Shahid Alhaji Farouk Gwadangwaji a wannan ranar ta Ashura, wanda suka kashe shi bayan kammala Muzaharar.
A garin Kaduna ma, sai da aka tashi Muzaharar lafiya, sannan da yamma jami’an tsaron tare da hadin gwiwar ’yan iskan gari suka auka wa ’yan’uwa a Markaz, inda a nan ma aka samu Shahidai 3, sannan kuma suka kona Markaz din. Bayan sun sace kayan cikin ta suka rushe ta, suka kuma je makarantar Fudiyya da ke Layin Kosai suka lalata ta.
Kwanaki uku bayan waki’ar Ashura a garin Kaduna, a ranar 15/10/2016 wasu ’yan’uwa suka je don su share Markaz din da aka rusa, nan take ’yan sanda suka zo da ’yan iskan gari, suka dira a kan ’yan uwan, suka kashe mutum daya nan take, suka jikkata da dama.
Daga nan jami’an tsaron suka kuma raka ’yan iskan gari zuwa unguwar Mu’azu, inda nan ma suka rushe makarantar Fudiyyar unguwar. Suka kuma shiga gidan wani dan’uwa, Sharif Awwal a Kinkanau suka samu karamar yarinya a ciki, suka hau ta da duka, suka ji mata rauni a ka, sannan suka je gidan wani dan’uwa Alhaji Usman shi ma suka lalata shi, suka kwashe kayayyakin da ke ciki.
WAKI’AR TATTAKI 2016
Waki’ar Tattakin Arba’in din Imam Husain (AS) a yankin Kano, ta auku ne a ranar Litinin 14/11/2016, inda ’yan sanda suka tare kan titi a daidai lokacin da masu Tattakin suka zo wani gari da ake kira karfi a Jihar Kano, suka bude wuta. Nan take suka kashe mutanen da har yanzu ba a tabbatar da adadinsu ba, sai dai akalla ana da tabbacin ba su gaza mutum 25 ba.
Jami’an tsaron sun sace gawawwakin wadanda suka kashe sun je sun bizne su a kabarin bai-daya, in ban da mutum 8 da suka ba da gawawwakinsu. Cikin wanda suka kashe har da jaririya ’yar kimanin watanni 8 da haihuwa mai suna Zainabul Kubra.
Jaririya Zainab, daya daga wadanda aka kashe a yayin Tattakin
A wannan waki’ar, ’yan sandan sun kama mutane kusan 90 a farko, suka ba da belin kananan yara daga baya, a yayin da kusan mutum 50 suka shafe tsawon watanni bakwai a kurkukun Kano, kafin kotu ta ba da belin su.
Yayin da yan sanda suke ruwan wuta a kan masu Tattakin Arba'een din
A ranar 5/3/2017 ne Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya furta da bakinsa cewa shi ya ba ’yan sanda umurnin bude wannan wutar da aka yi a kan masu Tattakin da ta jawo rasuwar mutane 25 a lokacin da yake ganawa da wasu Malamai da suka ziyarce shi a gidan gwamnati.
YUNKURIN AUKA WA ’YAN’UWA A SAKKWATO
Ranar Laraba 27/9/2017, Ashurar shekarar 1439 ta rage saura kwanaki kamar hudu, gwamnatin Jihar Sakkwato ta sanar da cewa ta haramta duk wani motsi ko muzahara da ’yan’uwa Musulmi almajiran Shaikh Zakzaky za su gudanar a duk fadin Jihar.
Washegari, Alhamis sai ga ’yan sanda dauke da muggan makamai a karkashin Kwamishinan ’yan sandan Jihar, Muhammad Abdulkadir sun zo Markaz, wadda ke kusa da gidan Shaikh Kasimu Umar. Lokacin da Shehin Malamin ya nufo Markaz din, sun tare shi sun yi magana da shi, ya tabbatar masu da cewa ba wani abu za a yi ba face abin da aka saba gudanarwa na zaman Ashura, sai suka tafi.
Yayin da Shaikh Qaseem ke magana da jami'an tsaron.
Ranar Juma’a sai suka kuma dawowa, suka daidaici lokacin fitowar Shaikh Kasim zuwa Markaz, sai suka bi ta hanyar, inda suka yi kokarin nuna an tare masu hanya ne, nan suka kama wasu ’yan’uwa guda 6, suka kai su State CID, sannan kuma suka girke jami’an tsaro a kowane lungun unguwar har zuwa wayewar gari.
Allah ya takaita lamarin, a yayin da ’yan’uwa suka samu sabati, kuma aka dauki matakan kaucewa duk wani mugun nufinsu, har ya zama ranar 1/10/2017, wanda ta yi daidai da 10/1/1439H, an gudanar da Muzaharar Ashura da asubahin ranar a Sakkwato, kuma an tashi lafiya. Sai dai an kama mutane 4 a garin Bodinga bayan kammala Muzaharar Ashura a garin, ciki har da Na’ibin Wakilin ’yan’uwa na garin, Malam Abubakar Modi. Sai da suka yi watanni hudu da kwana 10 aka sake su.
A ranar Lahadi, 22/10/2017 ’yan sandan sun kuma yunkurin auka wa ’yan’uwa a Sakkwato, inda suka je wajen da aka rufe Muzaharar Free Zakzaky. Da suka tarar an tashi sai suka harba Tiyagas. Daga nan suka nufi Markaz, inda suka tarar ba kowa, sai suka tafi.
A daidai wannan ranar, ’yan sanda sun bude wuta a kan masu Muzahara a Kaduna, inda suka jikkata ’yan uwa da dama, suka kuma kama mutane hudu.
WAKI’AR TATTAKI 2017
Shekara guda bayan wancan aukawar da ’yan sanda suka yi a kan masu Tattakin Arba’in din Imam Husaini (AS) daga yankin Kano, a ranar 5/11/2017 aka fara Tattakin wannan shekarar ta 1439H daga yankin Kano. An taso da misalin karfe 10:00ns daga Kofar Mazugal, aka yi Sallar Zuhuraini a kofar Nasarawa, sannan aka ci gaba da tafiya har inda aka rufe Tattakin a Dangi ‘Roundabout’ gab da wajen da ake ce wa Gadar Lado da nufin washegari za a tashi daga wannan wajen.
Kwatsam! Sai ga ’yan sanda nan sun taho cikin mota 10 a guje, suna zuwa kafin wasu su sauka a motocinsu ma suka fara bude wuta a kan ’yan’uwan da suke wajen ba su gama watsewa ba. Nan suka harbi ’yan uwa masu yawa, aka samu Shahidai guda uku; A’isha Muhammad Azare, Husaina Dauda Nalado Kano da kuma Shahid Umar Ahmad Gano, wanda shi sun tafi da gawarsa ne sai bayan kwanaki 28 suka ba da ita aka yi mata jana’iza.
Da yake an tsara bayan an kammala Tattakin kowane yanki, za a hadu ne a Abuja a yi taron Arba’in a ranar 20 ga Safar din shekarar. A wannan ranar wacce ta dace da 10/11/2017, jami’an tsaro sun kuma bude wuta a kan ’yan uwa masu taron Arba’in din, inda suka jikkata da dama da barkonun tsohuwa.
Za mu ci gaba insha Allah.
January 07, 2019
Manzon Allah (S) Ramzi Ne, Abin Koyi - Inji Shaikh Zakzaky (H)
Shaikh Zakzaky ya yi bayani a kan cewa Manzon Allah ne cikakken mutum, kuma abin koyi ga dukkan talikai. Ya Kuma jaddada alkawarin Allah ne dawo da addinin Musulunci ya yi iko da doron Duniya.
Takaicin Shaikh Zakzaky A Kan Kashe Jami'an Tsaron Nigeria
A ciki, Jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya, Shaikh Ibraheem Zakzaky ya nuna takaicinsa dangane da yadda ake tura jami'an tsaron Sojoji da Yan Sandan Nijeriya ana kashe su da sunan fada da Boko Haram.
January 06, 2019
Shekaru 3 Da Kisan Kiyashin Zariya (4)
Daga Saifullahi M. Kabir
BAYAN HUKUNCIN KOTU
Bayan hukuncin babbar kotun Tarayya da ke Abuja na umurnin sakin Shaikh Zakzaky da maidakinsa Malama Zeenah, da biyan su diyya da sauran sharudda kamar yadda suka gabata, an rika samun kungiyoyi da daidaikun mutane suna jaddada kira ga gwamnatin Nijeriya karkashin Shugaban kasa Muhammadu Buhari kan ta mutunta umurnin na kotun kasa.
Bayan wannan hukuncin, wani tsohon Shugaban kungiyar Lauyoyin na kasa (NBA), Dakta Olisa Agbakoba, ya yi kira ga gwamnatin Buhari kan ta bi umurnin kotu wajen sakin Shaikh Zakzaky da maidakinsa.
Ya ce; “A matsayinsa na dan kasar nan, El-Zakzaky ya cancanci ’yanci. In kuwa akwai wani dalili na tsare shi, me ya sa ba za a bi umurnin kotu a sake shi ba, alabashi daga baya a kai shi kotu bisa wannan dalilin na daban?”
Shi ma tsohon Shugaban kungiyar Lauyoyin na Lagos, Mista Monday Ubani, ya jaddada cewa; “Wajibi ne gwamnatin Tarayya ta bi umurnin kotun Tarayya a cikin umurnin nata.”
A yayin da shi ma Festus Keyamo, wani fitaccen Lauya a garin Lagos din ya nanata cewa; “In har kotun kasa ta ba da matsaya a kan wani abu, to, wajibi ne gwamnati da al’ummar kasa su bi wannan matsayar.”
A ranar 10/12/2016, kimanin mako guda bayan hukuncin na kotun, kungiyar Lauyoyin ta kasa (NBA) a wajen wani taro da ta gudanar a garin Lagos, ta jaddada kira ga mutunta dokar ta kotu ga gwamnatin Shugaba Buhari.
Shugaban kungiyar, Abubakar Mahmod (SAN), ya bayyana matukar damuwarsu a kan rashin bin umurnin na kotun kasa, inda ya ce; “Ya sabawa duk wata doka a ce gwamnatin kasa ta ki bin umurnin kotu.”
Ya kuma jaddada kira a kan a gaggauta sakin Shaikh Zakzaky da matarsa kamar yadda kotun ta yi umurni. Tare kuma da kira ga mabiya Harkar Musulunci kan su rika mutunta dokoki da hakkokin sauran jama’a.
An kuma rika samun sakonnin taya murna ga Harkar Musulunci bisa nasarar da ta samu a yayin da ta kafawa masu zaluntar ta hujja da abin da suka yi imani da shi, kuma ta yi galaba a kansu. Kamar yadda wata kungiya mai suna ‘Mahdi Muslim Community’ da ke Nairobi a kasar Kenya ta fitar da takardar taya murna ga Harkar Musulunci a kan wannan nasarar, ta kuma jaddada kira ga gwamnatin Nijeriya kan ta gaggauta bin umurmin na kotun kasar, a ranar 7/12/2016.
Ganin yadda ake ta kiraye-kiraye ta ko’ina a kan gwamnati ta bi umurnin kotu, kwatsam sai ga wata kungiya da ake kira MURIC, wanda a farkon waki’ar Zariya sune farkon wadanda suka yi Allah-wadai da ta’addancin sojojin a kan ’yan kasa Musulmi, a wannan karon kuma bayan nasarar ’yan’uwa a kotu, sai kungiyar ta fito ta bakin Daraktanta, Farfesa Ishaka Akintola, wai ta bayyana Harkar Musulunci a matsayin kungiyar ’yan tashin hankali.
Sun bayyana hakan ne a ranar 5/12/2016, kwanaki uku bayan hukucin kotun Tarayyar ta Abuja, sai ga gwamnatin Kaduna ta fitar da abin da ta kira ‘White-Paper’, wadda take nuna matsayar gwamnatin Kaduna dangane da sakamakon rahoton JCI da ta kafa don binciken dalilin kisan kiyashin Zariya.
A cikin abin da ta kira ‘White-Paper’ din, gwamnatin Kadunan karkashin Gwamnan Jihar, Nasiru El-Rufa’i, ta bayyana matsayarta kan cewa za su bukaci gwamnatin Tarayya ta damka masu Shaikh Ibraheem Zakzaky don su gurfanar da shi a gaban kotu don su caje shi da laifuka daban-daban da ya aikata wa Jihar Kaduna a tsawon shekaru fiye da 30 na gudanar da Harkar Musulunci.
A nan, sai El-Rufa’i ya yi kunnen-uwar-shegu da kiran da kwamitin binciken na JCI ya yi a cikin rahoton da ya mika masa a ranar 15/7/2016, inda ya bukaci a hukunta Shugaban rundunar sojoji ta 1, ‘GOC 1-Division Army’ da ke Kaduna, Janar Oyebade, wanda shi ne ya jagoranci kashe mutum fiye da 347 da duk abin da ya faru a Zariya ranar 12-14/12/2015.
Kwatsam, ranar 1 ga Janairun 2017, sai ga Shugaban kasa Muhammadu Buhari a yayin da yake jawabin sabuwar shekara, ya kira ’yan’uwa Musulmi almajiran Shaikh Zakzaky da sunan ’yan’uwansa. Buhari ya ambaci cewa: “’Yan’uwanmu maza da mata na al’ummar Shi’a”, ya yi kira gare su a kan su kasance masu bin dokokin kasa.
Wannan furucin ya sa al’ummar Nijeriya sun yi caa a kansa ta hanyar mai da masa da martanin cewa shi ya fi kamata ya bi dokar kotun kasa, tunda har yau ba a samu wani laifi kwara daya da wadanda ya kira ’yan Shi’a ko Jagoransu ya aikata, wanda ya sabawa dokar kasar ba, sabanin shi da ya ki bin umurnin kotun kasa tsawon lokaci.
Wannan ya tilasta Kakakinsa, Malam Garba Shehu yin magana a ranar 2/1/2017, a yayin da yake hira da BBC, ya bayyana cewa, al’amarin tsare Shaikh Zakzaky sha’anin Jihar Kaduna ne, ba abin da ya shafi Shugaban kasa da shi. Ya kuma kara da bayyana cewa, wasu mutane sun daukaka kara bisa hukuncin kotun da ta ce a saki Shaikh Zakzaky. Sai dai bai fadi ko su waye mutanen da suka daukaka karar ba.
Ranar 16/1/2017 ne wa’adin da kotun Tarayya ta ba gwamnati kan ta saki Shaikh Zakzaky da matarsa ya cika, a yayin da har zuwa wannan lokacin ba su bi umurnin kotun ba. Sai a ranar 21/1/2-17 jaridar DAILY TRUST ta kawo wani labari daga fadar Shugaban kasa, inda suka bayyana cewa, suna ci gaba da tsare Shaikh Zakzaky ne saboda matsalar tsaro da bukatar jama’a. Suka kuma ce ita matarsa Malama Zeenah ba suna tsare da ita ba ne, tana kula da mai gidan nata ne a inda ake tsare da shi.
Idan ba ku manta ba, a baya mun kawo cewa, a ranar 13/6/2016, Lauyan DSS, Bar. Tijjani ya bayyana a gaban kotu cewa, ba ana tsare da Shaikh Zakzaky ba ne bisa tilasci. Ya ce ana ba shi kariya ne a inda aka aje shi bisa yardarsa. Har ma ya ce DSS sun yi masa maganin raunin da sojoji suka masa na Naira Miliyan 5 da rabi.
A ranar Alhamis, 20/4/2017 kuma, sai ga mataimakin Shugaban kasa, Farfesa Yemi Osibanjo ya rubuta a shafinsa na Twitter cewa, suna ci gaba da tsare Shaikh Zakzaky ne saboda matsalar tsaro. Ya kuma ce sun daukaka kara na hukuncin babban kotun Tarayyar da ta ce a saki Shaikh Zakzaky din.
In mai karatu yana lura, zai ga yadda maganganu suke sassabawa a tsakanin kwanaki daga jami’an gwamnatin, ta yadda suka kasa bayyana takamaiman dalili daya da ya sa suke tsare da Shaikh Zakzaky. Don haka a karshe suka ga ba mafita face kawai su mika Shaikh Zakzaky din zuwa ga gwamnatin Jihar Kaduna, don ta caje shi da kirkirarrun laifuffukan da ta ga dama.
WASU MATAKAN
Cikin matakan da Harkar Musulunci ta bi wajen bayyana zaluncin da aka mata da kuma kokarin samar da adalci daga dokoki da ka’ida na hukunta masu laifin yin wannan kisan kiyashin, kwamitin da ke fafutukar ganin an saki Shaikh Zakzaky da ke karkashin Harkar Musuluci, har ila yau, sun aika da koke zuwa ga Hukumar kare hakkin bil’adama ta Majalisar Dinkin Duniya (United Nations Human Rights Counsil) da ke Geneva, dangane da kisan kiyashin da aka yi a Zariya.
Bayan aikawa da wannan koken, UNHRC da ke Geneva din sun bai wa ‘FreeZakzaky Champaign Committee’ gayyata har sau uku a karo daban-daban, amma sai ofishin jakadancin Switzerland ta hana ‘Visa’ don amsa wannan gayyatar na zuwa ba da bayanai. Daga baya ma ofishin ya sanya takunkumi na tsawon shekaru uku ga Wakilan Kwamitin fafutukar ganin an saki Shaikh Zakzaky din.
Har ila yau, Harkar Musulunci ta shigar da karar duk masu hannu a kisan kiyashin Zariya a kotun hukunta manyan laifuka ta duniya, wato ‘International Criminal Court’ (ICC), wanda izuwa hada wannan rahoton Kotun na ICC ta kammala bincikenta a matakin farko dangane da kisan kiyashin, kuma har ma binciken nasu ya tabbatar da cewa sojojin Nijeriya sun aiwatar da wannan kisan kiyashin a Zariya. Ya zuwa yanzu ana jiran mataki na gaba ne, wanda shi ne kotun ICC din ta ayyana wadanda alhakin wannan kisan kiyashin na Zariya 2015 ya rataya a wuyansu. Daga nan sai matakin tuhumar su da ba da ‘waranti’ na a kama su a gurfanar da su a gabanta a mazauninta da ke Hague a Netherlands.
Harkar Musulunci ta kuma rika shirya Muzaharori a Abuja da sauran garuruwa da kuma gabatar da tarurrukan wayar da kan al’umma da fadakarwa, tare da bayyana zaluncin da aka yi a Zariya, musamman ga ’yan boko da masu rajin kare hakkin bil’adam, inda aka samu da dama suka rika fitowa suna Allah wadai, musamman a kan ci gaban gwamnatin Buhari na yunkurin kawar da Harkar, da auka wa ’yan uwa Musulmi a duk lokacin da suka fito don yin Muzahara ko wani taro da ya shafi addini da fahimtarsu.
Ita kuwa gwamnati a kowane lokaci ba ta da aikin da ya wuce ci gaba da fada da Harkar Musuluncin a matakin Jiha da matakin Tarayya. Tun bayan waki’ar ta Zariya, jami’an tsaro sun ci gaba da auka wa ’yan’uwa a garuruwa daban-daban a lokuta daban-daban, kamar yadda za mu kawo su daki-daki a ci gaban rubutunmu in Allah ya nufa.
BAYAN HUKUNCIN KOTU
Bayan hukuncin babbar kotun Tarayya da ke Abuja na umurnin sakin Shaikh Zakzaky da maidakinsa Malama Zeenah, da biyan su diyya da sauran sharudda kamar yadda suka gabata, an rika samun kungiyoyi da daidaikun mutane suna jaddada kira ga gwamnatin Nijeriya karkashin Shugaban kasa Muhammadu Buhari kan ta mutunta umurnin na kotun kasa.
Bayan wannan hukuncin, wani tsohon Shugaban kungiyar Lauyoyin na kasa (NBA), Dakta Olisa Agbakoba, ya yi kira ga gwamnatin Buhari kan ta bi umurnin kotu wajen sakin Shaikh Zakzaky da maidakinsa.
Ya ce; “A matsayinsa na dan kasar nan, El-Zakzaky ya cancanci ’yanci. In kuwa akwai wani dalili na tsare shi, me ya sa ba za a bi umurnin kotu a sake shi ba, alabashi daga baya a kai shi kotu bisa wannan dalilin na daban?”
Shi ma tsohon Shugaban kungiyar Lauyoyin na Lagos, Mista Monday Ubani, ya jaddada cewa; “Wajibi ne gwamnatin Tarayya ta bi umurnin kotun Tarayya a cikin umurnin nata.”
A yayin da shi ma Festus Keyamo, wani fitaccen Lauya a garin Lagos din ya nanata cewa; “In har kotun kasa ta ba da matsaya a kan wani abu, to, wajibi ne gwamnati da al’ummar kasa su bi wannan matsayar.”
A ranar 10/12/2016, kimanin mako guda bayan hukuncin na kotun, kungiyar Lauyoyin ta kasa (NBA) a wajen wani taro da ta gudanar a garin Lagos, ta jaddada kira ga mutunta dokar ta kotu ga gwamnatin Shugaba Buhari.
Shugaban kungiyar, Abubakar Mahmod (SAN), ya bayyana matukar damuwarsu a kan rashin bin umurnin na kotun kasa, inda ya ce; “Ya sabawa duk wata doka a ce gwamnatin kasa ta ki bin umurnin kotu.”
Ya kuma jaddada kira a kan a gaggauta sakin Shaikh Zakzaky da matarsa kamar yadda kotun ta yi umurni. Tare kuma da kira ga mabiya Harkar Musulunci kan su rika mutunta dokoki da hakkokin sauran jama’a.
Wasu daga Lauyoyin Shaikh Ibraheem Zakzaky suna ganawa da manema labarai
An kuma rika samun sakonnin taya murna ga Harkar Musulunci bisa nasarar da ta samu a yayin da ta kafawa masu zaluntar ta hujja da abin da suka yi imani da shi, kuma ta yi galaba a kansu. Kamar yadda wata kungiya mai suna ‘Mahdi Muslim Community’ da ke Nairobi a kasar Kenya ta fitar da takardar taya murna ga Harkar Musulunci a kan wannan nasarar, ta kuma jaddada kira ga gwamnatin Nijeriya kan ta gaggauta bin umurmin na kotun kasar, a ranar 7/12/2016.
Ganin yadda ake ta kiraye-kiraye ta ko’ina a kan gwamnati ta bi umurnin kotu, kwatsam sai ga wata kungiya da ake kira MURIC, wanda a farkon waki’ar Zariya sune farkon wadanda suka yi Allah-wadai da ta’addancin sojojin a kan ’yan kasa Musulmi, a wannan karon kuma bayan nasarar ’yan’uwa a kotu, sai kungiyar ta fito ta bakin Daraktanta, Farfesa Ishaka Akintola, wai ta bayyana Harkar Musulunci a matsayin kungiyar ’yan tashin hankali.
Sun bayyana hakan ne a ranar 5/12/2016, kwanaki uku bayan hukucin kotun Tarayyar ta Abuja, sai ga gwamnatin Kaduna ta fitar da abin da ta kira ‘White-Paper’, wadda take nuna matsayar gwamnatin Kaduna dangane da sakamakon rahoton JCI da ta kafa don binciken dalilin kisan kiyashin Zariya.
A cikin abin da ta kira ‘White-Paper’ din, gwamnatin Kadunan karkashin Gwamnan Jihar, Nasiru El-Rufa’i, ta bayyana matsayarta kan cewa za su bukaci gwamnatin Tarayya ta damka masu Shaikh Ibraheem Zakzaky don su gurfanar da shi a gaban kotu don su caje shi da laifuka daban-daban da ya aikata wa Jihar Kaduna a tsawon shekaru fiye da 30 na gudanar da Harkar Musulunci.
A nan, sai El-Rufa’i ya yi kunnen-uwar-shegu da kiran da kwamitin binciken na JCI ya yi a cikin rahoton da ya mika masa a ranar 15/7/2016, inda ya bukaci a hukunta Shugaban rundunar sojoji ta 1, ‘GOC 1-Division Army’ da ke Kaduna, Janar Oyebade, wanda shi ne ya jagoranci kashe mutum fiye da 347 da duk abin da ya faru a Zariya ranar 12-14/12/2015.
Kwatsam, ranar 1 ga Janairun 2017, sai ga Shugaban kasa Muhammadu Buhari a yayin da yake jawabin sabuwar shekara, ya kira ’yan’uwa Musulmi almajiran Shaikh Zakzaky da sunan ’yan’uwansa. Buhari ya ambaci cewa: “’Yan’uwanmu maza da mata na al’ummar Shi’a”, ya yi kira gare su a kan su kasance masu bin dokokin kasa.
Wannan furucin ya sa al’ummar Nijeriya sun yi caa a kansa ta hanyar mai da masa da martanin cewa shi ya fi kamata ya bi dokar kotun kasa, tunda har yau ba a samu wani laifi kwara daya da wadanda ya kira ’yan Shi’a ko Jagoransu ya aikata, wanda ya sabawa dokar kasar ba, sabanin shi da ya ki bin umurnin kotun kasa tsawon lokaci.
Wannan ya tilasta Kakakinsa, Malam Garba Shehu yin magana a ranar 2/1/2017, a yayin da yake hira da BBC, ya bayyana cewa, al’amarin tsare Shaikh Zakzaky sha’anin Jihar Kaduna ne, ba abin da ya shafi Shugaban kasa da shi. Ya kuma kara da bayyana cewa, wasu mutane sun daukaka kara bisa hukuncin kotun da ta ce a saki Shaikh Zakzaky. Sai dai bai fadi ko su waye mutanen da suka daukaka karar ba.
Ranar 16/1/2017 ne wa’adin da kotun Tarayya ta ba gwamnati kan ta saki Shaikh Zakzaky da matarsa ya cika, a yayin da har zuwa wannan lokacin ba su bi umurnin kotun ba. Sai a ranar 21/1/2-17 jaridar DAILY TRUST ta kawo wani labari daga fadar Shugaban kasa, inda suka bayyana cewa, suna ci gaba da tsare Shaikh Zakzaky ne saboda matsalar tsaro da bukatar jama’a. Suka kuma ce ita matarsa Malama Zeenah ba suna tsare da ita ba ne, tana kula da mai gidan nata ne a inda ake tsare da shi.
Idan ba ku manta ba, a baya mun kawo cewa, a ranar 13/6/2016, Lauyan DSS, Bar. Tijjani ya bayyana a gaban kotu cewa, ba ana tsare da Shaikh Zakzaky ba ne bisa tilasci. Ya ce ana ba shi kariya ne a inda aka aje shi bisa yardarsa. Har ma ya ce DSS sun yi masa maganin raunin da sojoji suka masa na Naira Miliyan 5 da rabi.
A ranar Alhamis, 20/4/2017 kuma, sai ga mataimakin Shugaban kasa, Farfesa Yemi Osibanjo ya rubuta a shafinsa na Twitter cewa, suna ci gaba da tsare Shaikh Zakzaky ne saboda matsalar tsaro. Ya kuma ce sun daukaka kara na hukuncin babban kotun Tarayyar da ta ce a saki Shaikh Zakzaky din.
In mai karatu yana lura, zai ga yadda maganganu suke sassabawa a tsakanin kwanaki daga jami’an gwamnatin, ta yadda suka kasa bayyana takamaiman dalili daya da ya sa suke tsare da Shaikh Zakzaky. Don haka a karshe suka ga ba mafita face kawai su mika Shaikh Zakzaky din zuwa ga gwamnatin Jihar Kaduna, don ta caje shi da kirkirarrun laifuffukan da ta ga dama.
WASU MATAKAN
Cikin matakan da Harkar Musulunci ta bi wajen bayyana zaluncin da aka mata da kuma kokarin samar da adalci daga dokoki da ka’ida na hukunta masu laifin yin wannan kisan kiyashin, kwamitin da ke fafutukar ganin an saki Shaikh Zakzaky da ke karkashin Harkar Musuluci, har ila yau, sun aika da koke zuwa ga Hukumar kare hakkin bil’adama ta Majalisar Dinkin Duniya (United Nations Human Rights Counsil) da ke Geneva, dangane da kisan kiyashin da aka yi a Zariya.
Bayan aikawa da wannan koken, UNHRC da ke Geneva din sun bai wa ‘FreeZakzaky Champaign Committee’ gayyata har sau uku a karo daban-daban, amma sai ofishin jakadancin Switzerland ta hana ‘Visa’ don amsa wannan gayyatar na zuwa ba da bayanai. Daga baya ma ofishin ya sanya takunkumi na tsawon shekaru uku ga Wakilan Kwamitin fafutukar ganin an saki Shaikh Zakzaky din.
Har ila yau, Harkar Musulunci ta shigar da karar duk masu hannu a kisan kiyashin Zariya a kotun hukunta manyan laifuka ta duniya, wato ‘International Criminal Court’ (ICC), wanda izuwa hada wannan rahoton Kotun na ICC ta kammala bincikenta a matakin farko dangane da kisan kiyashin, kuma har ma binciken nasu ya tabbatar da cewa sojojin Nijeriya sun aiwatar da wannan kisan kiyashin a Zariya. Ya zuwa yanzu ana jiran mataki na gaba ne, wanda shi ne kotun ICC din ta ayyana wadanda alhakin wannan kisan kiyashin na Zariya 2015 ya rataya a wuyansu. Daga nan sai matakin tuhumar su da ba da ‘waranti’ na a kama su a gurfanar da su a gabanta a mazauninta da ke Hague a Netherlands.
Harkar Musulunci ta kuma rika shirya Muzaharori a Abuja da sauran garuruwa da kuma gabatar da tarurrukan wayar da kan al’umma da fadakarwa, tare da bayyana zaluncin da aka yi a Zariya, musamman ga ’yan boko da masu rajin kare hakkin bil’adam, inda aka samu da dama suka rika fitowa suna Allah wadai, musamman a kan ci gaban gwamnatin Buhari na yunkurin kawar da Harkar, da auka wa ’yan uwa Musulmi a duk lokacin da suka fito don yin Muzahara ko wani taro da ya shafi addini da fahimtarsu.
Ita kuwa gwamnati a kowane lokaci ba ta da aikin da ya wuce ci gaba da fada da Harkar Musuluncin a matakin Jiha da matakin Tarayya. Tun bayan waki’ar ta Zariya, jami’an tsaro sun ci gaba da auka wa ’yan’uwa a garuruwa daban-daban a lokuta daban-daban, kamar yadda za mu kawo su daki-daki a ci gaban rubutunmu in Allah ya nufa.
Shekaru 3 Da Kisan Kiyashin Zariya (3)
Daga Saifullahi M. Kabir
HARKA DA MATAKAN SHARI’A
A kokarinta na neman a yi mata adalci daga mummunan ta’addancin da sojojin Nijeriya suka yi na auka wa Jagoranta, rushe duk wani muhalli mallakinsa, kashe kimanin mutane 1,000 daga mabiyansa, da kuma kama shi a tsare ba tare da kwakkwaran dalili ba, Harkar Musulunci ta samar da Lauyoyi a karkashin jagorancin wani babban Lauya, Mr. Femi Falana (SAN), daya daga cikin lauyoyin da suka rika yin kira a kan a yi adalci ta hanyar hukunta masu hannu a rikicin Zariya tun a farkon Waki’ar.
Bayan shafe tsawon lokaci da aka yi Lauyoyin na Harkar Musulunci suna neman damar ganin Shaikh Zakzaky, sai a ranar Juma’a 1/4/2016, kimanin watanni biyar da tsare Shaikh din, sannan hukumomi suka bari Lauyoyin a karkashin Mr. Falana suka gana da shi a karon farko a inda ake tsare da shi a Abuja. Wannan ne ma ya ba Falana damar rubuta takarda a ranar 5/4/2016 ga Daraktan DSS na lokacin, Lawal Daura, a kan neman a bar iyalai da Likitocin wanda suke karewa su rika ganawa da shi.
Daya daga cikin lauyoyin Shaikh Ibraheem Zakzaky, Festus Okoye ya sanar da manema labarai a ranar 13/4/2016 cewa, sun shigar da kara a manyan kotuna guda biyu a Abuja da Kaduna a madadin Shaikh Ibraheem Zakzaky da matarsa, Malama Zeenah Ibrahim, bisa caji daban-daban.
Karan na kotun Babbar kotun Abuja (Federal High Court -6, Abuja), Shaikh Zakzaky da matarsa Malama Zeenah suna karar Antoni-Janar na kasa (AGF), Abubakar Malami, da Daraktan hukumar jami’an tsaron farin kaya (DG, DSS), Lawal Daura, da kuma shugaban hukumar ’yan sanda na kasa (IG).
Masu karan guda biyu, suna neman kotu ta tabbatar musu da hakkokinsu da suka hada da, hakkin rayuwa, hakkin walwala da zirga-zirga, hakkin kare daraja da mutunci, da kuma hakkin rayuwa cikin aminci tare da iyali.
Bisa take wadannan hakkokin da wadanda ake zargin suka yi ga Shaikh Zakzaky da Matarsa, ta hanyar tsare su na tsawon watanni biyar ba tare da likitocinsu, lauyoyinsu ko iyalinsu sun ziyarce su ba, sun bukaci kotun ta sa wadanda suke tsare da sun su biya su diyyar Naira biliyan biyu (2 Billion Naira).
Shi kuwa karar da aka shigar a Kaduna, Shaikh Zakzaky da matarsa Malama Zeenat ne suke karar Antoni-Janar na kasa (AGF), da Sojojin Nijeriya (NA), da Shugaban sojojin Nijeriya, Tukur Buratai, da Hukumar tsaron farin kaya (DSS), da kuma Antoni Janar kuma Kwamishinan shari’a na jihar Kaduna, bisa zargin kai hari a gidansu a ranar 12-14/12/2015, kashe musu ’ya’yansu da almajiransa a gabansu, rusa musu muhallansu da barnata dukiyarsu da kuma kama su a tsare, wanda ya tauye ’yancinsu a matsayinsu na ’yan kasa.
SHARI’AR KOTUN ABUJA
An fara shiga shari’ar da ke kotun Abuja ne a ranar 23/5/2016, a gaban mai shari’a Gabriel Kolawale, inda aka dage zuwa ranar 13/6/2016 sakamakon rashin zuwan wasu daga lauyoyin wadanda ake zargi. A ranar Talatar, 13/6/2016 aka ci gaba da shari’ar, inda lauyan DSS, Barr. Tijjani Gazali ya bayyana wa kotu cewa ba bisa tilasci ake tsare da Shaikh Zakzaky ba, yana tsare ne bisa zabin kansa, kuma su suna tsare shi ne bisa yardarsa don su ba shi kariya.
Gazali ya kuma bayyana wa kotun cewa, a tsawon watannin da ake tsare da Shaikh Zakzaky da Mai dakinsa a wajen DSS, an kashe masa abin da bai gaza Naira miliyan 5.1M ba na magani. A nan ne sai Lauyoyin Shaikh Zakzaky suka bukaci kotun ta ba su lokaci don mai da martani ga ikirarin na lauyan DSS, inda Alkalin ya daga ranar ci gaba da sauraron shari’ar zuwa ranar 13/7/2016.
Bayan dawowa kotun a ranar 13/7/2016, Lauyoyin Harka sun gabatar da amsa ga ikirarin na Lauyan DSS. Abin da ya tabbata shi ne hatta man injin da ke haska wajen da ake tsare da Shaikh Zakzaky a Abuja, Shaikh din ne ke saya da kudinsa tun sad da aka tsare su. Mai shari’a Kolawaye, ya sake dage ci gaba da shari’ar zuwa ranar 20/9/2016. Ya bayyana zuwan Alkalai hutu a wannan tsakanin a matsayin dalilin dagewa da nisa.
Kodayake Lauyan Shaikh Zakzaky, Mr. Falana ya nemi kotun ta ci gaba da zaman a cikin hutun, amma Alkalin ya yi watsi da bukatar tasa. Sai dai a ranar 30/8/2016, Falana ya aika wa kotun da wasika, yana mai neman ta ba da dama a kai Shaikh Zakzaky asibiti a kasar waje, sakamakon rashin lafiyar idanunsa da yake kara tsananta.
Bukatar Falana ba ta amsu ba, a yayin da aka dawo kotu a ranar 20/9/2016, nan kuma zaman kotun bai yiwu ba, sakamakon taron da Alkalan manyan kotuna suke yi a wannan ranar a Abuja. Sai aka kuma saka ranar 5/10/2016 a matsayin ranar da za a dawo don ci gaban shari’ar.
A ranar 5/10/2016, Mai Shari’a Gabriel Kolawale, bayan sauraron abubuwan da suka rage, ya bayyana takaicinsa matuka a kan shari’ar, inda ya ce irin wannan take hakkin na dan kasa abin kunya ne ga Nijeriya. Ya nemi da a je a sulhunta tsakanin masu karar da wadanda ake kara kafin ranar 25/11/2016, inda ya ce zai yanke hukunci a wannan ranar ko da ba a sulhunta ba. Ko da ranar 25/11/2016 ta zagayo, ba a yi zaman kotun ba, nan ma Alkalin ya sake kara mako guda, inda ya saka ranar 2/12/2016 a matsayin ranar yanke hukunci.
Ranar 2/12/2016 ne kotun ta yi zamanta na karshe, inda mai shari’a Gabriel Kolawale ya karanta hukunci. Ya bayyana tsare Shaikh Zakzaky da mai dakinsa da ake yi a matsayin haramtacce, wanda ya saba doka. Ya kuma saba wa kundin tsarin mulkin Nijeriya. A madadin kotun, Kolawale ya ba da umurni ga gwamnatin Nijeriya ta gaggauta sakin Shaikh Zakzaky da mai dakinsa, Malama Zeenat a cikin kasa da kwanaki 45 daga ranar wannan hukuncin.
Har ila yau, kotun ta ba da umurnin gwamnatin Nijeriya ta gina wa Shaikh Ibraheem Zakzaky gida a duk jihar da yake bukatar zama a fadin jihohin arewacin Nijeriya, tare kuma da biyan kowannen su, (Shaikh din da Malama Zeenat) diyyar Naira miliyan 25 na haramtaccen tsarewar da aka yi musu, wanda ya kama Naira miliyan 50. Sannan kuma a yayin sakin, Hukumar DSS su mika Shaikh din da Matarsa ga wani babban Dan sanda, su kuma su raka shi zuwa gidan da aka tanadar masa a cikin kasa da awa 24.
SHARI’AR KOTUN KADUNA
Ita kuwa shari’ar Kaduna, wanda aka shigar a High Court, karkashin mai shari’a S.M Shu’aibu, bisa neman hakkokin barnar da aka yi a Zariya, an fara gudanar da zaman kotun ne a ranar 18/5/2016, inda aka dage ta zuwa ranar 7/6/2016 don ci gaba da sauraron karar.
A ranar Alhamis, 7/6/2016, aka koma don ci gaba da shari’ar, inda bayan kammala karanta kara, sai lauyan gwamnati, wato Antoni Janar na Tarayya ya nemi kotun da ta ba su lokaci don nazari da mai da martani ga Karan. Nan aka dage ci gaban sauraron karar zuwa ranar 15/6/2016.
A ranar Alhamis, 15/6/2016 an dawo kotun don ci gaba da shari’ar. Sai dai Babban Lauyan da ke wakiltan Shugaban sojojin Nijeriya bai zo ba, ya turo wani Lauya mai suna Husain Oyebani a matsayin wanda zai wakilce shi. Husaini ya bayyana wa kotu cewa ba zai iya kare shari’ar ba saboda bai yi nazarin ta ba. Sai ya nemi a ba su lokaci don yin nazarin shari’ar. Kotun ta karbi uzurinsa, kuma Alkalin ya dage ci gaba da sauraron shari’ar zuwa ranar 30/6/2017, inda ya gargade su da shiryawa kare karar zuwa wannan ranar.
Ranar 30/6/2017, Lauyan na sojoji kuma mai tsayawa a madadin Tukur Buratai, wato, Mr. Biola Oyebanji ya bayyana a gaban kotun, inda ya bukaci kotun ta kori shari’ar, bisa hujjar cewa shari’ar na kotun Kaduna ta yi kama da ta Abuja da Alkali Kolawale ya yanke hukunci a ranar 2/12/2016.
Mai Shari’an, Sale Musa Shu’aibu, ya bayyana cewa kararrakin guda biyu da aka shigar a Kaduna da wanda aka shigar a Abuja abu ne mabambanta. Ya ce ya nazarci hukuncin da dan’uwansa Alkali Kolawale na babban kotun tarayya ya gabatar a kan neman hakkin tsarewa ba bisa ka’ida ba, da kuma neman ’yancin rayuwa. Kuma ya ga akwai bambanci da wanda yake gabansa. Don haka ya sanya ranar Alhamis, 6/7/2017 a matsayin ranar da zai yanke hukunci.
A ranar 6/7/2017, kwatsam sai Alkali S.M Shu’aibu ya bayyana da sabon al’amari. Inda ya karbi bukatar Lauyan sojoji, ya koma kan ra’ayin cewa kararrakin da aka shigar a kotun Abuja da wanda aka shigar a wannan kotun nasa abu guda ne. Don haka kai tsaye ya yanke hukuncin korar shari’ar gaba daya.
Da yake mai da martani a kan hukuncin na kotun, Shugaban kwamitin fafutukar ganin an saki Shaikh Zakzaky, Malam Abdurrahman Abubakar Yola, a wata takardar manema labarai da ya saka wa hannu a ranar 6/7/2017, ya bayyana bambancin da ke tsakanin karar da aka shigar a kotun Abuja da wanda aka shigar a Kaduna.
Ya ce, a Abuja an yi karar Antoni Janar na kasa, Shugaban DSS, da kuma Shugaban rundunar ’yan sanda na kasa a kan laifin da suka aikata a Abuja na tsare Shaikh Zakzaky da matarsa ba bisa ka’ida ba, da hana su ’yancin walwala. A Kaduna kuwa, an shigar da kara ne na Antoni Janar na kasa (AGF), da Sojojin Nijeriya (NA), da Shugaban sojojin Nijeriya, Tukur Buratai, da Hukumar tsaron farin kaya (DSS), da kuma Antoni Janar kuma Kwamishinan shari’a na jihar Kaduna, su kuma bisa laifin da suka aikata a jihar Kaduna na kai hari ga Shaikh Zakzaky da kama shi ba bisa ka’ida ba, kashe masa ’ya’ya da ’yan uwa da almajirai da kuma rusa masa muhallansa. “Don haka bambancin a bayyane yake,” in ji shi.
Malam Yola ya ce: “Wannan hukuncin ba zai taba karya mana kwarin guiwarmu na ci gaba da neman adalci ta hanyar bin matakan shari’a ba.”
Ya zuwa hada wannan rahoton, mun samu labarin cewa, Lauyoyin na Shaikh Zakzaky sun daukaka karar shari’o’in guda biyu zuwa kotun daukaka kara wato ‘Appeal court’; bisa rashin bin umurnin sakin Shaikh Zakzaky da kotun Abuja ta ba da, da kuma korar karar da kotun Kaduna ta yi bisa hujjar kamanceceniyar shari’un biyu. Sai dai alamu na nuna rashin jin dadin hakan daga hukumar Nijeriya, a yayin da ta kowane hali suke ta kokarin kawo cikas ga fara zaman na kotun daukaka kara a boye.
Ku biyo mu don jin abubuwan da suka biyo bayan yanke hukuncin kotun Tarayya da ke Abuja.
HARKA DA MATAKAN SHARI’A
A kokarinta na neman a yi mata adalci daga mummunan ta’addancin da sojojin Nijeriya suka yi na auka wa Jagoranta, rushe duk wani muhalli mallakinsa, kashe kimanin mutane 1,000 daga mabiyansa, da kuma kama shi a tsare ba tare da kwakkwaran dalili ba, Harkar Musulunci ta samar da Lauyoyi a karkashin jagorancin wani babban Lauya, Mr. Femi Falana (SAN), daya daga cikin lauyoyin da suka rika yin kira a kan a yi adalci ta hanyar hukunta masu hannu a rikicin Zariya tun a farkon Waki’ar.
Mr. Femi Falana SAN, na jawabi a wajen wani Muzaharar kira a saki Shaikh Zakzaky a Abuja
Bayan shafe tsawon lokaci da aka yi Lauyoyin na Harkar Musulunci suna neman damar ganin Shaikh Zakzaky, sai a ranar Juma’a 1/4/2016, kimanin watanni biyar da tsare Shaikh din, sannan hukumomi suka bari Lauyoyin a karkashin Mr. Falana suka gana da shi a karon farko a inda ake tsare da shi a Abuja. Wannan ne ma ya ba Falana damar rubuta takarda a ranar 5/4/2016 ga Daraktan DSS na lokacin, Lawal Daura, a kan neman a bar iyalai da Likitocin wanda suke karewa su rika ganawa da shi.
Daya daga cikin lauyoyin Shaikh Ibraheem Zakzaky, Festus Okoye ya sanar da manema labarai a ranar 13/4/2016 cewa, sun shigar da kara a manyan kotuna guda biyu a Abuja da Kaduna a madadin Shaikh Ibraheem Zakzaky da matarsa, Malama Zeenah Ibrahim, bisa caji daban-daban.
Karan na kotun Babbar kotun Abuja (Federal High Court -6, Abuja), Shaikh Zakzaky da matarsa Malama Zeenah suna karar Antoni-Janar na kasa (AGF), Abubakar Malami, da Daraktan hukumar jami’an tsaron farin kaya (DG, DSS), Lawal Daura, da kuma shugaban hukumar ’yan sanda na kasa (IG).
Masu karan guda biyu, suna neman kotu ta tabbatar musu da hakkokinsu da suka hada da, hakkin rayuwa, hakkin walwala da zirga-zirga, hakkin kare daraja da mutunci, da kuma hakkin rayuwa cikin aminci tare da iyali.
Bisa take wadannan hakkokin da wadanda ake zargin suka yi ga Shaikh Zakzaky da Matarsa, ta hanyar tsare su na tsawon watanni biyar ba tare da likitocinsu, lauyoyinsu ko iyalinsu sun ziyarce su ba, sun bukaci kotun ta sa wadanda suke tsare da sun su biya su diyyar Naira biliyan biyu (2 Billion Naira).
Shi kuwa karar da aka shigar a Kaduna, Shaikh Zakzaky da matarsa Malama Zeenat ne suke karar Antoni-Janar na kasa (AGF), da Sojojin Nijeriya (NA), da Shugaban sojojin Nijeriya, Tukur Buratai, da Hukumar tsaron farin kaya (DSS), da kuma Antoni Janar kuma Kwamishinan shari’a na jihar Kaduna, bisa zargin kai hari a gidansu a ranar 12-14/12/2015, kashe musu ’ya’yansu da almajiransa a gabansu, rusa musu muhallansu da barnata dukiyarsu da kuma kama su a tsare, wanda ya tauye ’yancinsu a matsayinsu na ’yan kasa.
SHARI’AR KOTUN ABUJA
An fara shiga shari’ar da ke kotun Abuja ne a ranar 23/5/2016, a gaban mai shari’a Gabriel Kolawale, inda aka dage zuwa ranar 13/6/2016 sakamakon rashin zuwan wasu daga lauyoyin wadanda ake zargi. A ranar Talatar, 13/6/2016 aka ci gaba da shari’ar, inda lauyan DSS, Barr. Tijjani Gazali ya bayyana wa kotu cewa ba bisa tilasci ake tsare da Shaikh Zakzaky ba, yana tsare ne bisa zabin kansa, kuma su suna tsare shi ne bisa yardarsa don su ba shi kariya.
Gazali ya kuma bayyana wa kotun cewa, a tsawon watannin da ake tsare da Shaikh Zakzaky da Mai dakinsa a wajen DSS, an kashe masa abin da bai gaza Naira miliyan 5.1M ba na magani. A nan ne sai Lauyoyin Shaikh Zakzaky suka bukaci kotun ta ba su lokaci don mai da martani ga ikirarin na lauyan DSS, inda Alkalin ya daga ranar ci gaba da sauraron shari’ar zuwa ranar 13/7/2016.
Bayan dawowa kotun a ranar 13/7/2016, Lauyoyin Harka sun gabatar da amsa ga ikirarin na Lauyan DSS. Abin da ya tabbata shi ne hatta man injin da ke haska wajen da ake tsare da Shaikh Zakzaky a Abuja, Shaikh din ne ke saya da kudinsa tun sad da aka tsare su. Mai shari’a Kolawaye, ya sake dage ci gaba da shari’ar zuwa ranar 20/9/2016. Ya bayyana zuwan Alkalai hutu a wannan tsakanin a matsayin dalilin dagewa da nisa.
Kodayake Lauyan Shaikh Zakzaky, Mr. Falana ya nemi kotun ta ci gaba da zaman a cikin hutun, amma Alkalin ya yi watsi da bukatar tasa. Sai dai a ranar 30/8/2016, Falana ya aika wa kotun da wasika, yana mai neman ta ba da dama a kai Shaikh Zakzaky asibiti a kasar waje, sakamakon rashin lafiyar idanunsa da yake kara tsananta.
Bukatar Falana ba ta amsu ba, a yayin da aka dawo kotu a ranar 20/9/2016, nan kuma zaman kotun bai yiwu ba, sakamakon taron da Alkalan manyan kotuna suke yi a wannan ranar a Abuja. Sai aka kuma saka ranar 5/10/2016 a matsayin ranar da za a dawo don ci gaban shari’ar.
A ranar 5/10/2016, Mai Shari’a Gabriel Kolawale, bayan sauraron abubuwan da suka rage, ya bayyana takaicinsa matuka a kan shari’ar, inda ya ce irin wannan take hakkin na dan kasa abin kunya ne ga Nijeriya. Ya nemi da a je a sulhunta tsakanin masu karar da wadanda ake kara kafin ranar 25/11/2016, inda ya ce zai yanke hukunci a wannan ranar ko da ba a sulhunta ba. Ko da ranar 25/11/2016 ta zagayo, ba a yi zaman kotun ba, nan ma Alkalin ya sake kara mako guda, inda ya saka ranar 2/12/2016 a matsayin ranar yanke hukunci.
Ranar 2/12/2016 ne kotun ta yi zamanta na karshe, inda mai shari’a Gabriel Kolawale ya karanta hukunci. Ya bayyana tsare Shaikh Zakzaky da mai dakinsa da ake yi a matsayin haramtacce, wanda ya saba doka. Ya kuma saba wa kundin tsarin mulkin Nijeriya. A madadin kotun, Kolawale ya ba da umurni ga gwamnatin Nijeriya ta gaggauta sakin Shaikh Zakzaky da mai dakinsa, Malama Zeenat a cikin kasa da kwanaki 45 daga ranar wannan hukuncin.
Har ila yau, kotun ta ba da umurnin gwamnatin Nijeriya ta gina wa Shaikh Ibraheem Zakzaky gida a duk jihar da yake bukatar zama a fadin jihohin arewacin Nijeriya, tare kuma da biyan kowannen su, (Shaikh din da Malama Zeenat) diyyar Naira miliyan 25 na haramtaccen tsarewar da aka yi musu, wanda ya kama Naira miliyan 50. Sannan kuma a yayin sakin, Hukumar DSS su mika Shaikh din da Matarsa ga wani babban Dan sanda, su kuma su raka shi zuwa gidan da aka tanadar masa a cikin kasa da awa 24.
SHARI’AR KOTUN KADUNA
Ita kuwa shari’ar Kaduna, wanda aka shigar a High Court, karkashin mai shari’a S.M Shu’aibu, bisa neman hakkokin barnar da aka yi a Zariya, an fara gudanar da zaman kotun ne a ranar 18/5/2016, inda aka dage ta zuwa ranar 7/6/2016 don ci gaba da sauraron karar.
A ranar Alhamis, 7/6/2016, aka koma don ci gaba da shari’ar, inda bayan kammala karanta kara, sai lauyan gwamnati, wato Antoni Janar na Tarayya ya nemi kotun da ta ba su lokaci don nazari da mai da martani ga Karan. Nan aka dage ci gaban sauraron karar zuwa ranar 15/6/2016.
A ranar Alhamis, 15/6/2016 an dawo kotun don ci gaba da shari’ar. Sai dai Babban Lauyan da ke wakiltan Shugaban sojojin Nijeriya bai zo ba, ya turo wani Lauya mai suna Husain Oyebani a matsayin wanda zai wakilce shi. Husaini ya bayyana wa kotu cewa ba zai iya kare shari’ar ba saboda bai yi nazarin ta ba. Sai ya nemi a ba su lokaci don yin nazarin shari’ar. Kotun ta karbi uzurinsa, kuma Alkalin ya dage ci gaba da sauraron shari’ar zuwa ranar 30/6/2017, inda ya gargade su da shiryawa kare karar zuwa wannan ranar.
Ranar 30/6/2017, Lauyan na sojoji kuma mai tsayawa a madadin Tukur Buratai, wato, Mr. Biola Oyebanji ya bayyana a gaban kotun, inda ya bukaci kotun ta kori shari’ar, bisa hujjar cewa shari’ar na kotun Kaduna ta yi kama da ta Abuja da Alkali Kolawale ya yanke hukunci a ranar 2/12/2016.
Mai Shari’an, Sale Musa Shu’aibu, ya bayyana cewa kararrakin guda biyu da aka shigar a Kaduna da wanda aka shigar a Abuja abu ne mabambanta. Ya ce ya nazarci hukuncin da dan’uwansa Alkali Kolawale na babban kotun tarayya ya gabatar a kan neman hakkin tsarewa ba bisa ka’ida ba, da kuma neman ’yancin rayuwa. Kuma ya ga akwai bambanci da wanda yake gabansa. Don haka ya sanya ranar Alhamis, 6/7/2017 a matsayin ranar da zai yanke hukunci.
A ranar 6/7/2017, kwatsam sai Alkali S.M Shu’aibu ya bayyana da sabon al’amari. Inda ya karbi bukatar Lauyan sojoji, ya koma kan ra’ayin cewa kararrakin da aka shigar a kotun Abuja da wanda aka shigar a wannan kotun nasa abu guda ne. Don haka kai tsaye ya yanke hukuncin korar shari’ar gaba daya.
Da yake mai da martani a kan hukuncin na kotun, Shugaban kwamitin fafutukar ganin an saki Shaikh Zakzaky, Malam Abdurrahman Abubakar Yola, a wata takardar manema labarai da ya saka wa hannu a ranar 6/7/2017, ya bayyana bambancin da ke tsakanin karar da aka shigar a kotun Abuja da wanda aka shigar a Kaduna.
Ya ce, a Abuja an yi karar Antoni Janar na kasa, Shugaban DSS, da kuma Shugaban rundunar ’yan sanda na kasa a kan laifin da suka aikata a Abuja na tsare Shaikh Zakzaky da matarsa ba bisa ka’ida ba, da hana su ’yancin walwala. A Kaduna kuwa, an shigar da kara ne na Antoni Janar na kasa (AGF), da Sojojin Nijeriya (NA), da Shugaban sojojin Nijeriya, Tukur Buratai, da Hukumar tsaron farin kaya (DSS), da kuma Antoni Janar kuma Kwamishinan shari’a na jihar Kaduna, su kuma bisa laifin da suka aikata a jihar Kaduna na kai hari ga Shaikh Zakzaky da kama shi ba bisa ka’ida ba, kashe masa ’ya’ya da ’yan uwa da almajirai da kuma rusa masa muhallansa. “Don haka bambancin a bayyane yake,” in ji shi.
Malam Yola ya ce: “Wannan hukuncin ba zai taba karya mana kwarin guiwarmu na ci gaba da neman adalci ta hanyar bin matakan shari’a ba.”
Ya zuwa hada wannan rahoton, mun samu labarin cewa, Lauyoyin na Shaikh Zakzaky sun daukaka karar shari’o’in guda biyu zuwa kotun daukaka kara wato ‘Appeal court’; bisa rashin bin umurnin sakin Shaikh Zakzaky da kotun Abuja ta ba da, da kuma korar karar da kotun Kaduna ta yi bisa hujjar kamanceceniyar shari’un biyu. Sai dai alamu na nuna rashin jin dadin hakan daga hukumar Nijeriya, a yayin da ta kowane hali suke ta kokarin kawo cikas ga fara zaman na kotun daukaka kara a boye.
Ku biyo mu don jin abubuwan da suka biyo bayan yanke hukuncin kotun Tarayya da ke Abuja.
Subscribe to:
Posts (Atom)











